Showing 99001 words to 102000 words out of 209297 words
mecin mutuncin uwata in ƙyaleshi, ɗakin baccinta gurin sirrinta ne, dan haka babu me shiga, jibi in Allah ya kaimu zamu tashi mu bar muku gidan, ba zamuyi shari'a daku ba, amma Allah ya biwa Ummana haƙƙinta"
Bello yace "kaikuma kai a wa? Gayyar tsiya arna a idi? Kama je kayi shari'ar damu mana, dalla gafara nan a duba ɗaki sirrin banza sirrin wofi"
"Wallahi taku ɗaya ka ƙara daga inda kake, kai yunƙurin shiga ɗakin nan idan na ɗaga ka se nayi jifa da kai ta katangar nan wallahi"
Tabbas yadda ƙirar jikin Yusuf take, dukda ba wani girma yayi ba tsaf ze iya aikatawa, haka suka haƙura suka tafi suka ƙyalesu.
Umman Yusuf ta cigaba tana cewa "Yusuf Allah yasaka mana, kana gani ana cewa an kashe Abbanka, aka dawo da motarsa suka ɗauka suka siyar, banyi magana ba, kuɗinsa suka fito suka wuce gaba suka karɓe suka cinye, se a bakin jama'a naji labarin kuɗin sun fito, duk 'yan kadarorin daya bari sun siyar, kuma suna kallon wahalar da nake yi, babu tausayi babu imani a tare da su, ya suke so muyi da ranmu Yusuf, sun cutar damu"
Tai maganar cikin kuka da sheshsheƙa, Yusuf yace "Umma kidena kukan nan, zanje a samo me siyan injin markaɗen nan, da ɗan cinikin da mukayi mu samu gida ko ƙaramine mu kama"
Jinjina masa kai kawai tayi, tana share Hawaye, Yusuf yace "Umma wao ya akayi kika san haƙƙin Abba ya fito sun cinye?"
Ta share hawayenta, ta gayamasa yadda suka yi da ɗan sandan nan, Yusuf yace "Umma tunda ya gayamiki haka, kuma beyi ƙoƙarin taimakonmu ba to tabbas dashi aka ci kuɗin nan, dan babu yadda za'ayi ba'aci kuɗi dashi ba yasan anyi, abunda nakeso dake shine kiyi haƙuri, Allah baya bacci, ki bar batun kaisu ƙara, mu barwa Allah, Insha Allah Ummana wataran zaki yi dariya zamuji daɗi, kidena kuka Umman Yusuf "
Yana maganar yana goge mata hawaye.
Yusuf kai inji kasuwa ya siyar, sedai babu wata daraja, saboda anga a Matse suke, suka har haɗa suka bada rabin kuɗin gida, suka wani ƙaramin gida haya, suka koma ciki suka zauna.
Yusuf ya kusa shiga aji shida ma sakandire, dan haka yasan dole za'a buƙaci kuɗi a hannun su, kuma yasan Umman bata dashi, ga kuɗin hannunsu babu, ɗan Abincin da suka koma gida dashi babu, ga babu jarin sana'a, kuma kuɗin haya rabi suka bayar .
Yazamana Yusuf ya fara tunanin mafita, ana idar da sallar Asuba, yake zuwa ya karɓi hayar kura yayi ga ruwa, ya tattara abunda ya samu, ya dawo gida ya saimusu abun karyawa, Umma ta matsa se taji inda ya samo kuɗi, yayi mata bayani aiko se kuka tace "Allah ya jiƙan Bashir, da yana raye nasan babu yadda za'ayi ya bar abun ƙaunarsa yayi wannan wahalar, Kayi haƙuri Yusuf nakasa baka kulawar data dace"
"Haba Ummana, aini na wuce lokacin da zaki nemo ki bani, sedai in nema in baki, dan Allah kidena kukan nan, kidena wannan tunanin please"
Haka rayuwa ta cigaba da ja, Yusuf sana'a iri iri, yayi wannan yayi waccan komai ƙasƙancinta kuwa, harya ɗan tarawa Ummansa jarin saida man ƙuli da manja a cikin gida, a haka suka tara cikon kuɗin haya, suka biya suka ɗan samu sassauci gurin samun Abincin da zasu ci.
Dayake da suka tashi ba nisa sukayi da unguwar tasu ba, dan haka wani lokacin idan ya turo kurar ruwa, yakan haɗu da maƙotansu na da, se yaji suna "Ohh rayuwa juyi juyi, wai yau ɗangata ke tura kurar ruwa, dama shiya dace dashi tunda dai ba'a gatan aka haife shi ba"
Yusuf baya tankawa, shi dai babban burinsa asirinsu ya rufu shi da Ummansa.
