Showing 162001 words to 165000 words out of 209297 words

Chapter 55 - Akidata Book 2 Hausa Novel Complete

01 Jan 2025

744

a maye, to ko ba'a mayen bama ya faru, sedai fatan Allah ya kyauta"

Amal ta tafi ɗakinta, dan itama fama take da kanta, wannan azabar ciwon marar da zubar jinin sun isheta haka.

Anty Saddiƙa ƙanwar Maman Nurat itace a gurin Nurat, itakuma maman Nurat ba'a barin kowa ya shiga inda take in ba likitoci ba, saboda tana ƙarƙashin kulawa ta musamman, Anty Saddiƙa taje salla Khalil na zaune a gurin Nurat, ai kuwa ta farka ta zaci zata ganta a ɗakin Dad ɗinta ya kulle ta, sedai tana buɗe ido tai arba da wani gurin daban, ta yunƙura zata tashi zaune, Khalil ya taho da sauri ya riƙeta yace  "yi haƙuri, ki kwanta kinji, karki gaggawa jikinki babu ƙwari"

A Shagwaɓe Nurat tace  "Brother ruwa zan sha"

Yace "ok bari in baki"

Ya ɗakko ruwam roba, ya buɗe ya bata ta sha, har ze gyara mata kwanciyarta ta kwanta, ta riƙe shi gam tana kallonsa, tana ƙoƙarin tuna meyafaru ihun Mummynta ta tuna, nan da nan ta razana tace masa "Mummy, Khalil Mummy na tana ina?"

Khalil yace "kwantar da hankalinki tana nan lafiya"

"A'a ban yadda ba, naji ihunta fa ranar, ban san meye ya sameta ba, tunda Daddy ya kulleni ban sake ganinta ba, waini ya akayi ma nazo nan ne?"

Khalil ya kalleta yace "kamar yaya ya kulle ki? Ya kulleki a ina?"

Nan ta kwashe duk abunda ya faru ta gaya masa, yai shiru yana nazarin maganganun Nurat, cikin kuka tace  "ina Mummy take? Dan Allah ka kaini in ganta dan Allah"

Khalil yace "ki kwantar da hankalinki, likitoci na can na kula da ita, idan ta farka zata zo ki ganta"

"to wai meyasa meta ne?"

"Bakomai, ta faɗi ne kawai saboda Dad ɗinki ya rufeki, bari Anty Saddiƙa tazo ta temaka miki kiyi wanka"

Bayan Saddiƙa ta shigone, Khalil ya tashi ya fita, a reception yaje ya samu Alhaji Musa a zaune, dan idan yazo Asibitin ya duba su Nurat nan yake dawowa ya zauna, dan gaba ɗaya haushinsa suke ji.

Ya zauna kusa da Alhaji Musa ya kalle shi yace  "garin yaya ƙanwar mahaifiyata ta faɗo daga bene?"

Alhaji Musa yace  "wace irin magana ce wannan? Ba a gabanka nayi wannan bayanin ba?"

Khalil ya kalle shi yace  "to ya akayi ka kulle Nurat? Laifin me tayi maka"

Da sauri Alhaji Musa yace  "tana ina? Nurat ɗin ta farkane?"

Yai maganar yana ƙoƙarin miƙewa tsaye, amma Khalil ya tareshi yace "na tambayeka kana ƙoƙarin tashi ina zaka?"

Yace  "wai ita Nurat ɗince tace maka kulleta nayi?"

Khalil yace "labari na samu, daga majiya me ƙarfin gaske, dan haka nake tambayarka garin yaya ka kulleta"

"wai Khalil yaushe ka koma haka? Yaushe ka koma mara kunyane?"

"ba rashin kunya bane, gaskiya ce dama ina da ayar tambaya akanka, wallahi muddin na ganoka da wani abu ba dai dai ba, naga wani abun kayiwa ƙanwar mahaifiyata ta faɗo daga bene, wallahi se nayi shari'a da kai, yanzun ma ba ƙyaleka zan ba, dan ba ƙaramin haushinka nakeji ba"

Alhaji Musa zeyi magana, amma Khalil ya dakatar dashi yace "ba abunda zaka gayamin, bana buƙatar jin komai daga gareka, amma tabbas ina nan ina bincike akanka, kuma wallahi ina daf da tsayawa a kotu a gaban alƙali da kai"

"Da nayi maka me?"

"in mun haɗu a kotu kaji"

Ya miƙe ya bar gurin, Alhaji Musa ya bi shi da kallo, yana tunanin me Khalil yake nufine?

