Showing 81001 words to 84000 words out of 209297 words
taje duk abunda ze sameta ya sameta, nan aka canza gurin aiki aka bawa ɗanta muƙamina, ba abunda tace se yanzu wani in mata jaje baza'ayi ba ɗin, Allah ya ƙara '
Harze wuce ya hangi Sakina ta taho da files a hannunta, yana ganinta ya fara murmushi yace "budurwar kidnapper, ashe abunda ya faru kenan? Saurayinki yaje ya sace' yar masu kuɗi gaskiya kuna ruwa"
Sakina tace "haba Abbas, yazaka maida abun abun wasa? Wannan maganar be dace a jita daga bakinka ba a matsayinsa na Abokinka, kuma abokin aikin mu, kuma kasan baze aikata hakan ba"
"ke dalla ware, waye yace miki baze aikata ba? Mutum nefa shi, waye baya son kuɗi a rayuwar nan? Kedai Allah ya kyauta kawai ya tona masa Asiri, dama ya daɗe yana naɗe kura da fatar Akuya ne"
Sakina ta dinga bin Abbas da kallon mamaki, wai babban abokine yake faɗar maganganu akan Abokinsa haka, lallai duniyar nan ba abun yadda bace.
Da Asuba Yusuf ya tashi Widad tayi salla, taji daɗi yau ya kulata ya tasheta tayi salla, bayan ta idar ta koma baccin nata na ƙa'ida.
Yusuf yayi komai, har sharar tsakar gida, Hanne a ɓangaren Jamila ta kwana, da safe ta dawo ɓangaren su dan taga Yusuf, aikuwa ta tarar dashi yana shara.
"Ina kwana? '
Yusuf ya kalleta ya amsa mata, ya cigaba da shara," kawo in share gidan "
Yusuf yace ' A'a bakomai zanyi, ai ba wani abu bane"
Duk yadda Hanne taso ko hira su ɗanyi da Yusuf yaƙi yadda, saboda ya gane Lagon Widad yanzu, kishi ne da ita matuƙa, dan haka ya fara ƙoƙarin kiyayewa.
Sam Hanne bata ji daɗin yadda Yusuf yayi mata yau ba.
Ya koma ya ɗora girki a ɗaki, yana yi ya kalli inda Widad ke kwance na bacci, yana zuwa beyi wata wata ba ya ɗagata sama yai waje da ita tsakar gida.
Buɗe baki tayi zata yi ihu, ya rufe mata baki yace "ke nine fa" sannan tai shiru tana ajiyar zuciya tace 'shine zaka tsoratani kuma?'
"Yaushe kika zama matsoraciya ne? Kedai kiyi bacci kiyi bacci, ko gajiya bakya yi? Karɓi brush ɗinki ki wanke baki, muje ki tayani girki"
Yai maganar yana matsa mata toothpaste, "Yayan Daddy ka dena fushin dani ne?"
"A'a har yanzu inayi"
"Meyasa bazaka haƙura ba?"
Yusuf yace "kona haƙura anjima ma, sekin sake abunda zanyi fushi dake"
"to ai nace Kayi haƙuri, kuma ai kai baka fushi fa"
Yace "waya gayamiki bana fushi? Nima mutum ne fa"
"To na dena kaji" tai maganar a sigar Shagwaɓa.
"Idan kika kuma, sedai ki wayi gari kiga na fece na barki"
"Aikuwa inaga da haɗiyar zuciya zanyi in huta"
Murmushi yayi yace "ba wani haɗiyar zuciya, ai bakya sona"
Ba tace komai ba ta fara wanke bakinta, suka gama suka koma ɗaki, can Widad tace "Yoseed, meyasa da nace maka Yuzarsef naga ka shiga damuwa jiya?"
Yace "karki damu ba wani abu bane, kin tunamin da babana ne"
"Allah sarki, Allah yayi musu rahama gaba ɗaya"
Yace "Ameen ya Allah masoyiyyata"
Yai maganar tare da sumbatar kumatunta.
Tayi murmushi tace "Yayan Daddy, kamin addu'a Allah yasa in samu ciki, so nake in haihu nima ace ina da baby"
Da sauri Yusuf yayi mata wani irin kallo, da ita kanga bata gane ma'anar sa ba....
LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
11/14/21, 6:09 PM - Ummee Musa: LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
IDAN KUMA KIN SIYA AMANACE KARKI FITARMIN DAN ALLAH 🙏🙏🙏
90_91
Saroro tayi tana kallonsa ta kasa gane me yake nufi da wannan kallon da yake mata, tace
"ya dai naga kamar ka ɓata rai? Ko na sake faɗan wani abun na dai dai ba"
Girgiza mata kai yayi yace "No bakomai"
"Amma naga kamar ka ɓata rai? Da ba a haka fuskarka take ba fa"
Yusuf yace "A'a ba ɓata rai nayi ba, karki damu zo kici Abincin ki, nasan kina jin yunwa yanzu, dan rana tayi baki karya ba"
Ya zuba mata Abincin, Haka taci Abincin tana lura da yadda Yusuf duk yayi wani iri, kamar wani abu yana ɗan damunsa, amma babu alamar ze faɗa mata meke damun nasa.
Anwar ya shirya yaje gidansu Fahad, domin yana son ganin Bulama suyi magana, sedai be sami Fahad a gida ba, dama ba gurinsa yaje ba dan haka be kula ba ya nemi idan Bulama yana nan a masa iso, Ramadan yayi masa iso zuwa gurin Bulama, Bulama na ganinsa yayi murmushi yace "Anwar, anya in kulaka kwana biyu baka leƙowa mu gaisa"
Anwar yayi murmushi yace "tuba nake, abubuwa ne suka ɗanyi yawa wlh, Daddy ya aiki ya gida? Naji amce zaka Umarah shiyasa nace bari inzo in sameka"
"Alhamdilillah Anwar, eh insha Allah sati ma gaba zan tafi da yardar Allah, ya gidan naku ya babarta ka da ƙannenka?"
Anwar yace "Tana lafiya ƙalau Alhamdilillah"
"Masha Allah, nice to hear that haka akeso ai, naji kana son ganina meyafaru ne?"
Anwar yace "Amm Daddy, dama nazo ne akan inji wai har yanzu babu wani labari game da ɓatan Mariƙinmune? Har yanzu babu shi babu Widad gashi lokaci yana ta ƙara ja, amma shiru babu wani labari akai"
Bulama ya gyara zama sannan yace "Ahh mekuma kake sonji Anwar, bayan wanda yake ta yawo a gari? Widad garin jajibe jajibenta duk wayo da ƙin mutanenta, amma ta yayimo tsiya, wani koɗaɗɗen yaro me kama da sadakar yalla nan, direbanta ta ɗauki duk wata ragamar yaddarta ta bashi, ko gidan nan tazo duk sirrin magana sedai muyi a gabansa, ko nan da cam ba zata je ba seda shi, duk maganar da zamuyi sedai a gabansa, dan haka duk yadda take kaffa kaffa yasan wasu daga cikin sirrinta, gashi ƙarshe 'yan sanda bincikensu ya tabattar musu da cewar, shine yayi garkuwa da ita, ya nemi kuɗin fansa a gurin mahaifinta, dabe samu ba shine yabi Asibitin ya sace mahaifinta, yanzu dai' yan sanda suna nan suna binciken inda zasu gansu, amma shiru babu Labari, sedai a cigaba da Addu'a sannan mu cigaba da sauraren abunda zasu ce, amma abun da ɗaure kai fa sosai"
Anwar yace "nifa Daddy har yanzu ban yadda da wannan sakamakon binciken ba da aka bayyana, babu yadda za'ayi ace shine ya saceta, Daddy kasanta da wayon tsiya, babu yadda za' ayi tana sane ta bari yasan sirrinta, sedai idan akwai wata manufa da take dashi a kanta, sannan daga rundunar 'yan sandan nan a farko an sanar da sace su akayi, har an siyar da motar da aka sace su a ciki an ganta a kasuwa, ba' a kumabi takan zancem ba, basu bincika ya akai motar taje kasuwa ba, kuma azo a sake sanar da cewa wai shine ya saceta, it doesn't make sense, kuma bayan haka ace ya kuma zuwa ya sace mahaifinta, sam beyi kama da criminals ba, ni gaba ɗaya banji ƙamshin gaskiya a lamarin nan ba, akwai wata a ƙasa dai"
