Showing 117001 words to 120000 words out of 209297 words
wallahi, kema sema wulaƙantaki,"
Amal ta ɗau wayarta ta tura masa saƙo tace "ka cigaba da kiran Mummy, kana cewa kana son Magana dani, wallahi idan baka yi wasa ba sena gayamata abunda kayi min, kuma kasan halinta sarai, kasan buyaginta zata maka abunda kai kanka zaka kasa gane kansa, dan haka muddin ba zaka cika sharaɗina ba, wallahi ba zan baka ba na gaya maka, kuma ni wannan kuɗin sunmin kaɗan, nima a account dina ina da wanda suka fisu"
Ta kashe wayarta ta sake kwanciya, ya duba message ɗin, yaja wata ajiyar zuciya yana cije leɓe, totally ta riga ta gama raina masa hankali, yama rasa me zeyi ko me zece.
Yana nan tsaye yana tunanin mafita kiran wayar Bukar ya shigo wayarsa, ya ɗaga jiki na tsuma, yace "Hello"
"Haruna, yau muna da zama na gaggawa, cikin dare dan haka duk ku tattaru"
Yace "harda Halima?"
"banda ita, sannan kazo min da wannan takaddar, zamuyi magana a kai itama"
Daga nan ya kashe wayar, Alhaji Haruna ya yakice gumi, yana huci Amal ta masa rashin mutunci, dan kawai abu ya shiga tsakaninsu se tayi masa haka?.
Mutan ƙauyen da Widad suka zauna suka dinga taradaddi, kowa da abunda yake faɗa wasu suna dama megari yayi wauta, wataƙila dama can 'yan fashi ne ko wasu masu laifin ne, amma daga zuwansu ya karɓesu, be san daga inda suke ba.
Hindu kam kuka, kamar wadda aka kama uwarta, ita kanta Hari gaba ɗaya jikinta a sanyaye yake, wunin ranar gidan daga masu koke koke, se masu salallami, Hanne kuwa ko a jikinta.
Koda Sunusi ya dawo, Jamika ta gaya masa abunda ya faru, dan haka yace dole gobe insha Allah ya tafi kank, yaje yaji ba'asin abunda ya faru.
Jamila tace "dan Allah karkaje, kar kaima a kama ka, dan na san da kana nan wataƙila da kai zasu haɗa"
Sunusi yace "da nayi musu me? Kince an kama Saleh, kuma Saleh shiya kawo su nan, meyasa aka kama shi, dole zanje inji"
Daddare megari ya tara iyalansa yace "to wannan bayin Allah dai, ni dai a ɗan zaman da mukayi dasu, ban tunanin mutane ne marasa gaskiya, ko makamancin haka, zamanmu da su ma mu alkhairi ya zame mana a garin nan, dan haka dan Allah ina roƙonku da kuyi haƙuri ku dena kuka, kukan ya isa haka, Hasana nasanki da son 'ya' ya kuma zamanmu dasu jin shaƙu dasu sosai, dan Allah kidena kuka kiyi musu Addu'a, Hindu Baffa kema kukan ya isa haka, muyi musu Addu'a, Allah ya basu mafita sannan Hari a samo makulli a rufe musu ɗakinsu, kar wanda ya sake shiga tunda da kayansu a ciki "
Hari ta tashi ta shiga ɗakinta ta samo mukulli, tana ƙoƙarin rufewa taga bokitinsu a tsakar gida, ta tafi ta ɗakko bokitin, kawai ta fashe da kuka tace " Allah sarki Wudas, da yanzu muna faɗa akan ruwan zafin da zata yi wanka, tace sena bata na bawa mijin ta, ban taɓa ganin abun tausayi kamar yau ba, yadda ta rikice tana kuka, Allah sarki Allah ya fitar dasu"
A kaita bata haƙuri, aka kulle ɗakinsu aka bawa Megari mukullin, ya kai ɗakinsa ya ɓoye.
Yusuf yana kwance a cikin cell, an raba masa cell shida Saleh, sauro yana ta masa buduri a ka, yai rigingine yana tunanin ya Umma zataji idan wannan mummunan labari ya isheta?.
Aka buɗe ƙofar cell ɗin, wasu 'yan sanda suka shigo su biyu, ya tashi zaune yana kallon su.