Bayan Ramlah ta tashi daga mayen da take ne, Hajiya Halima tazo ta sata a gaba tana tambayarta   "Ramlah wata magana naji kina yi ɗazu cikin maye, wai Fahad yasa miki cuta, kekuma kin sakawa Bulama, wacce magana ce haka?"

Ramlah tace  "Eh to, dukda kince a maye nayi maganar kamar yadda kiji maganar haka take, Bulama shiya fara lalatamin rayuwa ta, na kamu da son ɗansa wanda hakan yasa na biye masa, sedai Bulama yaƙi goyon bayan ya aureni, yake ta cusa masa 'yar Daula ya aura saboda ya cika burinsa, soyayyar da nakewa ɗansa tasa na dinga biye masa ya koyamin shaye2, ya koyamin rayuwar banza nida shi ba abunda bama yi, nace ya Aureni amma yaƙi, kuma na gano yana da cuta me karya garkuwar jiki, dan haka na ƙuduri aniyar ramawa na komawa mahaifinsa, kuma da yake ɗan Akuyane ya karɓeni, ba tare da yasan ina mu'amala da ɗansa ba, dan haka shima ya kwasa, zuwa yanzu nasan uwarsa ma ta ɗauka, hakan yasa na ɗan rage abunda ke zuciyata gara muyi jinyar tare hadda ubansa"

Hajiya Halima ta ɗora hannu a ka tace "yanzu Ramlah abunda kikayi kenan? Ramlah gaba ɗaya kika biyewa namiji kika barbaɗar da rayuwarki da mutuncinki? Kin kyautawa kanki kenan?"

Ramlah tace "Mummy, bafa laifina bane wannan lamarin, duk wanda yazo neman Aurena se ki nunamin ai shi ba sa'an aurena bane, ina gidan Attajiri kamar Daula bekamata in Auri wane ba, ƙarewa ɗan uwanki ya biyoni ya lalata, na kamu da son ɗansa amma yai biris dani, kuma akan idinki nake fita ai, kin taɓa tuhumata ina muke zuwa nida Fahad idan mun fita? Me yasa? saboda idonki ya rufe ke burinki ya kawo miki masu siyan kadarori ki tara kuɗi, don't blame me for this please "

Ta tashi tai tafiyar ta ɗaki ta bar mata falon, Hajiya Halima ta dafe kai ta fashe da kuka, Bulama ya riga ya gama cutarta a rayuwa, ba ta san mema za tace a game da shi ba, ya lalata mata rayuwar 'ya, kuma wai yanzu Ramlah na ɗuke da cuta me karya garkuwar jiki, wanda ta samune a sanadin ɗansa, kuma ya dawo yace a kashe mata ɗa, ta rushe da kuka harda sheshsheƙa, gaba ɗaya komai ya rikice mata, tama rasa meye abunyi, wannan wace irin masiface haka take bibiyar ta? Daga wannan se waccan gaba ɗaya 'ya' yanta sun barbaɗe, haka ta dinga gunjin kuka ita ɗaya a falo, Amal ta ƙarawa ƙofar ɗakinta key, dan bata son tashin hankali.


Da safe Fahad ya shiga cikin gida, domin gaida iyayensa, sedai yan zaune a falon Iman nata masa surutu amma sam hankalinsa baya kanta, yayi zurfi a tunani can ya ɗago kai yace "ke wai ina Mummy ne?"

Iman tace "tana sama ɗakin Daddy"

Ji yayi kamar ta watsa masa wuta, ta ina ze fara gayamata hakinda ake ciki? Koma ya gayamata ai yasan aikin gama ya riga ya gana zuwa yanzu.

Yana nan zaune Sega Bulama yana Sakkowa, hannunsa ɗauke da jakarsa, Mummy sanye da doguwar rigar baccinta, ta riƙo masa wayarsa suna hira, Fahad yaji kamar yaje ya make Bulama saboda tsabar baƙin ciki da takaici, ga wani irin tausayin mahaifiyarsa ya kama shi.

Hajiya Sarah ta kalli Fahad tace  "yau Allah ya nufe ka da shigowa cikin gidan kenan? Yaushe rabonka da shigowa"

Bulama yace "wai gidan ubanwa kake shigewa ne? Ko haryanzu yawon kake baka kwana a gida?" ga mamakinsa seya ga Fahad ya maka masa wata uwar harara, abun da be taɓa yi masa ba, ya kalli mahaifiyarsa yace  "Mummy ina kwana?"

"Lafiya ƙalau, ka tashi lafiya?"

