Showing 90001 words to 93000 words out of 209297 words
duk a bushe muke, saboda wannan iblishiyar matar, kana gani yanzu duk tarin jama'ar dake zuwa gidan nan yanzu babu kowa saboda baƙin halinta, wannan da a aljanu tazo ba shakka se ace itace babar sheɗan"
Nura yai dariya kamar cikinsa zs ciwo, ganin yadda Murtalah ya harzuƙa sosai se bala'i yake yana zage zage da rashin mutunci da gani kasan an kai shi maƙurar bangone.
Nura yace "malam kar dai kayi saɓo, a gidan ubanwa ka taɓa jin ance sheɗam yana da uwa, hattara dai"
"Bari Nura rainane ya ɓaci wallahi, Allah yasaka mana wallahi, Allah ya nuna mana ranar da dubunta zata cika a tarkatata a koreta da wannan iblisan 'ya' yan nata"
Nura yace "Ameen dai, manyan iblisai makuwa, dan wannan babbar me soyayyen ido shaye2 take yanzu, saura ƙiris shekaranjiya tabi ta kan ƙafar Isa da tayoyin mota, Allah ya temake shi yai saurin matsawa kuma ta fito daga motar, ta zage iyayi da kakaninsa tsaf sannan tabar gurin nan tana maye "
Murtalah yace " haka zasu ƙare, saura kuma hauka da tamɓele, tunda haƙƙin mutane suka san susa a gaba suci babu imani babu tausayi "
Hajiya Halima kuwa tana buɗe takaddar, taci karo da rubutun Anwar kamar haka
" *_Asslam Alaikum warahmatullah zuwa ga mahaifiyata, nasan lokacin da zaki riski saƙona nayi nisa da gida, nisam da bana tunanin zan iya waiwayar gida a kwanan nan, na bar gidane saboda faɗar ma'aiki salallahu alaihi wassalam, babu biyayya ga abun halitta gurin saɓawa Mahalicci, dan haka bazan iya jure cigaba da zama daku ba ana aiakta abunda be kamata ba, nasan idan nayi Yunƙurin yi miki nasiha ba zaki saurareni ba, kin zaɓi lalacewar 'yarki saboda tana miki hanya gurin tara dukiyar Haram, kin fifita akanmu wanda kema kin san hakan ba dai dai bane, kuma kina ɗauki ɗai ɗai ga kayan mutumin daya yayi sanadiyar fitarmu daga masifar talauci zuwa arziki, kin haɗa kai da maƙiyansa ana cutar dashi, nayi dana sani nayi kuka da bincike na ya tabattar min da dake aka haɗa baki komai yake gudana tsakaninsa da maƙiyansa, kaicon wannan butulci naki Mummy, ni bazan iya cigaba da zama daku ba dan haka na bar muku gidan, dama bana ubana bane ba, ina miki fatan Alkhairi dake da ƙannena a duk inda kuke, Allah ya sadamu da alkhairi, ɗanki me ƙaunarki har kullum ANWAR *_
Jikintane ya hau tsuma tana rarraba ido, yayin da wani irin gumi from no where ya shiga tsatsafo mata, ta dinga rarraba ido kamar shege a rabon gado.
Ramlah tace "Mummy lafiya kuwa, wetin inside that later?"
Miƙo mata tayi, domin idinta ya gane mata, Ramlah ta karɓa ta shiga karantowa a fili, tana zuwa ƙarshe ta yarda takaddar tace "shikenan munshiga uku Mummy, wallahi tonon asirinmu yazo, dan abune me sauƙi a gurin Anwar ya tona mana Asiri, kin san halinsa Mummy, yau munshiga uku, wayyo wallahi har cikina ya fara ciwo"
Amal tace "wannan shi ake kira tashin hankali wanda ba'a samasa rana, ina muka kama tunda wannan me iƙrarin ustazancin ya san abunda ake ciki"
Hajiya Halima ta goge fuskarta tace "ni tunanina a gidan ubanwa yasan wannan maganar? Waye ya gaya masa? Tsawon shekaru goma sha ɗaya ana abun nan a sirrance cikin rufin Asiri, waye ya tina min wannan Asirin haka ni Halima?"