Ɗaya ya kalleshi yace "munafuki, kalleshi kamar na Allah, amma ƙasurgumin Azzalumi ne, kai garkuwa da' ya ka koma kayi da Ubanta, saboda kai Azzalumi ne, kuma a haka wai kai ɗansanda ne"
Yusuf yai shiru be ko ɗaga kai ba, ɗayan yace "rabu dashi corporal Sani, zuwa gobe in Allah ya kaimu semun sauya halittun fuskarsa, kafin 'yan jarida suzo, a buga shi a nunawa duniya shi, azzalumin banza dana wofi kawai"
Yusuf dai yai shiru bece komai ba, suka gama zage zagensu suka fita, suka sake rufe shi, tun Abincin safe Yusuf be kuma cin komai ba, ga doguwar tafiyar da suka yi, amma sam baya jin yunwa tunanin makaomarsa kawai yake a wannan hali da yake ciki.
Nurat na kwance cikin dare, taji Mahaifinta yana waya ƙasa ƙasa, ya fito daga ɗakinsa da alama dai fita zeyi, ta kalli agogo ƙarfe biyu da rabi na dare, ta buɗe ƙofar ɗakin ta fito falo, aikuwa yana fitowa ya ganta a falo, ya ɗan haɗe rai yace "ke me kike yi a falo a wannan tsohon daren haka?"
Tace "ruwa na fito sha"
"ina ma fridge ɗin dakinki?"
"yayi sanyi da yawa, duk ya zama ƙanƙara shiyasa na fito"
Yace "to kin sha ɗin ne kokuwa?"
Tace "A'a yanzu dai zan sha"
"maza jeki sha, kizo ki wuce ki kwanta"
Ta nufi hanyar kitchen, tana tunanin ina zashi a wannan tsohon daren, ta fito ta tarar da shi a falon a tsaye, yace "kinsha ruwan?"
Tace "eh na sha"
"to maza ki wuce, ki tafi ɗakinki ki kwanta"
Harta juya ta tafi, ta waigo taga yana tsaye yana kallon ta, tace "Amma naga kamar fita zakayi, ina zaka yanzu dare yayi sosai"
"Yaushe na fara wasa dake? Ko kuma kika zama uwata da zaki dinga tuhuma ta haka?"
"hmm Daddy kenan, ai kaine kake abun tuhumar, wani irin abune wannan da ba'ayi ido ma ganin ido ba se yanzu a tsakiyar dare haka hmmm Allah dai ya kyauta?"
Ta buɗe ɗakinta ta shige, ta barshi tsaye yana binta da kallo, yarinyar da idan ta ganshi jikinta ke rawa, itace take gaya masa magama haka, tabbas uwarta ce ke zigata kuma zeyi maganinsu gaba ɗaya.
Kamar yadda suka saba haɗuwa yauma sun hallara gabaɗayansu, suna zazzaune a ɗakin Hotel ɗin da ya zamana babu ma me kama shi sesu.
Bukar yace "kyakkyawan labari"
Alhaji Musa yace "muna jinka"
Alhaji Bukar yace "yaron nan yazo hannu"
Sukace wane yaron?
Alhaji Bukar yace "ku duk baku sani ba, dukda yadda da labarin ya yaɗu a daren nan? To ina nufin Yaron nan Yusuf, direbanta wanda aka yi garkuwa dasu tare"
Sukace "Alhamdilillah, abu yayi kyau"
Alhaji Bukar yace "An kamosu a wani ƙauye a Bauchi, inda Saleh ya basu mafaka, yanzu haka yana hannun 'yan sanda, za' a tattare duk wata sheda da ta kamata daga nam za'a kaishi kotu, zamu saki kuɗi ayi masa shari'a da hukuncin daya dace da shi, saboda babu wanda ya ta:a kawo mana cikas da tangarɗa a harkar nan kamar shi, kunga daga nan babu wanda ya isa yace mune muka sa akayi garkuwa dasu"
Alhaji Munir yace "good, wannan abu yayi kyawuuu sosai, kuma ya tafi yadda ake so, dan haka semu hanzarta, mu kuma samu hanyar da zamu ɓalli namu kason tun kan Daula ya bayyana, dan shi har yanzu bamu san fa inda yake ba, kar muje wasu su rigamu karɓa abun nan fa"
Bukar yace "na toshe duk wata hanya da zata saka wani ya mallaki abun nan bamu ba, sannan dole nasa a matsa yaron nan, idan ma abun yana hannunsa ya faɗi inda suke"
Alhaji Musa yace "kai amma abu yayi kyau wallahi, komai ya tafi yadda yakamata"
Alhaji Bukar yace "Haruna ina takaddar da wancan yaron ya bari, ɗan gurin Halima? Shima nasa a nemo shi, duk inda aka ganshi kawai a kawar dashi, bama san duk wani abu da zesa a samu sheda a kanmu"
Alhaji Haruna yai tsilli tsilli da ido yace "Amm.. Mm.. Wallahi an ɗan samu akasine, na rasa inda takaddar ta faɗa amma ina ta ƙoƙarin dubawa"
Alhaji Bukar yace "Amma kasan bana son akasi ko?"