"Lafiya ƙalau, dama na shigo mu gaisa ne zan karya"

Tace "shi Daddyn naka bazaka gaishe shi ba?"

"Ai na gama gaidashi, ni da sake gaisheshi har abada"

Kallonsa sukayi gaba ɗaya, Hajiya Sarah tace  "Fahad, daga kan kayan shaye2 naka ka taso ka shigomin falo ko? Shine har kake gayawa mahaifinka wannan maganar?"

Alhaji Bukar yace "ƙyaleshi, ina daf da maganinsa akan wannan mummunar ɗabi'a ta shaye2, dank yake zancen, ban agogona zan fita ina da ayyuka da yawa a Office "

Yasa hannu ya karɓi agogonsa, yai waje bayan fitarsa Hajiya Sarah ta kalli Fahad tace " Fahad, meyasa ka gayawa mahaifinka wannan maganar haka? Kai lalacewar taka harta kai kayiaa mahaifinka haka? Me yayi maka? "

Yace " bakomai "

" Bakomai amma ka faɗa masa wannan maganar? Abunda kayi ya dace kenan?"

Ya girgiza kai alamar a'a

"to meyasa kayi, salon mutane suji suce ni nake saku a turbar banza, na ku Wulaƙanta mahaifinku?"

"Nifa Mummy bakomai, kema da kin san me yayi da baki faɗi wannan maganar ba, kawai dai Allah ya kyauta"

Ya mike a fusace ya baf falon, tabi bayansa da kallo, Iman tace  "Mummy"

"Na'am"

"wai kuwa idonki biyu, jiya da Maman su Amal tazo gidan nan?"

"haba dai? Gidan nan tazo? Ai ban sani ba"

Iman tace "wallahi tazo, bayan ƙarfe goma se bala'i take tana neman Daddy"

"subhanallah, Allah yasa ba'a akan Ramlah tazo ba, saboda kin san halin ɗan uwanku sarai, ina kyautata zaton akwai alaƙar banza a tsakanin sa da Ramlah"
. "Mummy ya akayi kika sani?"

"last week na ganta ta fito daga sashinsa, na tambaye ta amma bata gayamin komai ba, sema baƙar magana da tayi min"

Iman tace "Umma kiyi ta haƙuri, Yaya Fahad se Addu'a gaba ɗaya zamansa a ƙasar waje ba abunda yasa masa se koyar mugayen halaye"

Hajiya Sarah tace  "idan da zaman ƙasar waje dai to harda halinsa, meyasa shi Anwar be lalace ba se shi? Bani da abunyi se dai yi masa addu'a, baya jin faɗa baya jin rarrashi, babu wanda banyi ba, amma duk baya ɗauka"

"Mummy kiyi haƙuri, wataran se labari ze dena insha Allah"

"Mhmm Iman kenan, yaushene watarn ɗin? Mutum ya girma amma kullum ba hankali, Allah ya kyauta dai kawai".

Yanzu ma Bulama yana zaune a Office, kiran wayar Me Adda kawai yaje amma taƙi shiga, yai shiru can wayar ta fara ringing, cikin hanzari ya ɗauka ya zata me Adda ne, sedai yaga baƙuwar lambace, ya ɗaga yai sallama

"justice A dutse ne ke magana '

Bulama yace " ok nagane, ya kake ya aiki? "

" Alhamdilillah, dama na bugo in sanar makane da cewar tawagar lawyoyi da ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam sun ɗaukaka ƙarar shari'ar Yusuf da nayi, kuma ina kyautata zaton ƙarƙashin jagorancin shahararren lawayrn nan ɗan gwagwarmaya wato Barrister Adam A Adam, dan haka tun wuri kasan abunyi!!!





(Alhamdilillah masha Allah, nagode sosai Allah yasaka da alkhairi, da addu'oinku da na samu bisa rashin da akayi mana, nagode sosai Allah ya bar zumunci)

AMANA! AMANA! AMANACE!!!
AYSHERCOOL
07063065680
11/30/21, 8:20 AM - Buhainat: LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680

(Albishir ga masoya, ma'abota bibiyar litattaafaina, dama ta samu zaku fara samun litattaafaina na audio, akan YouTube channel ɗina me suna Cool Arewa TV
https://youtube.com/channel/UCD5vnvA5laU8ti4LLz2_QEg

Kuyi liking sannan ku danna subscribe, domin fara samun litattaafaina na audio, nagode sosai da ƙaunar ku gareni"