Bulama yace "eh to, kaima maganarka abun dubawace, amma ka sani mutum yana iya canzawa a kowane lokaci, kuma ze iya yuwuwa shine ya saida motar, tunda yasan siriikanta dan yasan abunda ban sani ba ni game da ita, sannan kuma duk abunka da ƙwaƙwƙwafinka kasan dai ba zaka gwadawa 'yan sanda aikinsu ba, tunda suka faɗi haka kasan abunda bincikensu ya nuna musu kenan, ba zasu yi ƙarya ba haka kurum, kabar mutum akan aikinsa kawai"
Anwar kamar ze kuka yace "Amma Daddy babu abunda' yan sanda ba zasu iyayi akan kuɗi ba kaima ka sani, idan wasu ba zasu yi ba, wasu zasuyi tunda suma mutane ne, dan haka ba abun mamaki bane suma 'yan sanda suyi komai akan kuɗi ba, dan haka yakamata ta ɓangarenka ma, kasa a sake bincikawa a tabattar da in dagaske binciken nasu haka yake, kasan Alhaji Nasir da' yarsa suna da maƙiya, komai fa ze iya faruwa, zata iya yuwuwa su suke wannan abubuwan haka"
Bulama yayi dariya irin tasu ta tsofaffin manya yace "Yaro yarone dai, Amma kaima kace wani abu me mahimmanci fa, shikenan Anwar tunda haka kace, Insha Allah zanga ƙoƙarin da zanyi ta ɓangarena, tabbas Daula yana da maƙiya kam, kuma komai ze iya faruwa, zanga abunda zan iya, Allah ya wuce mana gaba"
Anwar yace "Ameen Daddy, nagode sosai"
Kasancewar gidan babu kowa yasa Yusuf baya fita ko ina, dan baze iya fita ya barta a gida ba ita kaɗai, yasan ba zata zauna bama, suna zaune tama ta saƙa mafici Ya ɗan kalleta yace "Widad"
Ta ɗago ta kalleshi Tace "Na'am"
Yace "Me kike tunani game da wannan baƙin, ɗan megari da matarsa, bakya ganin Asirinmu ze iya tonuwa zamanmu dasu? Kar muje a samu matsala fa"
Widad ta ajiye abun hannunta jiki a sanyaye tace "To aini gaba ɗaya kaina ya kulle Yoseef, na rasa meye abunyi wallahi, kawai ni yanzu na fawallawa Allah lamarinsa, duk yadda yayi damu shikenan, ni dai babban fatana in cika burina kafin in mutu, nasan ko asirinmu ya tonu, ko be tonu ba dole ɗayanmu zeyi nasara, komu ko maƙiya, dan haka na miƙawa Allah lamarina, Allah ya kiyaye mu gaba ɗaya, amma nima nayi irin wannan tunanin naka, amma ba yadda na iya, in mun bar nan ina zamu?"
Yusuf yayi ajiyar zuciya yace "da farko ina ɗan jin shakku a raina ne, amma Saleh ya tabattar min da babu komai, ba abunda ze faru yasan matakan daya ɗauka, sedai ina fatan Allah yasa hakan, Allah ya kiyayemu da kiyayewarsa"
Tace "Ameen ya Allah, Amma Yoseef nifa har yanzu baka taɓa gayamin meka gano a naka binciken ba, da kayi a lokacin muna gida"
Yusuf ya ɗanyi murmushi yace "Anƙi a faɗa ɗin, kema ai jamin rai kika dingayi, kika ƙi gayamin tarihinki"
Cikin Shagwaɓa tace "please"
Yusuf yace "to shagwaɓaɓiya karkimin kuka dai, bincike daga cikin gidanku na fara yi, sedai nayi mamakin ƙiyayyar da matar mahaifin ki ke miki, da farko nayi zaton tana yi ne saboda halayenki, da abunda kikeyi na wulaƙanta ta da 'ya' yanta, sedai daga baya na gane son zuciyarta ne abunda take, akwai ranar da kika rufe ƙofa kika ƙi buɗewa, nasa Amal ta kawo miki tea, sedai kika zubar da tea ɗin, nayi mamakin ganin ƙwaya a ƙasan kofin shayin"
Widad tace "Kasan meyafaru a wannan daren, da na birkice?"
Ya girgiza mata kai alamar a'a.
