Showing 123001 words to 126000 words out of 209297 words

Chapter 42 - Akidata Book 2 Hausa Novel Complete

01 Jan 2025

760

miki ɗauki ne? Ba wani abu fa rainane ya biya kawai, ki kwantar da hankalinki kici Arziki ki barshi"

Kici kicin ƙwacewa ta shiga yi amma ya riƙeta gama, yana wani lashe baki kamar kare yace "'yar uwarki ta fiki wayewa, ke kamar ba' yar birni ba"

Ya fara ƙoƙarin rabata da kayan jikinta, sosai Amal take ihu tana ƙwacewa, tana rirriƙe jikinta tana kururuwa, amma tsohon najadun nan ko a jikinsa, burinsa kawai ya cimma burinsa, Amal ta dunƙule hannu ta dinga kai masa naushi kota ko ina, wani naushi data kai masa a ido a gigice ya sake ta, yaja da baya, ta durƙusa tana ƙoƙarin mayar da kayanta, kuma taso mata yayi haiƙan yana kuma riƙeta, sosai kokawa ta ka came a tsakanin su, ya hankaɗata ƙasa ta faɗi akan hannunta, ta kurma wani uban ihu, saboda azababben zafin da taji ya ratsa hannunta, haka ta kuma yunƙurawa ta miƙe sedai ta kasa ɗaga hannun nata, ganin zata hana shi rawar gaban hantsi, be tausayawa halin da take ciki ba, ya shammaceta ya buga mata kwalba a goshi, ta kuma kurma ihu ta baje a gurin a sume.




Yusuf seda ya kwana biyu sannan ya iya cigaba da fita, sedai wata irin shaƙuwa da kusanci ne ke ƙara shiga tsakaninsa da Widad, wata irin kulawa take bashi ta musamman wadda bata masa a baya, ga Jamila dake ƙara sata a hanya yadda zata dinga kula da mijin ta, gefe guda kuma ta tara ɗalibai sosai, idan yamma tayi cika gidan megari ake yara da manya tana koyar dasu ilimin addini dana zamani.
Yau Widad ta haɗa kayanta dana Yusuf ta wanke su tsaf, gwanin ban sha'awa.

Yusuf ya dawo a gajiye, yana dawowa ya tarar da Widad harta dafa ruwan wanka ta ajiye masa.
Yusuf yayi murmushi yace "Waini wannan kulawar da ake bani fa, nifa abun yana mamaki, an maida ni wani ɗan gata meye sirrin ne?"

Widad tai masa fari da ido tace  "tukuici kawai zaka bayar, if you really appreciate"

"to me akeso in bayar?"

Ba tace masa koma ba se murmushi da tayi, tana sake kashe masa ido, Yusuf yace "Ohh my God, wannan kallon da kikemin se in rasa ina zan sa kaina, gaba ɗaya narkamin zuciyata yake Baby"

Widad tai dariya tace "shagwaɓaɓɓe kawai, ji yadda yake magana kamar wani Baby"

"Baby ne mana, tunda na auri Baby nima na zama baby ai"

"Naji, je kayi wanka kazo in baka Abinci a baki zaka ci?"

"zan mana, dayawa ma zanci sosai tunda Baby ce zata bani a baki"

Yai murmushi ya fice daga ɗakin, yaje yayo wanka ya dawo ɗakin, sedai ya tarar bata ɗakin tana tsakar gida, yana zuwa yaga babu kayansa, ya duba Akwatin Widad yaga kayansa a wanke, ya ɗadɗaga ya haska yagansu a wanke fes, mamkine ya kama shi, ya fito ya ƙwala mata kira, ta taso taje Yusuf yace
"My Wife, gani nayi kamar an wanke min kaya, ya haka?"

Widad tace "to meye yafaru? Ko laifi ne?"

"Amma waye ya wanke min? Nidai nasan baki iya wanki ba, ni nake mana to yaya akayi aka wanke su?"

"Shikenan kuma a haka zan zauna ban iya komai ba,? To in gaya maka na iya aiki sosai yanzu, nice nan na wanke mana su ɗazu"

Yusuf yace "abun mamaki, yanzu ke kika wanke mana kayan nan duka? Ina mamaki fa"

"wallahi nina wanke mana, ko basu fita bane?"

