Showing 69001 words to 72000 words out of 209297 words
Allah kabari Yoseef, ni yanzu na fara mantawa da wasu abubuwan saboda sadaukarwarka a gareni, baka yi sallar isha'i bama, gashi yauma munyi dare, kayi salla kaci Abincinka seka kwanta "
Bece mata komai ba ya miƙe, sosai yake jin tausayin Widad, gaba ɗaya labarin nan ya tsaye masa a ransa, Widad ta koma kan shimfiɗarta, sannan ta fara zubda nata hawayen dan bata son ta sake ɗaga masa hankali, tana kallonsa sau biyu yana sake sallame salla, yayi ya idar nan ma ya daɗe sosai akan sallayar sannan ya tashi, be ko kula Abincin ba, shimfiɗar ma beyi ba a ƙasa yaje ya kwanta a rigingine.
Nanfa Ƙwaƙwalwarsa ta shiga kaiwa tana komowa akan abubuwa da dama, da irin binciken da yayi, lokaci lokaci idan ya tuna labarin Widad se yaja tsaki, dan ya rasa a inda yakamata ya ajiye wannan tsagwaron zalunci haka.
Ƙarshe ma tashi yayi zaune ya sake dafe kansa, sedai Duk abun nan Widad tana kallonsa, tana tunanin yanzu akwai wanda zeji labarin abunda ya sameta ya tausaya mata haka, harya shiga wannan irin damuwar? Dukda tarin wulaƙanci da isa data dinga nuna masa, amma ya dake ya shanye har yake jin tausayinta haka, bayan ɗawainiyar da yayi da ita, da ƙoƙarin kareta daya dingayi, lokacin da akazo sace ta ba dashi sukayi niyyar ɗauka ba, ya dage ba zasu tafi da ita ba, shine suka haɗa dashi, ga wahala da azaba da ya sha gurin kuɓutarsu, gashi har yanzu a kan shan wahala yake, a rayuwar da tayi idan akace mata akwai mutum me irin zuciyar Yusuf a zamanin nan to tabbas za tace ƙaryane, ita kam me zata yiwa Yoseef, ta saka masa tasan ko duk abunda ta mallaka zata bashi bata isa ta biya shi ba.
A hankali ta tashi ta tafi inda yake zaune ya rafka tagumi, ta janye hannun tace "wai bazaka kwanta bane? Kuma ina shimfiɗar kake zaune a ƙasa haka?"
"Bana jin bacci" ya bata amsa
"ko Abinci ma fa baka ciba, ga yunwa ga rashin bacci? Gaskiya ban yadda ba"
Yusuf yace "kije ki kwanta kawai, ni bana jin bacci"
Tace "Shikenan nima bana ji, bari mu zauna kawai"
"A'a, kije ki kwanta kinji nasan zaki bacci idan kika kwanta"
Tace "shikenan, kwanta se in kwanta a jikinka"
Yusuf yace "No jikinki ze ciwo, ki kwanta akan katifarki"
Tai murmushin ƙarfin hali tace "baka san jikinka yafi katifar nan daɗin bacci ba, kwanta se in kwanta"
Haka Yusuf ya kwanta, ita kuma ta kwanta a jikinsa, tasa hannu ta zare ribbon ɗin kanta, ta kamo hannunsa ta ɗora a kan gashin ta, a hankali ya rungumeta da hannu ɗaya, yasa hannu ɗaya yana wasa da gashin nata.
Tana jin yadda zuciyarsa ke lugude da ƙarfin gaske, ya zamana ma taji kamar baya numfashi daidai, dukda a duhu ne amma Widad ta gane har yanzu Yusuf kuka yake, yana da matuƙar dauriya da juriya, amma wannan karon ya kasa jurewar, saboda jin Widad yake tamkar wani sashine na tsoka a zuciyarsa, haka kurum yake jin kamar shi akayiwa laifin ma ba ita ba.
Ƙanƙame Yusuf tayi ta fashe da kuka, Cikin jan numfashi Yusuf yace "Widad lafiya, kukan me kike kuma?"