Yace "Ayimin afuwa dan Allah, Insha Allah za'a nemota in kawo"
Alhaji Bukar yace "shikenan, nan da kwana bakwai, na baka isashen lokaci, nan kusa nake so a fara shari'ar yaron nan, ba da nisa ba, kuma ina son a rufe duk wata hujja da zata bayyana mu"
Alhaji Haruna yace "insha Allah, zan kawo takaddar nan ba da jimawa ba"
Haka suka gama tattaunawa sannan suka watse.
Widad ce ke ƙoƙarin farkawa, se jujjuya wuyanta take tana kuka cikin bacci, "Wayyo Allah na, yuzarsef yunwa nake ji, zuciya ta ciwo take, Yoseef dan Allah, dan Allah ka dawo please! Ta farka a gigice tana kiran Yoseef! Yoseef kana inane?"
Bulama ne da Matarsa Hajiya Sarah a gigice suka yi kanta gaba ɗaya, Bulama yace "Sannu daughter, sannu ki kwantar da hankalinki, kin ganni a tare da ke, ga Maman Iman ma, an kuɓutar dake ki kwantar da hankalinki"
"Ni bazan kwantar da hankalina ba, ina mijina yake? Ina Yoseef kace su sakarmin shi, ni ba saceni yayi ba, wallahi idan basu sake shi ba mutuwa zanyi, laifina ne, duk saboda ya ceceni haka ta faru dashi, beyi laifi ba, tun farko seda na gaya masa death contract ne amma ya amince, kaga abunda nake nufi Yoseef, dan Allah ku ƙyaleshi idan wani abu ya sameshi bazan yafewa kaina ba, dan Allah ka cewa Bukar na dawo, ni yazo ya kamani yasa a sakarmin mijina dan Allah "
Tai maganar wasu irin hawaye na ambaliya daga idonta, idanun da suka rine zuwa kalar ja jawur suka kumbure.
Bulama yace "toni ina na san wani Bukar, balle in nemo miki shi? Ke kaɗai kika sanshi, ni ban san a inda yake ba"
Kafin ya rufe baki...
Ayi subscribing YouTube channel ɗina please 🙏 🙏 🙏 🙏
Ayshercool
11/18/21, 7:47 AM - Buhainat: LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
(Albishir ga masoya, ma'abota bibiyar litattaafaina, dama ta samu zaku fara samun litattaafaina na audio, akan YouTube channel ɗina me suna Cool Arewa TV
https://youtube.com/channel/UCD5vnvA5laU8ti4LLz2_QEg
Kuyi liking sannan ku danna subscribe, domin fara samun litattaafaina na audio, nagode sosai da ƙaunar ku gareni"
108_109
Kafin ya rufe baki ta cire drip ɗin hannunta tayi jifa dashi tace "ni na sanshi, kuma zan nemo shi insha Allah, dole a sakarmin Yoseef ɗina"
Hajiya Sarah tace "haba Widad, baji da lafiya fa, drip ne a jikinki, ya zaki cire ki yar?"
"ni lafiyata ƙalau, ba abunda yake damuna se son inga an sakarmin mijina"
Bulama yace "wai waye mijin naki ne?"
Tace "Yoseef, mijina ne, Aure mukayi dashi"
Hajiya Sarah tace "wane irin aure ba tare da izinin magamabatnki ba? Anya ba ciwon nakine ya tashi ba?"
"Karka ƙara dangantani da hauka, na gaya maka in bahaka ba zan maka haaukan ganin idonka"
Ta diro daga kan gadon zata yi waje, aka Riƙeta da ƙyar tana fizge fizge seta ƙwace ta fita.
Da Alhaji Musa ya koma gida a harabar gidan ya tarar da Nurat a zaune yai parking ya fito ze wuce ta kalle shi ta dauke kai, ya kalleta yace "can't you greet your Dad?"