Ramlah tace "Mummy ba wannan tunanin ya kamata kiyi ba, tunanin meye mafita yakamata ayai, tunda sanin inda ya samu labarin bashi da amfani"
Hajiya Halima tace "toni ta ina zan fara ne? Ta ina yakamata infara neman mafitar? Na farko ban san inda ya tafi ba, kuma tabbas abune mawuyaci ya iya ɓoye abun nan yakasa gayawa wani, ke ni gaba ɗaya na rasa abunyi wallahi, kuma ɗazun nan naje mukayi kaca kaca dasu Alhaji Munir, da Alhaji Musa na zata su suka sace shi, ni wallahi da iya tafiyar yayi da sauƙi, amma sanin wannan abubuwan yafi komai masifar ɗagamin hankali, kar Anwar ya tona min Asiri in lalace a bakin duniya"
Ramlah tace "aida iya lalacewa a bakin duniya ne da sauƙi Mummy, idan Asiri ya tonufa se komai ya watse ya lalace manya manya abubuwa ne zasu tonu, wanda baki isa kici bulus ba"
Cikin tashin hankali Hajiya Halima tace "Au nikaɗai ma banda ku?"
Ramlah tace "Mummy koda mu koba mu, ai laifinki yafi namu yawa, duk abunda mukayi kece kika samu a hanya, yanzu mafita ɗaya ce, kije ki samu su su Alhaji Harunan, ku sake sasantawa dama kun saba faɗa ku shirya ai, kuje ku sasanta kunemi mafita, dan wallahi Asirin ki ya tonu nasu ya tonu dan se mun faɗi komai "
" Kai Amma wannan yaro akwai shege me baƙin hali, kamar duk fafatukar nan ba danku nakeyi ba? "
Amal tace " Mummy amma kin san halinsa, dama da kuɗin nan sun samu ban san yadda za'ayi dashi ba, dan kema kanki kin san baze cisu ba"
Halima ta zauna kawai murza goshi take yi, saboda tashin hankali da damuwa.
Widad fafur taƙi Yusuf, zaman ɗakinma ta ƙiyi, ya dafa Abinci da safe amma taƙici, ƙarshe ma ta koma ɗakin Gwaggo, ta hau gadon Gwaggo tayi kwanciyar ta, Yusuf ya rasa ta ina ze fara yiwa Widad bayani, ta ina ze fara nuna mata yana mata son da baze taɓa juya mata baya akan wani abu da takeso ba muddin be saɓawa ubangiji ba? Yana da dalilinsa me ƙarfi ya zeyi tagane gaba ɗaya ta fututtuke taƙi saurarensa.
Haka ya shirya ya fita, se bayan ya fita ta koma ɗakin ta gyara, ta barmasa Abincinsa taƙi ci, da yamma ɗalibai suka shigo karatu gurinta, sukayi karatunsu har kusan magariba sannan ta sallamesu.
Gwaggo ta fuskanci kamar sun kuma samun saɓani tsakanin ta da Yusuf, amma bata son taita mata shisshigi, dan haka ta ƙyaleta, dan gaba ɗaya walwalarta ta ragu, kusan ko san magana ma ba tayi, ko kayi maganar ma bata san abunda kake faɗa ba tana tunani.
Dan mamaki yakasa barin zuciyarta wai Yusuf ne yake gudun ta haihu dashi, ita iya tunaninta babu wani dalili daze sa yayi hakan sedai son zuciyarsa kawai.
Da daddare ya dawo tana kallonsa, bata kulashi ba dan ko sallamarsa ƙin Amsawa tayi, ta barmasa ɗakin gaba ɗaya ta koma tsakar gida inda aka baje tabarma ana hira.
Haka ya fito kamar maraya, yayi alwala ya tafi salla, ya dawo shiru shiru taƙi komawa ɗakin, har kusan ƙarfe goma na dare, ya fito yazo inda take dayake duk hirar nan ma da ake yi, ita ba wani magana take ba, sedai in anyi abun dariya ta ɗanyi murmushi, sam hankalinta baya kan hirar ta fitone kawai dan karma Yusuf yayi mata magana.
Tana jikin bango, babu haske a inda take zaune, yazo ya zauna a kusa da ita yayi ƙasa da muryarsa yace "My love, dan Allah kizo muje ɗaki mana, kin barni kamar maraya kin dawo nan kin zauna, dan Allah kiyi haƙuri kizo mu koma mana, kina da miji amma kizo zaman hira"
"Yoseef bana son sake jin kalamn nan naka na yaudara, wanda naji a bayama sun isa Allah ya amfana, kaje da can ai ba tare muke hirar ba"
"Widad kalaman nawane na yaudara?"