"Dan Allah Yoseef kamanta da labarin nan da na gaya maka, karkasa shi a ranka dan Allah, kar wani abu ya same ka ji yadda kake numfashi fa"
Sosai ya sake rungumeta yace "Never mind dear, ba abunda ze sameni insha Allah, ina tunanin meye mafita ne kawai, a shirye nake da in baki gudunmuwa kota wani ɓangare dan tina Asirin wanda suke aikata muku wannan zalunci haka, amma kafin nan nasan koba duka ba kin san wasu daga cikin mutanen nan, meyasa kika ƙyalesu baki tona musu Asiri ba? "
" Yossef yadda nake shiri akansu haka suke yi a kaina, sun fini iya mugunta da zalunci, na haskawa mahaifina wasu daga cikin su, hakan yasa ya yanke hulɗar kasuwanci da wasunsu, sannan wace hujja nake dashi daze tabattar da abunda nake zarginsu? Bani da sheda se Allah"
Cikin raɗa Yusuf yaje dai dai kunnenta yace "meyasa kika ƙyale Bulama, bayan ko a binciken da nake, ina sanya babbar alamar tambaya a gareshi, dan sam ban yadda da shiba, amma naga kina masa kallon uba, kuma ni shine babban suspect ɗina"
Widad tace "saboda ko yana ciki ni ba ta tashi nake ba"
"Meyasa?" Yusuf ya tambaye ta.
"Saboda bashi nake hari ba, Bukar nake hari, na barwa zuciyata insha Allah koni ko shi, ko kuma muyi mutuwar kasko dashi, Insha Allah se Bukar yaje ƙiyama da tabon da zan masa, ya azabtar da rayuwata, yaso kassarani da mahaifina yamin zalunci mafi muni, wannan abunda akayi mana nasan da sa hannunsa, da Bukar da Baban Nurat sesun wulaƙanta a rayuwa, sun cutar dani Yoseef " tai maganar tana fashewa da kuka, rarrashinta ya dingayi sannan yace
"Waye kuma Bukar? Banji kin faɗe shi a labarin da kika bani ba"
Ta gyara kwanciyarta sannan tace "Bukar! Bukar! Alhaji Bukar! Tabbas ban faɗeshi a labarin da na baka ba, saboda labarin ma wani sashe na baka, na ɓoye maka wani, na kuma canza inda faɗa maka bashi da amfani, saboda jin wani sashin na labarina a gareka tamkar tarwatsa shirin sa nake ne, amma ina fatan ubangiji, Allah ya maida mu gida lafiya, zan baka sauran ɓangaren dana cire maka a labarin, dan se mun koma gida jin ɓangaren zeyi amfani, har in cika dukkan burikana, sannan a lokacin zan baka labarin waye Bukar "
Yusuf yace " Shikenan, ubangiji Allah ya kawo lokacin da zamu koma, Insha Allah se inda ƙarfina ya ƙare Widad, zan baki goyon baya ɗari bisa ɗari mu shiga kowane irin ƙalubale dan cikar burinki"
"Thank you Yoseef, Allah ya jiƙan magabatanka, nagode sosai"
Tai maganar tana Ƙanƙame shi sosai.
Haka suka kwana a ƙasa shida ita, a gurin nan ga sanyi cikin dare amma basu iya tashi daga gurin ba, saboda damuwar da zukatansu suke ciki.
Umman Yusuf se fama take da hawan jini saboda damuwa da tunani, ga rashin cin Abinci da bata iya ci balle bacci, gaba ɗaya ta rame tayi wani iri saboda tunanin halin da ɗanta Yusuf ke ciki, ga kuma wannan labari daya cika gari, ita dai tasan ɗanta ba mutumin banza bane, dan tasan tabbas wannan zance ƙaryace akayi masa.
Tana nan kwance bayan la'asar a inda tayi salla, tana jan carbi tana ta kai kukanta ga Allah akan Allah ya kuɓutar mata da ɗanta, yasa yana cikin ƙoshin lafiya.
Sallama Suleiman yayi, taja jiki da ƙyar ta tashi zaune da ƙyar ta amsa masa, ya tsorata ganin halin da take ciki, a ɗan firgice Suleiman yace "Umma meyasameki haka?"