Tace "samunsu nayi a falo, suna tattauna yadda zata damfari Daddy kuɗi, kasan na kanyi kwanaki a part ɗina ban fito ba, shine suka sakankance suna hirarsu, basu yi tsammani ba kawai suka ganni a ƙofar falo, shine suka shiga kame kame, bance musu komai ba, na fita dama fita zamuyi da kai ranar, bayan mun dawo cikin dare ina bacci, da yake ban rufe ƙofar ɗakina ba, kawai seji nayi cikin bacci ana lalabun hannuna, nayi yinƙuri zan ƙwaci hannuna kawai akayi min Allura, irin Allurar da'ake min a baya a birkita ni, take na fara dena gane abubuwa sosai, ban san wanda yayi min allurar ba, amma a haka bayan ya fita na tashi ina tangaɗi na rufe ƙofata, tun daga nan ban sake sanin abunda ke faruwa ba, se bayan dawowar Daddy, shiyasa a rayuwa na tsani matar nan Yoseef, na tsaneta fiye da yadda kake tunani, ji nake kamar in shaƙeta seta mutu"
"a'a karki kuma cewa zaki kashe mutum, sannan kika sani ko Daddy yana son matarsa? Ki barwa Allah zakiga sakayyar daze miki, amma banda ambaton kisa"
"Rabu dani bazaka gane ba Wallahi, dama muna komawa Seta barmana gida, sannan Aure zan nemawa Daddy da kaina, sannan ko banyi kisa ba idona idon Bukar a zahiri seya tafi lahira da tabom da zanyi masa"
"Kibi komai a hankali Widad, Insha Allah komai zamu bishi a hankali, kuma zamuyi nasara da yardar Allah, Amma karki yinƙurim ɗaukar doka a hannu, dukda bansan waye Bukar ɗinba, kuma bansan meya yi miki ba, amma karkiyi ganganci, muyi komai a dokance"
Ta girgiza kai tace "bazaka gane me nake jiba a Yoseef, idan ban kashe mutumin nan ba kona masa illar da zan nakasta shi ba, to zan mutu ne" tai maganar tana kwanciya a jikinsa.
Yasa hannu ya rungumeta a jikinsa, shiru ya wanzu a tsakanin su.
Yusuf idan suka gaji da zaman ɗaki sesu dawo tsakar gida, suyi shimfiɗa suyi zaman su, sannan gaba ɗaya Yusuf ya shiga kiyaye abunda yasan zai ɓata mata rai.
Lokaci lokaci takan shiga ɓangaren Jamila, dan ta ɗau jaririyarta, dan har goya mata ita take yanzu, idan ta goyamata ita ta zauna guri ɗaya ta nutsu sosai kamar am goyawa yaro, Jamila tace "Widad waike bakya saka Atamfa ne,? Kullum se ƙananan kaya, baki san yawan saka abu ɗaya yana gundurar mijinki ba?zeso yaga kin canza ai"
Widad tace "nifa ban iya saka wata atmfa ba, tun taso wata ni bana saka wata Atamfa fa ko makamancin haka"
Jamila tace "Eh naga alama nima, amma Aikuwa yakamata mu bawa mijinki mamaki, ina da sabuwar atamfa na haihuwar Yusra da aka bani na barka, zan kai a ɗinka miki"
Widad tace "A'a karfa Yoseef yaji haushi, ko yace ban gaya masa ba"
Jamila tace "baze ce komai ba, zeyi mamaki ya ganki acikin Atamfa, karki damu ba abunda zece zeyi murna shima, kim san maza nason a basu mamaki, amma ina fatan kun shirya da shi"?
Widad tace "eh mun shirya, tun jiya amma da ƙyar yayi fushi dani sosai"
Jamila tayi murmushi tace "Yawwa tawan, karki ƙara bari ya kwana yana fushi dake kinji ko, sannan ke zakiyi dabarun daze dena daɗewa yana fushi dake"
Widad tace "to ni ya zanyi?, yana daɗewa beyi ba, amma idan yayi fushi da ƙyar yake sauka fa"
Tace "to kidena yin abunda ze sashi fushin mana, kuma Kinga yadda kike da kyan nan masha Allah, gaki da manyan idanu masu ɗaukar hankali masha Allah, ki dena kallonsa kamar yadda kike kallon sauran mutane, ki nuna masa Wata kissar sai mata (wanda be karanta littafin wata kissar sai mata ba na Ammar da Mufeeda, ya garzaya ya nemi nashi, akwai darasi a ciki 😍 da Nishaɗantarwa)
Idan zaki masa magana, ki dinga kashe masa ido, ko ɗan shanye idanunki kamar kina maye, dama na ganki masha Allah, shagwaɓaɓiya ce duk kidinga masa, ko yayi fushinma da kansa ze sakko, saboda karya yi missing wannan kallon"
Widad kawai ta kwashe da dariya, "Au dariya ma na baki? Aiko ki gwada zaki bani labari, ki dinga zuwar masa da abubuwan da bakya masa a baya, hakan zesa ya ƙara sonki, kin san mazan ne seda lallaɓawa, amma dukda haka suna mana ƙoƙari kuma suna haƙuri damu, sedai duk Allah ya bamu haƙurin zama da juna"
Hanne ce ta shigo, ta dinga jiyo dariyar Widad da Jamila, ta ƙaraso ta ɗaga labule, taga Widad a zaune da goyon 'ya suna hira da Jamila, ai shigowar da ba tayi ba kenan ta koma, tana tsaki.