Allah ya temake shi yaci qualifying, dan haka kuɗin Neco kawai ya biya, da na Jamb dayake Asusu sukayi shida Umman, suke jefa abunda ya samu saboda hidimar karatunsa.
Yusuf ya zana jarrabawa gaba ɗaya, Waec, Neco, da kuma Jamb, dayake Allah maji roƙon bawane, kuma kullum cikin yi masa addu'a Umma take, Se Allah yasa ya tsallake gaba ɗaya jarabbawarsa, ya samj maki me kayu da ake nema, dan haka har admission ya samu a jami'a, sedai fannin daya ɗauka na medicine, kuɗinsa ya kai kusan naira dubu sittin ta wannan lokacin, wadda kuma kuɗi ce masu yawa a wannan zamanin, Nanfa murnar Umma ta koma ciki, ina zata samu wannan kuɗin? Me take dashi wanda zata yi ta cika burin ɗanta? Burin da dashi Abbansa ya rasu, Yusuf yayi karatu ya amfani al'umma......
LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
IDAN KUMA KIN SIYA AMANACE KARKI FITARMIN DAN ALLAH 🙏🙏🙏
(Albishir ga masoya, ma'abota bibiyar litattaafaina, dama ta samu zaku fara samun litattaafaina na audio, akan YouTube channel ɗina me suna Cool Arewa TV
https://youtube.com/channel/UCD5vnvA5laU8ti4LLz2_QEg
Kuyi liking sannan ku danna subscribe, domin fara samun litattaafaina na audio, nagode sosai da ƙaunar ku gareni"
11/15/21, 4:53 PM - Buhainat: LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
IDAN KUMA KIN SIYA AMANACE KARKI FITARMIN DAN ALLAH 🙏🙏🙏
(Albishir ga masoya, ma'abota bibiyar litattaafaina, dama ta samu zaku fara samun litattaafaina na audio, akan YouTube channel ɗina me suna Cool Arewa TV
https://youtube.com/channel/UCD5vnvA5laU8ti4LLz2_QEg
Kuyi liking sannan ku danna subscribe, domin fara samun litattaafaina na audio, nagode sosai da ƙaunar ku gareni"
102_103
Abu ya zamana ga ƙoshi ga kwanan Yunwa, ga bikin zuwa babu zanin ɗaurawa, course me wahalar samu gashi Allah yabawa Yusuf amma babu hanyar yinsa.
Yusuf kam ya fidda rao, dukda ƙaunar karatun da yake a ransa, amma babu yadda iya, tunda yasan basu dashi.
Allah sarki, Jidda ta damu kanta, tasan ba lallai ya kuma samun wannan damar ba, yana son karatun sosai, idan be samu ba tasan abun ze dameshi, amma baze nuna mata ba, ta duƙufa addu'a, ta nayi tana rarrashin Yusuf akan idan karatun nan be samuba, su barwa Allah, Allah ya kawo masu mafita.
Sam Yusuf baya nuna mata da ya damu lallai se yayi karatun, 'yan unguwa suma ganin yadda suke fama da rayuwarsu, amma babu me tallafarsu se Allah.
katsam aka kira shi a waya akace gwamnati ta bashi scholarship, an fidda gwarazan shekara na makarantun kimiyya da fasaha, kuma Sunan Yusuf ya fito ya samu.
Shi Yusuf jin abun ya dingayi kamar almara, banda iko na ubangiji wa zeyi wannan hukuncin haka? Umma kamar ta zuba ruwa a ƙaaa ta sha dan farinciki, tayi murna ta godewa Allah, babu zato babu tsammani dama tazo musu ba tare da wata wahala ba.
Akayi shirye shiryen komai ya fara karatu, sedai wannan karatun karatune me wahalar gaske, ba karatun ne matsalar Yusuf ba sedai kuɗin transport, na handout excursions, practicals, field trips, kullum cikikn kawo kawo ake, gashi baya samun damar yin 'yan sana' oinsa saboda zaman makaranta.
Dama a unguwa babu ruwansa da kowa, ko abokai bashi da su saboda gudun gori da wulaƙancin mutane, Amma dukda haka be tsira ba, aita surutu waiya fiue girman kai, daba'a san wayeshi bane shine ze dinga jawa mutane aji, yana wani hura hanci, shi dai shirune nasa, baya tofa komai baaa gaban sa.