"Ni na isa ince basu fita ba, sun fita fes, amma baki saba ba karki sake wankewa, zan wanke mana da kaina kinji matar Yusuf"

"A'a gaskiya, ni dai sena wanke"

Yace "bafa na son gaddama, kawai ka bari nagode Allah yayi albarka, amma ni zan dinga wanke mana kinji beautyna"

"A'a ai kai ba bawana bane, dan haka nima yakamata in dinga ƙoƙartawa, tunda ina iyawa ai bakomai kai ba murna zakayi ba ina koya ba"

Yusuf yace "naji amma ki bari mu dingayi tare, kinji Babyn Yusuf"

Tace "to naji"

"Yawwa Babyna I love you" yai maganar yana kissing din goshinta, bata bashi amsa ba se murmushi da tayi, tana lumshe ido, babban abunda yake bawa Yusuf mamaki da ita be wuce yadda idan har yace yana sonta, sedai tayi murmushi amma ita ta kasa gayamasa hakan, har yanzu yakasa gane haƙiƙanin abunda yake ranta, sedai yana ganin kishinsa da tausayinsa muraran a idonta, sedai tausayi da kishi suna cikin alama na soyayya.


Widad tace "zauna inzo in baka abincin, naga kwana biyu ba kaci kana ƙoshi, bana son mu koma gida a ganka a rame, bazanji daɗi ba, aga nayi ƙiba mijina kuma a rame ba'"

Yusuf yace "inyee kaga masu miji, kamar ba mutum ne yake cewa shi be yadda da Aure ba, baze aura ya zauna a ƙarƙashin wani ba, kawai se naji mutum yana cewa ina son Aurena Yoseef, Zan zauna da kai a yadda kake, ya akayi mutum ya canza ra'ayi ne haka da sauri?"

Murguɗa baki tayi tace 'bana son tsokana fa"

Yusuf yayi dariya yace "gayamin meyasa kike son Aurennaki ne? Gayamin mana"

Widad tace "nima ban san yadda akayi haka ba, a baya ina da dalilin da yasa nace bazan yi aure ba, amma yanzu na samu mijin marainiya, wanda yake lallaɓani ban yaɓa zaton akwai miji irinsa ba, ka bani farinciki mara misaltuwa, shiyasa nake jin kamar bazan iya bari kayi nesa dani ba, shiyasa nake son Aurena "

Yusuf yayi murmushi yace "Mutum ma ya faɗi gaskiya ma, se wani kauce kauce kike, zama ki faɗi gaskiya ne ai"

Widad ta buɗe baki tace "ba ruwana, Allah ya shiryeka, a haka kaman salihi amma mutum yaita sakin magana"

"Kyaji dashi dai, ni dai azo a bani Abincina inci yunwa nakeji"

Ta zauna tana bawa Yusuf Abincin sa a baki, suna hirarsu cikin nishaɗi da jin daɗi.






Amal kawai farakwa tayi ta ganta akan gadon Asibiti, taga kanta nannaɗe da bandeji, hannunta ma data faɗi akai haka, mamkine ya kamata ta juya ta ganta a ɗakin Asibiti a kwance, ga wani irin raɗaɗi da yake ratsata daga tsakanin ƙafafunta.

Shiru tayi taga Mummy ta shigo ɗakin hannunta da ledar magani, ta ƙaraso da sauri tana Autana sannu, ya jikin naki ne?"


Amal tace "Mummy meya sameni ne?"

Mummy tace "hatsari kika yi mana Baby, ina zaune a gida Alhaji Haruna yayi min waya yacemin bayan kin kai masa takaddar, kika samu hatsari a titin unguwarsu"

Wani uban ihu ta saki, da tuno abunda ya faru tsakaninta da Alhaji Haruna, ya mata fyaɗe kenan, kuma yake gayawa mahaifiyarta hatsari tayi.

Ta fashe da kuka, tana jujjuya kanta, wani irin baƙin ciki ne da takaici ya mamaye mata zuciya.

Mummy tace " Haba Amal, kiyi haƙuri dan Allah, ai abun be tsawwala ba Autana, karaya kika samu a hannu se kwalba daya fasa miki goshi, Ai Alhaji Haruna yayi mana mutunci, shiya kawoki Asibitin nan"


Kawai Amal ta dinga kuka, ji tayi kamar ta shaƙe mahaifiyarta jin maganar da take, ya cuceta ya kassara rayuwarta, ya raba ta da mutuncinta, kuma ya kawota Asibiti yace hatsari tayi, ji tayi kamar zuciyarta ta tsaga ƙirjinta ta fito saboda azabar baƙinciki da takaici, tama rasa me zata yi, kawai ta fasa ihu ta fizge ruwan dake jikinta tayi jifa dashi, ta dinga wani uban ihu, da ƙyar aka kira likitoci, aka daddanneta akayi mata allurar bacci.