"I don't think my Dad still loves me"
Yace "why"
"saboda yadda kake treating ɗina kamar ba 'yarka ba" ta ƙarasa maganar tana tashi ta bar gurin ya bita da kallo.
Harta shiga ɗaki taji ta gaji da zaman, ga Khalil yace zezo amma shiru bezo ba, fitowa tayi daga ɗakinta ta haɗo tea, ta dawo falo ta zauna ta kunna TV ta nayi tana ɗan shan tea ɗinta a hankali.
Ta tarar har angama title ɗin news ɗin an fara labaran, sedai ana fara gabatar da labarin su Yusuf jikinta ya hau shaking, gabanta ya shiga dukan uku uku, ai ba'a gama labaran ba ta saki kofin tea ɗin dake hannunta, da ibu zata saka amma ta toshe bakinta, ta shiga ɗakinta da sauri ta kulle ƙofa, zubewa tayi a gurin ta shiga rusar kuka kamar wadda babanta ya mutu, ta dinga kuka tabbas babu ko tantama wannan ƙulle ƙullen mahaifinta ne, wataƙila shine ma dalilin kwanansa a waje jiya, wannan labarin sam babu ƙamshin gaskiya a cikinsa, ta yaya za'ayi garkuwa da mutane kuma an gano su ace Yusuf ne ya saceta baze yuwu ba.
Ta ɗakko wayarta ta shige toilet, ta nemo lambar Khalil, tana kuka Khalil ya ɗaga, yana ɗagawa ta fashe da kuka yace 'Nurat lafiya kuwa, meyafaru ne? "
"bakaga News ba na yau, wanda akayi da safen nan?"
Yai ajiyar zuciya yace "Na gani sister"
"Amma meyasa baka gayamin ba? Kaga abunda ya faru kaga abunda akace Yusuf yayi ko?"
Khalil yace "nagani, bana son in ɗaga miki hankaline, amma tun jiya da daddare na gani, gefw guda kuma Anwar ɗan gidan Hajiya Halima shima ba'asan inda yake ba, duk na ɓoye ne, dan gudun tayar miki da hankali"
Nurat ta share hawayenta tace "Yaya Khalil, ka dena min ɓoye ɓoye, lokaci yayi da zaka temakeni, Khalil mahaifina azzalumi ne wallahi, jiya be kwana a gida ba, nasan saboda wannan dalilin ne, Wallahi idan ba'ayi wani abu a kai ba, rayuwar Yusuf zata shiga garari"
"Nasani Nurat, but am doing my best kinji, bari kinga yanzu zan shigo gidan naku kafin in wuce office"
Nurat tace "No karkazo, ka san shi da zargi, zefara zargin wani abune dan Allah karka zo ka bari kawai, mu dinga communicating ta waya ya isa, bana son ya gane komai"
Khalil yace "shikenan, naji ki kwantar da hankalinki, komai zezo da sauƙi zancigaba da bibiya inga yadda zata kaya"
"Shikenan brother nagode sosai, dan Allah ka ƙara ƙoƙari"
"karki damu sister, Insha Allah i will do my best for you"
Ta jinjina kai ta ajiye wayar, tana ci gaba da jujjuya kai tana tausayawa Yusuf.
Ma'aikatan gidan Alhaji Daula suka rikice jin kabarin abunda ya faru da Yusuf, sun kadu matuƙar gaske dukda wasun su suna jin haushinsa amma a zaman da suka yi dashi sun sanshi da sanyin hali, basa tunanin ze aikata wannan aiki haka.
Ɓangaren Suleiman makuwa ya kaɗu Matuƙa da jin wannan labarin, hankalinsa ya tashi sosai ya tafi headquarter da kansa dan ganin Yusuf, amma fafur aka hanashi ganinsa, dukda shima babban jami'ine amma a kace baze ganshi ba, ana kan gudanar da bincike akansu ne.
Yusuf kam yaci duka da kulki a hannun kuratan 'yan sanda, yama rasa dukan me suke masa? Me suke yai musu su ƙyaleshi, ya daku iya dakuwa ƙafafunsa da bayansa ya gaya masa saboda duka, yana nan gurin a duƙe wani ɗan sanda ya shigo aka ajiye ɗan sandan kujera ya zauna, ya sallami kowa daga gurin, ya ɗan ƙurawa Yusuf ido sannan yace "Malam Yusuf"
Yusuf yai shiru be ɗagoba, yana nan zaune ya durƙusar da kansa.