Take ta fashe da kuka tace "baka ga Sanarwar da akayi a kafafen yaɗa labarai bane? Wai Yusufana ake nema ido rufe wai ya sace 'ya, haɗuwar Ɗana da wannan alhali ba alheri bane, tunda ya fara aiki da yarinyar nan walwalarsa ta ragu kullum cikin tunani yake, kullum cikin damuwa yake banda sintirin fita da wuri baze dawo ba se dare amma ƙarshe abunda za'a sakamana da shi kenan, bakomai akwai Allah, Allah ya bimana haƙƙinmu"
Suleiman yace "Umma kiyi haƙuri, yanzun ma abunda ya kawoni kenan, amma yanzu zan fara kaiki Asibiti tukuna, a duba ki kamar baki da lafiya"
Umman Yusuf tace "Ni ba inda zani, lafiya ta ƙalau ɗana nake tunani kawai, shiyasa ake ganin kamar bani da lafiya"
Da ƙyar Suleiman ya lallaɓata ta yadda ya kaita Asibiti, sukaje akayi mata gwaje gwaje, akace hawan jinine ga ulcer, aka rubuta mata magunguna sannan ya ɗauketa zuwa gida.
Suna tafe tana share hawaye, bayan ya kaita gida yace "Umma ki kula da magungunanki, kidinga shansu akan lokaci, sannan shi lamari irin wannan Addu'ar ku muke nema, idan harda Addu'ar ku, babu wani abu daze same mu insha Allah, Yusuf Addu'ar ki yake nema kiyi haƙuri, komai ze daidaita insha Allah"
"Amma Suleiman, kana ganin yau watanni huɗu kenan, ban saka Yusuf a idona ba, baya nan ban san idan yake ba katsam kuma inga wannan al'amari haka, kuma naji labarin Abokinsa Abbas yazo, amma ko jaje bezo yamin ba"
Suleiman yace "ki kwantar hankalinki Umma, Abbas baze dawo miki da Yusuf ba, ki manta dashi, Insha Allah muna nan muna ƙoƙari akai, sannan insha Allah zan kawo miki kayan Abinci dana buƙata, amma kisa haƙuri a ranki"
Umma tace "shikenan, nagode sosai Allah yasaka da alkhairi, Allah yayi maka albarka ya raba ka da duniya lafiya"
Suleiman yace "Ameen" sannan ya tafi.
Aka cigaba da yamaɗiɗi da zancen Yusuf, akan ya sace Widad ya gudu da ita, fastocinsa suka cigaba da yawo, dayake in Allah yasa kana zaman lafiya da kowa, baka rasa masoya, wanda suka san Yusuf suka san halinsa suka dinga ƙaryatawa, suna taya shi da Addu'a.
Ramlah na kwance akan gadon ɗakin Hotel, Fahad yana tsaye yana taje kansa a gaban mudubi, Ramlah tace "Fahad, lokaci fa yana ƙurewa, zuwa yanzu yakamata ace an fara maganar aurenmu, amma naga kamar baka damu ba ko zancem baka yi"
Fahad cikin salonsa na yaudara yace "Beb kin fiye garaje fa, mubi komai a hankali mana, nida nake so ayi classic wedding, so nake bikinmu ya zama the expensive wedding of the year, wasu kuɗi nake jira a hannun Dad, shiyasa amma kiyi haƙuri, soon za'ayi komai insha Allah"
Ta ɗan kwaɓe baki tace "Allah yasa, danni ina ma tantama akanka, kar inje Widad ta dawo kaƙi Aurena kace se ita, dan haka kayi min wancan karon"
"No karki damu, ai abunda yaaa nace zan Aureta, saboda in karɓo mana kuɗaɗen hannunta ne, in rabata da komai im azabtar da ita, sannan in sake ta, that's my plan, but unfortunately it's fails, ni yanzu wannan jakin daya gudu da ita, Allah yasa karya karɓe abun ya barmu "
Ramlah tace 'kamar kuwa ka sani, dan wallahi zata iya bashi, can you imagine ATM ɗinta yayi over 1 week a gurinsa, naje masa mu haɗa kai a samu wani abu amma fafur yaƙi, munafuki se gashi yayi awon gaba da ita"
Fahad yace "suje su ƙarata, ai tunda ba' a san inda Dad ɗinta yake ba, zan cigaba da kawo masu siyan kadarorim nan, a rage wani abun"
Ramlah tace "hakane kam, nidai so nake ayi muyi Auren nan, kaga sau biyu ina abortion fa"
"Ai kece, nace miki kije kiyi planning, amma kinƙi"
"Aini kasan abun planning ɗin nan, suna da nasu matsalolin, ɗan bani tablet biyu in saka a coc, i want doze up"
Ya miƙo mata magani, ta zuba a lemo ta girgiza tasha, sannan ta kwanta bacci.