"bakaji bane in sake maimaitawa, kalaman yaudara da kake yaudara ta dasu na fara amince maka zaka butulcemin mana"
"Yi haƙuri dan Allah karki ɗaga murya mana, zomu je ɗaki muyi magana"
Widad tace "bazani ba, nace bazanje ba, ka ƙyaleni"
Yusuf ya sake marairaicewa yace "nasan haushina kikeji, a ƙule kike dani amma please and please am very sorry, kiyi haƙuri mu koma ɗaki"
Ƙarshe ma juya masa baya tayi, alamar idan ya gama ze iya tashi yayi gaba.
Abun duniya ya ishi Yusuf, haka ya tashi ya tafi ɗaki, jiki a sanyaye, ya dinga tunanin dama tun farko data fara zancen cikin, ba haka ya ɓullo mata ba, gashi ta birkice gaba ɗaya, tama ƙi saurararsa.
SE kusan sha ɗaya da rabi, dabar hirara nan ta watse, kowa ya tashi ya tafi makwancinsa, Widad ma ɗakinsu ta nufa, sedai tana zuwa ta tarar da Yusuf a zaune be kwanta ba.
Tazo ta tsallake shi ta shige abunta, tana ƙoƙarin canza kaya, Yusuf yace "Widad, akwai buƙatar ko sau ɗaya ki bani dama, in kare kaina yana da kyau kiji ta bakina kafin yanke hukunci"
"baka da ta cewa fa, ai labarin zuciya a tambayi fuska babu wani abu da zaka gayamin, fuskarka ta bayyana abunda ke cikin zuciyar ka, dan haka ka ƙyaleni kawai, bana san sake jin komai kawai ka rabu dani, kuma ɗane idan Allah ya bani kace ba naka bans, ni ima so kuma bana buƙatar taimakonka a rainon ɗana, da can baka san cikin ze shiga ba kake mu'amala dani, ko in an tashi bani ciki shawara za'ayi da kai? "
" Nace dai kiyi haƙuri please, zan gayamiki dalilina dan Allah, amma kiyi haƙuri ki dena wannan fushin"
"Se kuma kayi, kanka ake ji"
"Widad, Widad magana fa nake miki"
"kaga idan ka takurani wallahi zan fita ina kwana a waje, ka ƙyaleni"
Ya dinga binta da kallo harta kwanta abunta taja bargo ta rufe kanta.
Amal ce zaune tayi tagumi jugum, kamar an musu mutuwa tace "Mummy, yanzu idan kinje gurinsu Alhaji Haruna me zaki ce musu? Kuma ta ina za'a fara binciken inda ya tafi?"
Hajiya Halima tace " sanin gaibu se Allah Amal, zanje dai inga yadda zamuyi dasu ne kawai"
Ramlah tace "to yanzu idan aka ganshi Meza kiyi masa?"
Hajiya Halima tace "ubansa zanci da farko, sannan ince masa duk abunda aka gayamasa ƙaryane"
"Mummy, Yaya Anwar fa isa almost 30 years, he is not kid, tayaya zaki gayamasa haka ya yadda, idan kuma ba gaya masa akayi ba wani abu ya gani fa?"
"Waike Amal bakinki baya faɗar alheri se sharrine, to rufen baki tunda bazaki faɗi abun alkhairi ba"
Ramlah tace "bahaka bane Mummy, yanzu idan kika je neman mafita gurinsu Alhaji Haruna, kina ganin suna ganin Asirinsu ze tonu idan suka ganshi zasu ƙyaleshi hakane? Karfa ki manta har yanzu babu wanda yake sa tabbas na Bala yana raye a kurkuku, saboda sun tsoron Asirinsu ya tonu ana cewa sunsa an kashe shi, kuma sun cigaba da aiki da Saleb, ba tare da yasan sun kashe ɗan uwansa ba, those people are evil, they are very dangerous fa"
"Na shiga uku ni Halima, yanzu ya zanyi wallahi duk cikinku ina sonku, babu wanda zan iya zuba ido inga ya cutu in haƙura, duk ni na haifeku ina ƙaunar ku"
Amal tace "mun sani Mummy, kiyi haƙuri ki kwantar da hankalinki a nemo mafita mana"
Isa megadi na zaune a bakin gate, riƙe da 'yar radionsa, yana ta fama ya kama stationsa amma se wani ɓurari take saboda rashin batur, ya dire radion yana zage zage da Tsinewa Hajiya Halima, ganin kuɗin batirin radio ma ya ga gareshi.