Karatu abu fa ya fara gagara, da ƙyar Yusuf ke iya karatun nan, saboda babu, Yusuf gashi ƙwaro na gaske saboda haddar Al'qur'ani babu karatun dake bashi wahala.
Shekararsa biyu yana karatun, akayi zaɓe aka canza gwamnati, ba tausayi ba ragayya ga yaran talakawa gwamnati tace babu kuɗi, bazata iya cigaba da biyawa yaran da aka bawa scholarship kuɗin makaranta ba, wanda yake da hali ya ɗau nauyin kansa.
Yusuf yanaji yana gani ya ajiye karatun medicine ya dawo gida ya zauna, Umma seda tayi kuka, shiko Yusuf akwai dakiya yaita bata haƙuri yace "Umma da bamu san zan fara karatun bama, Allah ya bani dama, yanzu kuma ya ƙwace damarsa, mu ɗauka a ranmu Allah yayi mana wani tanadine wanda yafi wannan karki damu Ummana"
Ita babbr damuwarta kar karatun ya fita daga ransa, yazo ko an samu damar ya ƙiyi takasa cika masa burinsa.
Nanma 'yan unguwa suka ɗau surutu, dan Ya dena zuwa makaranta, baƙaƙen maganganu habaici da zunɗe haka yake ganinsu kala kala, Yusuf ya kan rufe kansa a ɗaki da daddare yayi kuka, yayi kuka har ya gaji ya bawa kansa haƙuri, tun tasowarsa yake fuskantar ƙubalen cin zarafin wai shi bashi da iyaye, a gidan marasa iyaye aka tsinto shi,har yanzu yi ake ba'a fasa ba.
Yusuf ya dawo zaman gida, ya shiga neman yadda zasuyi su rufawa kansu asiri shida Ummansa, a haka wani mutum anan maƙotansu, dan sun ɗanfi wanda suka baro mutunci, ya samowa Yusuf Form na polytechnic, Yusuf yaji daɗi Sosai dan shi yanzu duk abunda yazo masa a rayuwa karɓarsa yake, bashi da wani zaɓi wanda ya wuce hakan, ya sake jamb ya cike Civil engineering a nan polytechnic, aikuwa ya samu ya fara zuwa, cikin ikon Allah sana'ar Ummansa ta mai ta kafu ta karɓu, ana siya sosai, ta nemawa Yusuf gurin koyon sana'a a gurin masu furniture, shima seda ta biya kusan dubu hamsin sannan aka karɓeshi.
Kullum idan ya dawo daga makaranta, se yaje gurin koyon aiki, idan ya tashi ya shiga kasuwa yaga meze samu yayi, saboda baya san ɗorawa Ummansa wahala, sam Yusuf bashi da hutu, a haka ya kammala poly, Umma tace baze tsaya ba, ya nemi Form na D. E ya tafi, shi gaba ɗaya jikinsa ya fara sanyi da harkar karatun nan, ta bashi kuɗi yaje ya karɓo form yayi applying, aikuwa by luck ya samu suka bashi level 2 a university, haka nan yau akwai gobe babu haka rayuwa ta dinga tafiya, a wahalce da ƙyar Yusuf ya kammala karatun nan, aka zo maganar tafiya service, Umma taji bazata iya jure Yusuf ya bar gari ya batta ba.
Haka akayi cuku cuku, Yusuf yayi service ɗinsa a kano, bayan an kammala yazo babu aikin yi, sedai kame kame, ga inda yake koyar aikin kafintan Wasu yarabawa ne, masu muguntar tsiya, ganin yana da saurin ganewa yasa suke masa mugunta, gurin koyarwar.
Zaman haka ba aiki ba sana'a ya ishi Yusuf, sedai 'yan bige bige, amma a hakan idan Ummansa taji tana da kuɗi a jikinta, haka take siya masa kaya masu tsada na sawa, shiyasa bazaka ce suna fama da rayuwa ba.
Rannan yana zaune yana duba wayarsa, yaga wani posting, mutane nata tofa albarkacin bakinsu akan harkar tsaro, sedai babban abunda ya bashi mamaki, be wuce yadda mafi yawa sharhin da akayi, ƙorafine akan jami'an tsaro, seya tuna hirar da suka taɓa yi da Abbansa kafin ya rasu, ya tuna yadda akayi aka haɗa kai aka cinye haƙƙin ummansa, tabbas kamar yadda Abbansa ya faɗa, koda mutum ɗayane yake nagari a cikin 'yan sanda, ko yaya wani ze amfanu dashi, dan haka se yaji yana sh' awar yayi applying shima.