Ya kalleta a ransa yace "baki da hankali, uban waye ze Aureki ashe ma bani da hankali, zanta lallaɓaki ina morewa, gefe guda kuma in cigaba da damfararku"
Yauma Yusuf se a ɗaki sukayi salla, dan bacci be ɗauke shi ba, se daf da Asuba.
Bayan sunyi salla, suka koma suka kwanta bacci, sedai shi Yusuf baccin ya gagareshi sam, a cikin tunanin ma ya raaa wanne zeyi, se kusa ƙarfe goma sannan ya kwantar da Widad ya tashi ya shiga gyaran ɗaki, ya shaee ɗakin ya haɗo kwanukan wanke wanke ya fito tsakar gida.
Da Hanne yayi karo tana shara, tana ganinsa ta zuba masa ido tana murmushi, Yusuf yace mata "Ina kwana"
Cikin yashe baki tace "ina kwana"
Yusuf yace "lafiya ƙalau kina lafiya"
"Lafiya ƙalau, kawo in wanke maka kwanukan"
Yusuf yace "A'a, yi shararki kawai"
"bakomai kiyi aikinki kawai"
"A'a dan Allah ka kawao"
Tasa hannu ta karɓa, Yusuf ya koma ɗaki ya dafawa Widad ruwan wanka, sannan yaje ze tasheta.
Zama yayi ya zuba mata ido, yana jin ƙaunarta da wani irin tausayinta yana ratsa ko ina na jikinsa
Numfashin da yake mata a fuskane yasa ta buɗe ido tana kallonsa, har yanzu idon Yusuf ja, ga alamun damuwa nan ƙarara a fuskarsa.
Yusuf yace "tashi ga ruwan wanka nan, kiyi wanka ki karya"
Miƙa tayi tana ɗan lumshe ido, Yusuf se binta da kallo yake.
"To ka matsa in tashi mana, ka danne ni kuma kana ina tashi"
"Widad bana gajiya da kallon ki, nidai ina sonki Widad"
Ajiyar zuciya tayi, ta shafi sajensa a hankali tace "naji ɗagani in cire kaya inje inyi wanka"
Maimakon ya ɗaga ta seya sake gyara kwanciya a jikinta, yana kuma nanata mata "ina sonki Matata, ina sonki Widad"
Gaba ɗaya taji wata kasala na saukar mata, batayi magana ba sedai tasa hannu ta rungumeshi itama.
Hanne cw ta bankaɗo ɗakin sannan zata yi sallama.....
LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
IDAN KUMA KIN SIYA AMANACE KARKI FITARMIN DAN ALLAH 🙏🙏🙏
11/14/21, 6:09 PM - Ummee Musa: LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
IDAN KUMA KIN SIYA AMANACE KARKI FITARMIN DAN ALLAH 🙏🙏🙏
84_85
Yusuf ya ɗago da sauri, yayin da jikin Hanne ya ɗau rawa, ba tare da tace uffan ba ta ajiye kwanukan da ta wanke, jikinta na rawa ta fice waje, yayin da wani abu kamar dutse yazo ya daskare mata a ƙirjinta, tana tafe amma kamar ta kifa, danko gabanta bata gani, maimakon taji haushin Yusuf, se wani tuƙuƙin tsanar Widad da taji a ranta, kamar ta janyo ta ta shaƙe haka take ji.
Widad kuwa tsaki tayi, ta haɗe rai tace "kaga malam ɗagani mana"
Yusuf yace "to nikuma meye laifina da zaki wani haɗemin rai haka?"
Ta ƙara haɗe rai tace "kaika sani dan Allah nika ɗagani, ina da abunyi fa"
Yai ƙasa da murya yace "My queen..
Ta katse shi ta hanyar cewa" dan Allah malam ka ɗagani nace, bana son jin komai daga bakinka, kuma karka ƙara bawa wata 'yar ƙauye kwanukana ta wanke min na gaya maka, in bahaka ba nika ajiyemin abuna zan wanke, idan kuwa ta sake wanken kwanuka na, wallahi sena zuba su gaba ɗaya a wannan rijiyar ta gidan nan, kuma idan na kuma ganinta a ɗakina duk abunda nayi mata ita ta janyowa kanta na gaya maka "
Yusuf ya ƙura mata ido, yana kallon yadda take masifa fuskarta na bayyanar da matsanancin kishin dake zuciyarta, amma yanzu daze ce tana sonshi seta fara masa iyayi, tana ita bata san so ba, kawai dai danya temake ta ne.