_(INNALILLAHI WA INNA IALAIHI RAJI'UN  ina amfani da wannan damar gurin miƙa saƙon ta'aziyya ga Ɗaukacin zuriyar Hajiya Aisha Muhammad (Baba) bisa babban rashi da mukayi na rasuwar ta ina fatan ubangiji Allah ya jiƙan ta yai mata rahama, ya kai haske kabarainta, ubangiji Allah ya duba zuriyar da ta bari, ya bata ladan ɗawainiya da iyalI da tayi tsawon ranta, ubangiji Allah ya jiƙan kafatanin  wanda suka rigamu gidan gaskiya Musulmi, idan tamu tazo Allah yasa mu cika da kyau da imani_)

IN THE MEMORY OF LATE HAJIYA AISHA MUHAMMAD, I DEDICATED THIS PAGE TO LATE HAJIYA AISHA MUHAMMAD (BABA) MAY ALLAH SUBHANAHU WATA'ALA, GRANT HER JANNATUL FIRDAUSI AMEEN _

142_143

Yusuf ya dinga jujjuya takardar nan, ya kalli Barrister Hafiz yace  "Ya akayi ta rubuta takadda a bani?"

Barrister Hafiz ya matso daf da Yusuf, ya shiga yi masa magana ƙasa ƙasa  (ni kaina da nake ɗakko rahoton banji me yace masa ba)

Yusuf ya sunkuyar da kai yana sauraren Hafiz, Hafiz ya gama gaya masa abunda ze gaya masa, Yusuf ya dinga jinjina kai, Hafiz yace "ka sairaremu nan da wani ɗan lokaci, mungode sosai"

Sukayi musabiha da Yusuf, suka miƙe suk tafi, Yusuf kuma aka maida shi inda yake, hannunsa ɗauke da takaddar da'akace Widad ce ta bayar a bashi, yaje ya samu guri ya zauna yana jujjuya takaddar da'aka bashi yana sake karantawa.

A hankali ya furta  "Allah yasa kina lafiya Widad, koba wane hali kike Allah ya kuɓutar dake, ya sake ƙaddara saduwarmu dake"

Widad tana nan a tunanin Allah yasa saƙonta ya isa inda ta aika shi, dan zuwa yanzu ta sare da zata bar gurin nan, dan bata ga hanyar barin gidan nan ba, Amma Allah yasa kafin ta mutu Yusuf ya yafe mata, karta mutu yama ɗauke da pain ɗin bada shedar ƙarya da tayi akansa.
Da ta lumshe ido se hawaye, wani na bin wani, tana tunanin anya zata samu sassauci game da wannan halin ni 'yasu da take ciki? Ita dai fatan ta Allah ya haɗa ta da Yusuf ta nemi afuwarsa.

Ganin Widad dagaske ba zata bashi inda dukiyar take ba, tana ta faman raina masa hankali, ya ƙudurce tabbas ze ɗakko mahaifiyar Yusuf yayi garkuwa da ita, ko ta bashi, ko kuma ya illata ta a gabanta, tunda ya fuskanci bata son duk wani abu daze saka Yusuf da ahalinsa su shiga damuwa.
Dan haka ya ɗakko wayarsa, ya kira me Adda  "Allah ya temaki Oga, in ba kai waza mu duƙawa muci?"

Bulama yace "kai kana inane? Kana  cikin garin nan ne?"

"A'a, na ɗan baza yin wata harƙalla, duk cikin iya taku da ɓoyewa masu saka na mujiya"

"ina son ganinka a yau ba se gobe ba, a cikin daren yau nake so kaje ka ɗakkomin tsohuwar wancan sakaram yaron"

Me Adda yace "sa hankalinka a inuwa, turo adreshinta, zamuyi ram da ita mu kawo maka"

Bulama yace "Good, zan turo maka adreshin, a daren yau nake son a gama komai, ku ɗakkota ka kawomin ita"

"An gama yallaɓai" me Adda yai maganar kamar yana maye.

Likitoci suka yi iya abunda zasu iya akan Mahaifiyar Nurat, amma babu wani cigaba, ta gaza farfaɗowa gashi jini yaƙi tsayawa, numfashi kawai take amma sam zuciyarta bata harbawa yadda yakamata, tuni danginta da 'yan uwanta suka cika Asibitin, Alhaji Musa yayi mamakin yadda akayi suka ji, bayan shi dai be kira kowa ya gaya masa ba.

Nan suka shiga tambayar ba'asi, akan yadda akayi' yar uwarsu ta faɗo daga kan bene?