Sunusi ne mijin Jamila ya dawo, dan haka Widad ta bawa Jamila' yarta ta fice, dama ba gaisawa suke ba da Widad, dan haka ne kulata ba bata kula shi ba ta fito ta tafi ɓangarensu, ta tarar Yusuf ya shimfiɗa tabarma a tsakar gida yayi ruf da ciki, yana karanta azkar.
Tana zuwa ta cire hijjabinta, ta hau kan bayansa.
Yace "ya hakane? sekin karyamin baya ne? So kike ki maidani gurgu?"
"Idan na maida kai gurgu ai dai mijinane bana wata ba ko?"
Yusuf yace "Allah? waye mijin naki, gayamin"
Tace "Yoseef ne mana"
Yace "to naji ɗagani, dan kin ƙara nauyi, matar ƙauye kawai kina ƙauye amma ƙiba kike"
"kaima Mijin ƙauye, kuma bazan tashi ba, idan ka takuramin kuma ka sha cizo ba"
Yusuf yace "hmm aikin taɓa cizona fa, akwai tabon a jikina"
Ta zare ido tace "yaushe na cijeka?"
"Ranar da aka yi ruwan sama mana da daddare"
Tace "wane ruwan saman akayi?"
Yasa hannu ya janyota daga bayansa, ya kwantar da ita a jikin bango yana kallonta, sannan yace
"Ranar da kika kusa taramin jama'ar garin nan, kalli inda kika cijeni, banda duka dana sha a gurinki"
Tura baki tayi tace "Eh anyi ɗin ba kaine ka... Se tai shiru
Yace " ƙarasa mana"
"Anƙi a ƙarasa ɗin" tai maganar tana dariya.
Yusuf ma dariya yayi ya juya yayi rigingine, ta kwanta a ƙirjinsa tace "Yayan Daddy, a rayuwa yadda da farinciki sune gaba gurin sada mutum da walwala, kalleni a garin da babu wauti, ba ruwa, ba waya, ba system, ba motoci babu duk wani abu na more rayuwa, amma gashi kai kaɗai kana bani farincikin da duk wannan abubuwan dana rayu dasu basu bani ba, dukda na sha wahala kafin sabawa da wasu abubuwan a garin nan, amma bayan na saba sena gane ita rayuwa a bace me sauƙi, yadda ka ɗauketa haka take zuwar maka Nagode sosai Ɗan uwana, kayi rawar gani a rayuwar Yarinyar da baka haɗa komai da ita ba"
Rungumeta yayi yace "ina fatan kasancewa dake har ƙarshen rayuwa ta Widad, dukda bani da tabaccin ina da mahalli a zuciyarki, kuma ban san yadda al'umma zasu karɓi Auren nan namu ba, amma nidai nasan ina sonki Widad, ban san yadda hali zeyi ba a nan gaba, ko dai mu kasance tare, kokuma mu rabu, amma ni dai nasan ina sonki, Dukda soyayya ta ta baya, banji naso wata kamarki ba, I love you Widad "
Ƙanƙame Yusuf tayi, tana jin wani irin shauƙi yana ɗibarta, a koda yaushe ta kanji farinciki idan yana tare da ita, koda suna gida yana a matsayin direbanta, ko tana cikin ɓacin rai idan taga yazo se taji damuwarta ta ragu, tana jinsa sosai a ranta amma ta kasa danganta hakan da Soyayya, a duk lokacin da taji damuwa ta mata yawa, tana haɗa ƙirjinta da nasa zataji bugun zuciyarta na daidaituwa,