Mummy ta kalli likitan cike da damuwa tace "Doctor, wai dan Allah meyasa meta ne? Naga kamar ta haukace"

Likitan yace "A'a ba haukacewa tayi ba, stress ne da damuwa suka ɗan dameta amma insha Allah komai zezo da sauƙi, zamu sake mata hoton hannun, idan hali yayi a goben ma insha Allah zamu iyayi mata aikin, tunda Alhaji Haruna ya gama biyan komai, dama anan yake da family file "

Hajiya Halima tace
"shikenan, mungode nidai Alhamdilillah tunda ba wani abunne ya sameta ba"







Bayan sallar isha'i Yusuf ya shigo, ya tarar da Widad a kwance ta kunna fitila, tana ta saƙa maficinta daga nan inda take kwance, yai sallama ta amsa, yana zuwa ya kwanta a kanta.

Cikin Shagwaɓa tace "wayyo Allah na, Yuzarsef meye haka? Kana fa da nauyi seka danne min kan Babyna"


Yusuf yace "wainine nake da nauyi, ina wani Baby yake anan?"

Tace 'ba a nan mana" tai maganar tana nuna masa cikinta.

Yusuf yasa hannu ya danna cikin nata yace "Malama bakomai anan hanji, waye yace miki a nan ɗa yake zama"

"wayyo Allah na, Yoseef yau cinzali kake ji, dan Allah ka dena danna min cikina, kar kasa in haifi ɗa da lotsatsen ƙeya mana"

Yace "Madam wannan cikin naki bakomai a ciki, inma akwai be zama mutum ba, amma duk kin ishi mutane, ke wannan idan cikin ya samu na shigesu, da langwai da Shagwaɓa"

Widad ta tura baki tace "Yuzarsef, da nace zan sakawa jaririna sunanka, amma na fasa tunda kana adawa da baybn nan nawa"

"Au da bazaki saka sunan Daddy ba, se sunana?"

"Eh mana sunanka zan samasa mana"

Yusuf yace "salon Daddy yace kinfi son mijinki akansa"

Tace "to ai dai ɗana ne naga, ko ɗan Daddyn ne?"

"Iyee, ba kara ba kunya Baby, Allah ya shiryeki wallahi za'aga uwa mara kunya gaskiya"

Tace "eh naji ɗin, ni ɗagani karka samin ɗa kuka"

Yusuf yace "iko se Allah, wai yanzu ke kin haƙiƙance ɗane a cikinki? Kwana nawa kika ƙara baki period ba?, ina shekaranjiya kika cemin mararki na ciwo baki period ɗinba?"

"Ai bezo ba tukuna, kwana biyar ya ƙara fa, Insha Allah ina da ciki"

Yusuf yace "mara kunya kawai" yai maganar tare da danna gefen mararta ɗaya, wani irin ihu tayi haɗi da zillo, se hawaye, Yusuf ya bita da kallo yana nazarinta.

Cikin hawaye tace "Yusuf meye haka? Da zafi fa wallahi"

Yusuf yace "yi haƙuri, am sorry kinji babyna, yi haƙuri bazan sake ba insha Allah, abu nake son ji"

"Ni ƙyaleni, kawai se cin zalina kake, kuma bazan kwana da kai ba a katifata ba, tunda haka ka koma"

"Ke kin isa ki koreni daga kan katifar nan, ina nan tare zamu kwana semun samo Babyn Baby"

"Ni na samu Babyna in gaya maka, kuma sena rama abunda kayi min, ni wanka zanje inyi"

Yusuf yace "ina nan ina jiranki, kije kiyi wankan kizo kimin tausa inyi bacci"

"bazan ba" tai maganar tana hararasa, sannan ta miƙe ta fice daga ɗakin tana murmushi.


Haka suka kwana tare abunsu, cike da soyayya da ƙaunar juna, tana sake jin Yusuf a zuciyarta, bata jin zata iya rabuwa dashi.