Alhaji Musa yace  "Wallahi ta fito ne daga ɗaƙi, zata sakko daga kan bene kawai ta zamo ta gangaro, dama tun safe take cemin tana jiri, nace mata ko  Asibiti zamuje tace in bari seda yamma, ina ga harda jirine ma ya ɗebe ta yasa ta faɗo"

Barrister Khalil kallon Alhaji Musa kawai yake, ji yake tamkar ya danƙo wiyansa ya rufe shi da duka, dan sam beji ya gamsu da maganar da ya faɗa ba.

Amal ta shirya tsaf, dan taje a zubar mata da ciji ba tare da mahaifiyarta ta san halin da take ciki ba, gaba ɗaya ta tattara ta zuba musu ido, dan itama fama take da kanta, ko gani bata iyayi sosai sedai dususu saboda tsabar ɓacin rai da damuwa da yake ta'azzara mata hawan jini, gaba ɗaya ta koma kamar wata zararriya, yauma ta tashi tana ta fama da kanta, jiri da ciwon kai jininta ya hau, tana kwance a falo tana fama da kanta, Amal tazo zata fice.

"Amal ina Ramlah ne?"

Amal tace "tana ɗakinta, inaga yauma tayi shaye2 tana can tana bacci"
. Hajiya Halima tai ajiyar zuciya, tace "kekuma ina zaki? Naga kamar fita zakiyi"

"Eh zan ɗan fitane, ba nisa zanyi ba"

"Amma kina kallon yadda nake fama, ina kwance ina fama da kaina, amma zaki saka kai ki fice ki barni a haka?"

Amal tace  "Mummy, na matsu in fitane ina da wani uzuri na gaggawa, ba daɗewa zanyi ba, ga Ramlah can kuma tana nan ai, ba daɗewa zanyi ba"

Tai maganar tana tafiya, a haka harta bar falon ta fice abunta.

Tana zaune a mota ta kira Alhaji Haruna, ya ɗaga ba tare da yasan wanda ya kira shi ba, "na gaya maka ina ɗauke da juna biyu, Amma kaƙi ɗaukar kowane mataki ko? To ka saurareni wallahi zan tona maka Asiri, duniya taji abunda ka aikata"

"wai ke ni dan Allah ya kike son inyi ne? Har yanzu baki fanshe bane? Me kike so inyi miki?"

'haka ma zaka ce? To shikenan, ciki dai nakane, kai kayi shi, wallahi ba zanyi abun kunya ni kaɗai ba, na gaya maka'

Ta ajiye wayar, tare da yin ajiyar zuciya, ta kunna motar ta ta fita.

Suka yi waya da wannan Nurse ɗin, wadda tace zata taimaka mata ta zubar da cikin nan, ta gaya mata a dai dai inda zasu haɗu.

Aikuwa tana zuwa suka haɗu, ta ɗau Nurse ɗin a motarta, ta fara nunawa Amal hanyar zuwa Gurin, Amal tace "nifa gaskiya tsoro nakeji, wallahi ji nake kamar wani abu ze faru"

Nurse ɗin tace "haba ke kuwa, amma dai wannan ne karon farko da zakiyi abortion ko?"

Amal ta jinjina kai alamar eh, Nurse ɗin tace "karki damu mana, ai ke naki cikinma ƙaramine, nan da nan za'a cire shi babu wani tashin hankali, ɗan pain ɗin kaɗanne, ke ciki koya kai 9 months Doctor Hamisu ze jajjageshi ya cire shi tsaf, dan haka ki kwantar da hankalinki, komai ze tafi normal"

Sukaje Asibitin, Nurse ɗin ta jata har office ɗin doctor Hamisu, suka tarar yana aiki a system, Nurse ɗin ta gaisheshi tace  "Doctor, ga customer fa cikine take son a cire mata"

Ya ɗago ya kalli Amal sannan yace "cikin wata nawane?"

Amal tace "nima ban sani ba, amma naji da akamin test ance watansa ɗaya be cika biyu ba"

Doctor Hamisu yace "ai wannan ba abun damuwa bane ba, za'a cire shi ba wata wahala, an gayamiki kuɗin aikin?"

Tace "eh an gayamin, zanyi transfer ɗin kuɗin".
Ya ɗago ya sake kallon ta yace "you look familiar to me, is like I know you somewhere"

Amal tace "eh nima ina ganin kamar na sanka fa, kamar likitan dake duba Widad shekarun baya"

Yace "exactly, that's where I know you, ya maman naki?"

"tana lafiya ƙalau"

"masha Allah, amma ya akayi ke kuwa wannan abun ya faru haka?"

Amal ta ɗan ɓata fuska tace "wallahi wanine yamin Akuya, daga zuwa kai masa saƙo, shiyasa nake

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login