Ta ture shi daga jikinta, ta miƙe tana kumbure kumbure ta cire kayanta ta tafi wanka.
Bayan fitarta ya miƙe, ya gyara mata shimfiɗarta, Gwaggo ta aiko musu da Abun karin kumallo.
Koda Widad ta fita tsakar gida, tana kallon mugun Kallon da Hanne ke mata, banda Widad na ganin darajar Gwaggo, da ba abunda ze hana tayiwa Hanne rashin mutunci me wuyar mantawa, amma ta ƙyaleta taje tayi wankanta.
Data dawo ɗakima Yusuf yana ta ƙoƙarin rarrashinta, amma ta basar dashi taƙi kula shi, ta barshi yaita ɓaɓatunsa shikaɗai, ta ɗakko kaya zata saka yazo ya karɓi kayan daga hannunta, amma tasa hannu fizge abunta, sosai kishi me zafi ya bayyana a fuskarta, Yusuf yace bari yayi amfani da wannan damar gurin jarraba Widad, bari yaga idan dagaske kishinsa take ko kuwa?.
Ya koma gefe ya zuba mata ido, tasa kayanta, ta koma gefe tana shafa mai tai kicin kicin da fuskarta, kamar ba itace suke tare ɗazu ba cikin farin ciki.
Yusuf yace "Allah sarki rayuwa, Ohh koya Amal ɗina tayi da taji an sace mata ni, Amal ta gama matowa a sona, she really loves me, ga Nurat ma light, ga fara'a ga kirki she also loves me, itama ban san ya zataji ba, ga Sakina abokiyar aikina, abunda ya hana in bawa Sakina fuska shine shigar matsatsun kaya, da yawan kule kulen maza, se gashi Allah yasa na Auri me sa matsatsun kayan, ga tsiwa gashi sam bata sona, taita bani wahala, gashi ina matuƙar sonta, kissing ɗinta in nayi ta dingamin faɗa kenan tanamin tsiwa, laifi koni nayi ko bani nayi ba taita fushi dani, bata tausayina sam, nikaɗai nake sonta, Nasan da Nurat na Aura dana huta, zan sha soyayya dan akwaita da tausayi da sanyin hali, sannan masha Allah, gata da lips masu kyau, nasan ita ba zata dinga ƙyamata ba, ko kissing ɗinta na....
Aibe ƙarasa ba yaji saukar ludayin roba a ƙeyarsa, seda ya razana ya kalli inda Widad take, kawai ta fashe da kuka harda hawaye.
Yusuf yace "Ke lafiya Mena yi miki kuma? Kinƙi kulani nazo ina hirata kuma seki jefe ni, sekin jimin rauni tukuna, mu koma gida 'yan matan nawa duk su gujeni?ko kuma su kasa ganeni?"
Aikuwa ta ƙara sautin kukan nata sosai, harda sheshsehseƙa, wani guntun murmushi yayi a ransa yace' yarinya kin faller '
Amma a zahiri seya miƙe, yazo inda take yace " Widad, meyasa ki kuka ne? Kowani abun nayi miki ne?"
Cikin shagwaɓa Tace" Nima ban sani ba"
Yusuf yace "to meyasa kika jefeni da ludayi? Baki san naji zafi ba?"
"Ni bana son zancen da kake ne, raina ɓaci yake ni karka ƙaramin zancen wata a gabana, bana so am feeling bad, ni gaba ɗaya ma zuciyata haushi nake ji"
Yusuf ji yayi kamar ya ƙyalƙyale da dariya, amma yasan yana yin hakan, sabuwar rigima zata saka masa, dan haka yace
"Ohhh shikenan ya isa haka, am very sorry bazan sake ba, dena kukan kinji abar sona, na dena insha Allah dena kukan haka kinji gimbiyar"
Ya dinga share mata hawayen da yake ta binta fuskarta.
Widad ta ture hannusa cikin zumɓira baki tace "ni rabu dani, tunda ka sani kuka"
"Yi haƙuri I don't mean to hurt you Baby, ban zaci ranki ze ɓaci ba, kinga se binki nake ina magana amma kika shareni, se da ki kaji nafara lissafin 'yan matama sannan kika hau kuka"
Widad tace "to waima meyasa nayi kuka ne?"
Yusuf yace "Oho nima ban sani ba, aike zan tambaya" Yusuf ya bata amsa