Saleh kam iya azaba ya shata, su ciko bokiti su danna kansa a ciki, seya suma, banda wutar lantarki da suka dinga jona masa, ga ba Abinci babu ruwan sha, ya galabaita fiye da tunani, banda duka da suke masa da katakwaye, sun masa laga laga gaba ɗaya Saleh ya zama abun tausayi, ya galabaita ya lalace saboda azaba, suyita buga masa itace a ciki, kai da ƙirjinsa, ya dinga fidda jini ta baki da hancinsa, gaba ɗaya ya suma baya hayyacinsa a haka se da aka kwana uku, sannan suka yi waya suka sanar da Bukar, yace musu yana nan tafe zezo gidan da ake ajiye da Saleh yaji idan yayi laushi zuwa yanzu.





"Alhaji Bukar, kana sane da cewar mahaifinmu yazo har gidanmu ya saka hannu ya mareni?"

"Eh, naji na samu labarin zuwansa, amma ni sam ban san da zancen ya dakeki ba"

Ramlah tace "to ya saka hannu ya dakeni, bayan tsawon shekaru be san cina shana ko suturata ba, an gayamin cewar hatsabibine, dan haka sonake in nuna masa ya haifi wadda ta fishi hatsabiban ci"

Alhaji Bukar yace "Anya zakifi mahaifinku hatsabibanci kuwa? Amma me kike so ayi masa?"

"Sonake a nemo shi duk inda yake, a sauke masa hannun da ya mareni dashi"

"Amma fa naga mahaifinkine, idan kikayi haka baki kyauta ba"


"Naga dai shima ba mutumin kirki bane, koda bama tare dashi, labarin aika aikar dayayi duk na sani, dan haka rama cuta ga macuci ibadane, zan kawo ƙarshen iya shegensa, a sauke masa hannu nake buƙata"

Alhaju Bukar yace "kin samu yarinya, kije kin kwantar da hankalinki, za'ayi abunda ya dace, yadda kike so haka za'ayi ai".



Koda Amal ta sake farkawa ta ganta a Asibiti ta tabattar ba mafarki take ba, ta sake fashewa da kuka, ta tuna yadda suka yi da Alhaji Haruna, shikenan Ya kassara mata rayuwa, ya cuce ta, ya gama da ita, tinƙahon kowace mace shine budurcinta amma a banza wani tsohon najadu dabba ya kassara mata rayuwa, ya tarwatsa mata rayuwa ya cuceta, wasu irin zafafan Hawaye suka shiga yi mata sintiri a fuskar ta, tana tunanin me zata yiwa Alhaji Haruna ta huce, me zata yi masa wanda zesa ta huce, ita gaba ɗaya Yusuf ta tanadar wa kanta, saboda babu komai a zuciyar ta inba shiba, dole tayi wani abu wanda zaya rama abunda Alhaji Haruna yayi mata.

Ramlah ta kalleta tace "Amal wai wannan wani irin kukane haka? Ki saurarawa kanki mana, Allah ya taƙaita miki wahala baki mutu ba, kuma hannun be cire gaba ɗaya ba, amma se kuka kikeyi, ki kwantar da hankalinki dan Allah kiyi haƙuri.

Mummy da ta idar da salla tace " tayani gaya mata dai Ko zataji, tunda abun nan ya faru take kuka, na rasa kukan ubanme take haka? Ni kin kai masa takadda makuwa kafin abun ya faru?"

Banza tayi mata, ta ɗauke kanta ta cigaba da kukanta, Alhaji Haruna ne yai sallama, ya buɗe ƙofar ɗakin ya shigo, hannunsa ɗauke da manyan ledoji, ya shigo suka gaisa da Mummy, yace " Ya jikin Auta kuwa? "

Mummy tace "Jiki da sauƙi, sedai se kuka take, taƙi yin shiru, kuma ga abun be tsawwala da yawa ba, karayace kuma ance yau za'a mata ɗori"

Alhaji Haruna ya zauna a gefen gadon yace "Auta ya jikin naki?"

Lallai mutumin nan ya cika gardin ɗan iska, ya mata wannan aika aika, sannan yazo wai yazo dubata, shiru tayi taƙi magana.

Hajiya Halima tace "Amal ba magana ake miki ba kika yi shiru? '

Alhaji Haruna yace "Halima ku ɗan bamu guri dan Allah, zan mata magana"

Ba musu suka fice, sedai kallo Ramlah ta dinga binsa dashi na tuhuma.