Jiya yi ana bugun gate ɗin da ƙarfi kamar za' a karya ƙofar, shi dai beji horn ɗin mota ba, dan baka ya miƙe a fusace yana bala'i yana masife yana cewa "wani jakin me wannan yake mana wannan bugun se kace gidan ubansa, kokuma wani ɗan fashi, mutum se kace gidan uabansa, ko yaya kuka buga anaji, muma za'a buɗe amma komai se mutane sun yi hauka, aikin banza iyayen maula kawai"
Haka ya ci gaba da surfa masifa, sannan ya buɗe gate ɗin, wani mutum ya gani a tsaye, da wani koɗaɗɗen yadinsa shara shara, hularsa ma tayi baƙi ƙirin saboda dauɗa wani zaburarre dashi kamar korarre, Isa ya ƙare masa kallo yace "mutane ba dai Jaraba ba, baka san an sace me gidan ba, dama shine yake baku, wannan mastiyaciyar me hannun jarirar ba'a ɓanɓararta jeka Allah ya baka haƙuri, an dema sadaka a gidan nan"
Mutumin yace "ba Sadaka nazo nema ba, gurin Halima nazo"
"au gatsal kake faɗar sunantaa? Allah yasa ta jika, tukuna ma a danginta ban taɓa ganin mutum kamarka yazo ba, daga ina ko kwatance akayi maka?"
"ba kwatance akayimin ba, kaje kace mata tayi baƙo, ita tasan waye"
Isa yace "shikenan, shigo daga ciki seka zauna akan benci, amma in turoka akayi a baka aikima, babu guri dan muma ba biyanmu take ba, mace ce hannu kamar kuturwa, tasan a bata amma bata san ta bayar ba"
Haka Isa ya cigaba da soki burutsunsa, yaje ya sanar da Hajiya Halima zuwan baƙon nan, amma ƙarshe seda ya fito da baƙin ciki da dana sanin zuwa sanar da saƙon nan.
Har kusan awa guda bata fito ba, Muratalah ne yaji tausayinsa ya bashi ruwa, dan da gani muyumin ya jigata kafin yazo, ita shaf tama manta da wani baƙo da akace tayi, ta shiryo tsaf abunta zata fita, har an ɗakko mata mota, Nura yace "Hajiya baƙonki fa"
A fusace ta juya zata yi masifa "wai wane jarababbem ne haka aka dameni dashi"
Muyumin yace "nine nan"
Tana waiwayawa ta zare ido ta dafe ƙirji tace "Na shiga uku, Shu'aibu!!!"
Abun duniya ya dami Yusuf, baccinma ya gagar ɗaukarsa, jin shiri yasa ya zata ko Widad tayi bacci, kwana biyu kenan basu kwanta manne da juna ba, duk yaji babu daɗi, a hankali ya lalaɓa yaje bayanta ya kwanta ya shiga bargon nata, ya rungumeta a jikinsa.
"Malam meye hakane? Ka lallaɓone kazo ka samu abunda kake so in anjima nace Allah ya bani ciki ka haɗe rai"?
Yusuf ya girgiza mata kai yace "Aa', ɗumin jikinki nake son ji, dan Allah kimin afuwa Widad, ki saurareni please"
"Dan Allah nima ka ƙyaleni, wallahi bana son jin komai daga bakinka, lallaɓani zakayi in yarda da kai, in anjima kuma ka juyan baga"
"babu juya baya tsakanina dakw Widad, ina son ki fahimceni ne kawai, bari in baki labarin wani yaro"
Miƙewa take ƙoƙarin yi, tace "bana son ji, ka riƙe abunka"
"Dan Allah ki tsaya kiji, yana da mahimmanci sannan akwai darasin rayuwa a ciki"
Ganin bata da niyyar saurararsa yasa ya janyota jikinsa, ya rungumeta gam sosai yana ajiyar zuciya, a hankali taji ɓacin ran nata na raguwa, dan haka ta kwanta tayi shiru tana sauraren bugun zuciyarsa.
Yusuf ya nisa sannan yace "Labarin yaron nan zaki ji daɗinsa sosai, bari in gayamiki abunda ya samu yaron.....