Sun gama cin Abinci shida Ummansa da daddare yace "Umma"
Tace "Na'am yaron kirki"
"Umma wata magana ce dama nazo da ita, so nake in gaji Abbana"
"Kamar yaya kenan?"
"Ɗan sanda nake son zama"
"Kamar yaya Yusuf? Bana son rasaka kamar yadda na rasa Abbanka, dan Allah kabar maganar nan"
"Umma, idan baki amince ba shikenan, amma Umma bakya tunanin da akwai wani tsayayyen ɗan sanda me gaskiya a gurin da an tsaya mana gurin karɓo haƙƙinki, Umma kin san mutane nawane ke shiga garari sakamakon rashin aiki yadda yakamata da wasu maciya amana sukeyi a ƙasar nan? Umma in dai zamu dinga ƙyamar aikin mu dingawa 'yan sanda kuɗin goro to tabbas za' aita cutar mutane, duk abu ba'a rasa na Allah, sedai idan suka yi ƙaranci zalunci ne yake yawaita, Umma idan kika bibiya akwai mata irin irinki wanda aka zalunta, kuma za'a cigaba da yi idan har ba'a ɗau mataki me kyau ba, ina son yin aikin ɗan sanda ne saboda in temaki al'umma, ima son zama ɗan sanda dan in ɗora daga inda mahaifina ya tsaya, dan Allah Umma ki amince, amma in bakya so na haƙura "
Jikinta ne yayi sanyi, ta ɗanyi shiru taga tabbas maganganun Yusuf haka suke, kuma tana da yaƙinin cewa Yusuf mutum ne nagari, abune mawuyaci a haɗa kai dashi a cuci wani.
Ta numfasa sannan tace " Shikenan Yusuf, na amince ubangiji Allah yayi maka jagora, ya goyi bayanka ya kareka a duk inda kake, Allah ya wuce maka gaba a al'amuranka, ina fatan zaka zama mutum nagari me gaskiya da riƙon Amana, Allah yasa a sanadiyar ƙudirinka ya zamana an share hawayen wanda aka zalunta, kayi gaskiya da adalci Yusuf "
Yusuf yayi murmushin jin daɗi da farinciki, yace " Insha Allah Ummana, in Allah ya yadda ba zanyi wani abu wanda ya saɓawa Alƙawarin da mukayi dake ba, Addu'ar ki nake buƙata, Allah ya kauda zuciyata daga aikata duk wani abu da ze saɓawa Allah "
Umma tace "Addu'a ai kullum cikinta nake Yusuf, ina fatan Allah ya tsare, amma bana son ka sha wahala, training ɗin nan nasufa da wuya, karka je su baka wanda bazaka iya ba, Abbanka yana bani labarin wahalar abun nan"
"Haba Umma, sekace wani ragon maza, kin ganina santalelen ƙato dani, se in goya maza goma in gudu dasu a bayan nan nawa"
Umma tai dariya tace "eh lallai, ba shakka naga alama kam"
Nanma Allah ya temake shi ya samu makarantar horar da 'yan sanda, Yusuf yasha wahala ya fuskanci ƙalubale daban daban, a haka harya kammala makarantar nan, sukayi passing out, Allah ya temake shi ya fita da babban rank, sakamakon yayi karatu yana da degree.