"Ina so karka bamu wahala, kuma karka bawa kanka wahala, yana da kyau ka amsa laifinka tun a nan dan muyi gaggawar kaika kotu a yanke maka hukuncin daya dace, sannan abu na gaba shine, Widad ta baka bayanin inda dukiyar da mahaifinata ya ware take?"
Ɗago kai Yusuf yayi, ya kalli ɗan sandan, se yanzu ya ƙara tabattar da cewa wannan abun set up ne kawai, an shirya wulaƙant shi ne kawai.
Ya maida kansa ya sunkuyar, yaƙi magana.
Cikin shouting ɗan sandan yace" ba magana nake maka ba? Ta gaya maka ko kuwa, ka sauƙaƙawa kanka ka gayamin suna ina? "
Cikin dakiya da juriya irin na Yusuf, ya sake gyra zamansa ya ƙi kallon ɗan sandan, ai kuwa ɗan sandan nan ya harzuƙa, yasa aka kawo masa kulki, ya ding bugawa Yusuf, Yusuf ya dinga juyi a gurin saboda azabar wahala dayake sha, dan dukan kulkin nan ba ƙaramin shigarsa yake ba, amma sukayi sukayi, Yusuf yaƙi cewa uffan.
Widad kam aka hana 'yan jarida ganinta, aka gama bata magunguna da gwaje gwaje, Bulama ya ɗauketa zuwa gidan sa, Widad sam bata iya ma magana yanzu, haka aka tafi da ita gidan Bulama.
Likitoci suka bada rahoton, wai ta samu raunuka a jikinta, kuma ta galabaita saboda rashin Abinci da azabtarwar da ta sha hannun Yusuf da yayi garkuwa da ita.
Bulama ya tafi da ita gidansa, sedai banda sharar hawaye babu abunda take yi, ƙarshe ma maganar ta gagara, aka bata ɗaki, suna shiga ɗakin ta zube a ƙasa tana maida numfashi, saboda nauyin da taji ƙirjinta yayi mata, ta kalli Bulama tace "meyasa ka kawoni nan?"
Yace "A'a, daughter nanma ai gidanku ne, meye na damuwa kuma?"
"Nan ba gidanmu bane, ina Daddy yake tunda nazo ban ganshi ba, yana ina?"
Hajiya Sarah ta kalli Bulama, shima ya kalleta yace "Amm daughter kin gane, ki kwantar da hankalinki kinji, Daddyn ki yana nan lafiya, kuma yana nan zuwa insha Allah, kedai ki kwantar da hankalinki kawai saboda lafiyarki"
Widad tace "ni babu abunda ya sameni, ka gayamin ina mahaifina yake? Ina Daddy na"
Hajiya Sarah tace "Kaga, Ka gayamata gaskiya kawai, tunda har Allah yasa an gano ta bashi da wani amfani a cigaba da yi mata ɓoye ɓoye, dan haka kawai ka fito ka faɗa mata gaskiya"
Bulama yace "Sarah meyasa kike hakane? Kina ganin halin da take ciki amma kina wani zance daban meyasa kike hakane?"
Hajiya Sarah tace "dan meyasa ba zanyi haka ba, ka gayamata gaskiya mana da wuri, kasan halinta sarai ba baka sani ba, idan ta sani daga baya duk seta ɗaga mana hankali gaba ɗaya gidan nan, ni a yanzu hakama a tsorace nake, kafi kowa sanin halinta"
Bulama yace "koma meye halin nata ba haƙuri zakiyi ba, da 'yar kice haka zaki ce? Kiyi haƙuri mana muga yadda hali zeyi"
Sunata jayayya a tsakanin su, Widad ta zame jiki ta zauna a gurin, tai musu shiru ta lumshe idonta tana jin sautin yadda zuciyarta ke bugawa da sauri sauri kamar zata tsaga ƙirjinta ta fito.
Bulama ya durƙuso gabanta yace "ki kwantar da hanlinki kinji daughter, babu wata matsala Daddynki yana nan lafiya, zezo inda kike, amma sekin kwantar da hankalinki, kin san baki da cikakkiyar lafiya, mubi komai a sannu"
Idonta a lumshe bata buɗe ba tace "Daddy"
Yace "Na'am daughter"
"kasa a sakarmin Yusuf"
"saboda me? Meyasa zakice a sake shi, mutumin da yayi garkuwa dake, aka samoki da ƙyar a wani ƙungurmin ƙauye, sannan kice a sake shi, baki duba abunda yayi miki bane?"
"Yoseef beyi