Mun kusa ƙarƙare part 2, idan part 2 kawai kika siya karki sake ayi 3 babu ke.
LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
IDAN KUMA KIN SIYA AMANACE KARKI FITARMIN DAN ALLAH 🙏🙏🙏
11/15/21, 4:53 PM - Buhainat: LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
IDAN KUMA KIN SIYA AMANACE KARKI FITARMIN DAN ALLAH 🙏🙏🙏
98_99
"Akwai wani Mutum me suna Bashir, shida matarsa me suna Jidda, wadda sukayi Auren soyayya, kusan shekara uku babu haihuwa, kin san yanayin ƙasar Hausa, abun ya kan zama abun damuwa koma gori ga matar da bata haihuwa.
Aka dinga ziga mutumin nan akan yaƙara Aure tunda bata haihuwa amma yaƙi, gashi babban ɗan Sanda yana matuƙar son matar nan tasa, yana da rufin Asirinsa dai dai gwargwado, matar nan tasa tana matuƙar kyautata masa shida 'yan uwansa dukda yadda suka tsaneta suka sata gaba, suna ganin komai ya samu akanta yake ƙarewa, gata da yawan larura Kasancewar tana da Athma, kuma genotype ɗinta AS ne, dan haka kusan kullum cikin rashin lafiya take da zaryar Asibiti, shi kuma yana jin tausayinta saboda mahaifiyarta bata raye, ga mahaifinta bashi da cikakkiyar lafiya shima.
Idan ciwonta ya tashi, shine yake ayyukan gidan, ko kuma yayi zaman jinyarta a gida ko a Asibiti, duk wata kulawa daya dace ya bata yana bata, katsam Allah ya bata ciki ba zato ba tsammani, ya dinga murna shida ita, sedai cikin beje ko ina ba ya zube saboda yawan rashin lafiya.
Bashir mutum ne me tawakkali dan haka be taɓa gazawa ba, baya nuna mata ya ƙosa da rashin lafiyar da take yawan yi, ya kance a tausayi irin na mata da son da matarsa Jidda ke masa, idan shine yake a halin yawan larurar nan bazata guje shi ba, to shi meze sa ya gujeta, bayan ba ita tayi wa kanta ba, Allah ne ya jarabceta.
Bashir Ya zama abun kwatance a dangi, mijin tace nusari da ire iren wannan miyagun sunayen haka suke kiransa, wai ya ƙare a gindin mace seta talautashi tukuna ta tsiyata shi, kullum cikin ciwo gashi bata da wata mamora tunda ba haihuwa take yi ba, ya zamana saboda irin wannan cin mutunci da ake mata ko shiga tarurrukan biki ko suna ko makamancin haka ya hanata, saboda muddin zasu haɗu da 'yan uwansa gorin nan ne se anyi shi.
Idan suka fuskanci baya gari, haka zasuje har gida su zazzaga mata rashin mutunci iri iri, su ɗauki abunda suka ga dama, suce ai kayan ɗan uwansune, banda tayi Asiri ta mallake shi, ta yaya ze dinga bata abubuwa bayan juyace ba haihuwa take ba, se aikin larura dasa ɗanuwansu zaryar Asibiti, duk ta tsiya tashi saboda yawan rashin lafiyar da take yi, yayi da lafiyarsa yayi da aljihunsa, dan hatta jini idan ta buƙata shike bata.
Ita kuma ba sawa ba fitarwa, haka zasuyi abunda suka ga dama idan sun tafi ta sha kukanta, kamar yadda suka saba baya gari sukaje suka mata cin kashi yadda suke so, ya dawo ya tarar da ita tasha kuka, ya tambaye ta meyasa meta? Tace masa ai bakomai, seda taga ze ɗau zafi sannan ta gaya masa, shi yayi mamaki, be taɓa sanin har gida suke biyota suyi mata ba, aikuwa yaje yayi musu tatas, kuma yace musu mutu ka raba shi da matarsa, tana da matsayi me girman gaske a zuciyar sa, dan haka komai tayi bata laifi a gurinsa, yace larura da lafiya duk na Allah ne, me lafiya na ina komawa mara ita, mara ita ya samu, babu wanda yake sa kuɗinsa dan ya sai cuta, sedai Allah yana jarrabar komai, dan haka ya yadda rashin haihuwar Jidda, da rashin