Yusuf ya kama aiki, sedai Umma kullum cikin nasiha take, na akan yaji tsoron Allah akan wannan aiki daya fara, cikin ikon Allah yana fara samun salary yazo ya zubewa Umma kuɗin yace "Umman Yusuf, Insha Allah inaji a jikina lokacin da zamu samu sassauci yazo, ga wahalarmu ta wannan watan, na karɓo salary"
Umma tace "Alhamdilillah, dama komai yayi farko zeyi ƙarshe ai, Allah yayi albarka amma ka ɗau kuɗinka, ni duk abunda ka sanmun karɓa zanyi ince Allah yayi albarka"
"Haba Umman Yusuf, wannan nakine halak malak, na bar miki, ba abunda zanyi dasu ni duk abunda kika sanmun a ciki shikenan nagode, ki fara more wahalar da muka sha Umma"
Kawai seta fashe da kuka, Yusuf ya rikice gaba ɗaya yace "subhanallah, Umma laifi nayi mikine? Yi haƙuri dan Allah, ban san zan ɓata miki rai ba"
Ta girgiza kai cikin kuka tace "Tun kana ƙarami Yusuf, naso inyi duk me yuwuwa dan ganin baka gane bamu muka haifeka ba, amma hakan ya gagara, duk yadda muka kai ga ɓoyewa nida Abbanka abu ya gagara, bakin mutane yakasa yin shiru, suka dinga wulaƙantamin kai da maganganu marasa daɗin gaske masu muni, har seda suka saka kasan bani na haifeka ba, amma haka kake min biyayya kamarni na haifeka, A baya nayi kukan Gorin rashin haihuwa, an goran tamin nayi kuka nayi kuka, amma tunda Allah ya bani kai, na dena wannan kukan, nasan ba lallai ɗan dana haifa yayi min biyayyar da kake mun ba Yusuf " ta ƙarasa maganar cikin kuka, Yusuf yaji ta fama masa ciwon dake raɗaɗi a cikin zuciyar sa, yaji kamar ya fashe da kuka, sedai be taɓa gangancin zubda hawayen rashin sanin suwaye iyayensa a gaban Jidda ba, dan idan yayi haka ya zama butulu abun Allah wadai, ya tattara nutsuwarsa ya dake, ya riƙe hannunta yace "wayema yace ba Yusuf ba ɗan Ummansa bane, samun uwa kamar Umman Yusuf me sadaukarwa da juriya a wannan lokacin se anyi tonawar gaske, Wa Yusuf zeso in be so Ummansa ba, waze wa Biyayya idan bebi Ummansa ba, Ummana ina neman Aljannata, duk me neman Aljannarsa Annabi salallahu alaihi wassalam yace yabi Allah da ma'aiki sannan yabi uwa, shiyasa nake bin tawa mahaifiyar domin neman albarka da samun wannan Aljannah, shiyasa nake bin Ummana nasan babi da abun biyanta ladan shayarwarta da ɗawainiyarta, Allah ya haɗamu a Aljanna gaba ɗaya, amma wannan kuɗin na Umman Yusuf ne halak malak, da Yusuf da abunda Yusuf ya mallaka duk na Ummane"
Ta rungume Yusuf ta fashe da kuka, a hankali Yusuf ya lumshe ido yana zubar da nasa hawayen ƙasa ƙasa, dan karta ji yana kuka, ta goge hawayenta tace "Yusuf indai nice, nagode sosai Allah yayi Albarka, amma ka ɗauki kuɗinka, kaje kayi buƙatunka gabanka, sedai ka ɗan sai mana Abinci"
Yusuf yace "Umma, nifa kuɗin nan bazan ciba, ki sanmun na mota zuwa gurin aiki kawai"
"A'a Yusuf, bana son jayayya fa"
Yusuf yace "ni na isa inyi Jayayya dake, tunda kin rasa abunyi dasu bari in baki shawarar yadda za'a kashe, ki rabasu biyu, rabi ki ban abunda zakimin, ki riƙe sauran, rabin idan mun samu kuɗi mudinga ƙarawa a kai, mu nemi fili a wata unguwar, mu fara gini, gara mu koma gidan kanmu "
Umma tace " na daɗe ina wannan tunanin Yusuf, yana da kyau ko fili mu siya, sedai bazan karɓe maka kuɗi duka ba, nasan kana da buƙatu kaima "
Yusuf ya haɗe rai, tace " ya dai naga ɓata rai"
"Umma ni zan baki abu kiƙi karɓa ko? Allah ya jiƙan masoyina, nasan da shine baze min haka ba"
Umma tace "shikenan, naji Allah yayi albarka, Allah ya kareka daga sharrin maƙiya"
Shigar Yusuf aikin ɗan sanda na farin kaya, nan da nan sunansa aka fara saninsa, musamman jin laƙabin sunan mahaifinsa, Yusuf Bashir Maitama, Yusuf akwai ƙwazo akan harkar aiki, baya wasa ba ruwansa da cin hanci ko rashawa shidai aikinsa kawai.
Bayan ya fara aikine ya gano irin cakwakiya da maguɗin dake cikin aikin, da irin tuggu da maƙrƙashiya dake aikin, ga me laifi ƙiri ƙiri kana gani amma saboda yana da wane ko yasan wane, se ace a ƙyaleshi, amma idan aka kamo ɗan malam wane ƙarshe 'yan sanda suna iya ajalinsa, ko ka samu case ka fara aiki a kai, daga sama se a turaka wani gurin a karɓe aikin, ko a ƙirƙiri laifi a ɗorawa wani dan a samu