Yace "Haba Baby, daga abu ya faru shikenan seki ɗaga hankalinki, haba Baby Amal, kiyi haƙuri kinji ai is not that painful, zaki warke kuma karayar nan is just an accident, zaki warke insha Allah, amma kidena kukan haka kinji"

Ji tayi kamar ya kunna wuta a zuciyarta, tabbas ds da makami seta kasheshi kome za'ayi mata ayi, ga mahaifiyarta sam batayi hankalin gane abunda ya faru ba.

Ganin tayi shiru, yasa ya janyo ya jikinsa yana faɗin "you make my day jiya, na daɗe ban samu mace kamarki ba, ki kwantar da hankalinki mucigaba da rayuwar mu babu wanda ze gane kinji"

Amal tai shiru, taƙi buɗe ido zuciyarta ta dinga tafasa, ganin tayi shiru batayi magana ba, yasa seda yayi shagalinsa sannan ya dunƙulo bandir ɗin kuɗi ya zube mata.


Seda yaje bakin ƙofa ze fita tace "idan ba'a gaɓa gwada maka kaidin mace ba, ka fara ƙirgawa daga yau zaka fara gani, wallahi Haruna sena maka abunda bazaka manta ba har abada, sena maka Baƙin tabon da yafi wanda kayi min, wallahi sena ƙulla maka makirin da duniya basu isa su kwance maka ba, zaka gane baka da wayo daga maina bazaka sake gwada akuyanci akan wata 'ya ba, ka saurareni....'



.
LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
IDAN KUMA KIN SIYA AMANACE KARKI FITARMIN DAN ALLAH 🙏🙏🙏

(Albishir ga masoya, ma'abota bibiyar litattaafaina, dama ta samu zaku fara samun litattaafaina na audio, akan YouTube channel ɗina me suna Cool Arewa TV
https://youtube.com/channel/UCD5vnvA5laU8ti4LLz2_QEg

Kuyi liking sannan ku danna subscribe, domin fara samun litattaafaina na audio, nagode sosai da ƙaunar ku gareni"
11/21/21, 7:45 AM - Buhainat: LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
IDAN KUMA KIN SIYA AMANACE KARKI FITARMIN DAN ALLAH 🙏🙏🙏

(Albishir ga masoya, ma'abota bibiyar litattaafaina, dama ta samu zaku fara samun litattaafaina na audio, akan YouTube channel ɗina me suna Cool Arewa TV
https://youtube.com/channel/UCD5vnvA5laU8ti4LLz2_QEg

Kuyi liking sannan ku danna subscribe, domin fara samun litattaafaina na audio, nagode sosai da ƙaunar ku gareni"

112_113

Alhaji Haruna yai murmushi irin na tsofaffin 'yan duniya sannan yace

"hmm Yaro man kaza, wato shi dai yaro yarone kam, ke a gwagwarmayar da nayi, babu kalar karuwar da ban gani ba, babu kalar barazana da kaidin matan da ban gani ba, nayi Aure Aure, nayi biye biye ba irin matan da ban gani ba, dan haka' yar ƙaramar barazanar ki bazata tsoratani ba, you better calm yourself down, ba'a kanki aka fara ba kuma ba'a kanki za'a ƙare ba, karki ƙarawa kanki ciwo akan ciwo, ki kwantar da hankalinki ki more ƙuruciyarki ki tara abun duniya"

Wani gululun baƙin ciki ne yazo ya tokare maƙogwaron Amal, wanda yasa ta jan numfashi da kyar, ta rasa me zata yiwa Alhaji Haruna wanda zesa taji ta rage azabar da zuciyarta ke mata, ga karaya data samu ga rauni a kanta, ga uwa uba fyaɗe da yayi mata, kuma yazo ya tsaya yana gayamata maganar banza, ta lumshe idonta wasu irin hawaye na takaici da baƙin ciki suna bin gefen idonta.

Tana jinsa ya buɗe ƙofar yai waje abunsa hankalinsa kwance wani nishaɗi yana ratsashi, dan ba abunda yake ji na damuwa ko tashin hankali a tare da shi dangane da abunda ya aikata.

Kusan mintuna ashirin da fitarsa, Ramlah tai sallama ta dawo ɗakin, ta janyo kujera ta zauna a gaban gadon Amal, Amal tace 

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login