Showing 177001 words to 180000 words out of 209297 words
me shari'a, duba da tarin hujjoji da shedu da kuma sakamakon' yan sanda, da muka gabatarwa wannan kotu, muna neman wannan kotu me albarka ta wanke wanda ake ƙara daga wannan tuhuma da 'ake masa
Justice Mustapha Yace " duba ga yadda shari'a ta kasance, da tarin hujjoji da shedu da aka gabatar, wannan kotu da dogon Nazari da duba ga kudin shari'a wannan kotu ta wanke wanda ake zargi, wato Yusuf Bashir Maitama, sannan wannan kotu me albarka tayi umarni da hukumar 'yan sanda su kama Alhaji Bukar Bulama, da muƙarabbansa don zurafafa bincike a sake gurfanar dasu, sannan hukumar' yan sanda zata biya wanda ake ƙara Wato Yusuf Naira million goma, sakamakon ɓata masa suna, da tauye masa haƙƙinsa a matsayinsa na ɗan ƙasa dukda dama da kundin tsarin mulki ya bashi, sannan kotu tana umarni a maida shi bakin aikin sa "
Yusuf yana jin haka ya fashe da Kuka, ya zube a gurin yana sujudu shukur ga ubangiji subhanahu wata'ala, kuka sosai kamar wani ƙaramin yaro, Umma ta taho da gudu, ta rungume shi itama tana zubar da hawaye, tawagar 'yan sanda suka rako Yusuf wajen kotu, yayin da akayi Ram da Bulama da Alhaji Haruna dake gurin, sannan aka bazama nemo sauran.
Yusuf na fitowa jama'a suka baibaiyeshi, sedai ya kasa magana se hawaye, Suleiman ya rungume Yusuf yana faɗin "barka da Arziki abokin aiki, barka da Arziki Yusuf"
Yusuf ya rungume Sulaiman shima, sedai ba bakin magana se hawaye dake fita daga idonsa, tawagar lawyoyin nan suka zo gaban Yusuf suka dinga miƙa masa hannu suna gaisawa, Cikin kuka Yusuf yake faɗin "Nagode, Nagode, Nagode" yana maganar yana kuka dan yama rasa meze ce musu.
Umma ta rirriƙe Yusuf, kamar za'a sake ƙwace mata shi, itama kuka kawai take yi.
Khalil yace "yau na sauke babban nauyin dana ɗauka, na Alƙawari ga Nurat, da nace zanyi iyayina inga ka kuɓuta"
Yusuf yace "Nurat kuma?"
Khalil ya jinjina kai, yace "Eh Nurat, sannan Yakamata a wuce dashi Asibiti, a duba lafiyarsa.
Bulama kuwa aka fito da shi, da Alhaji Haruna, dasu Musa a ƙasƙance, mutane nata tsine musu, 'yan jarida suka sa kasu a gaba, amma sukaƙi magana sam, suka duƙufar da kai kamar munafukai.
Bisa rakiyar' yan sanda, aka tafi da Yusuf Asibiti.
Yusuf kuwa ya galabaita, dan admitting ɗinsa akayi, yana buƙatar agajin gaggawa, saboda tarin raunuka dake jikinsa, gashi ya kasa dena kukan da yake yi, Suleiman cewa yake "Yusuf, kukan nan ya isa haka, ka godewa Allah, dan shine ya dubi halin da kake ciki ya fitar mana da kai, amma mun shiga cikin damuwa muma lokacin da ka shiga mawuyacin hali"
Cikin kuka Yusuf yace "Yallaɓai, yanzu kenan harda Abbas aka haɗa kai dan cutar dani? Yace be san da an bani aikin nan ba? Abbas fa? Aminina Abbas fa?"
Suleiman yace "koma dai menene, ba gashi kai ka kuɓuta ba, kuma nasan shima dole kotu ta neme shi ai"
Wayar Suleiman ta fara ringing, ya ɗakkota a aljihunsa ya saka a kunnensa, "Innalillahi wa inna ialaihi raji'un, ubangiji Allah yai musu rahama, Allah ya jiƙan su"
Umma tace "Sulaiman waye ya mutu?"
Suleiman yace "Ina Barrister Khalil? Lawyern daya dinga magana daga ƙarshe"
Umma tace "eh nagane meya sameshi?"
"Ai ɗan uwan Nurat ne, kuma itace ta tsaya kai da fata akan ganin an kuɓutar da Yusuf, Mahaifiyarta ce ta rasu, kuma mahaifintane ya turo uwar daga kan bene, dan ta masa magana ya kulle Nurat ɗin, ashe duk saboda shari'ar kane akan ta dage ayi maka adalci, ya gano ta san sirrinsa shine yai dalilin rasuwar mahaifiyarta"
Umma ta dafe ƙirji tace "subhanallah" , Yusuf ya girgiza kai hawaye na bin idonsa yace
"Allah sarki Nurat, Allah ya jiƙan Mummynki, nayi silar shigarki matsala kema Allah sarki Nurat"
(INA JIRAN TUKUCINA NA WANNAN OAGE ƊIN, TUNDA AN SAKAR MUKU YUSUF 😎😂😂)
Ayshercool
07063065680
12/7/21, 11:04 PM - Buhainat: LITTAFIN KUƊI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ƊAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
(Albishir ga masoya, ma'abota bibiyar litattaafaina, dama ta samu zaku fara samun litattaafaina na audio, akan YouTube channel ɗina me suna Cool Arewa TV
https://youtube.com/channel/UCD5vnvA5laU8ti4LLz2_QEg
Kuyi liking sannan ku danna subscribe, domin fara samun litattaafaina na audio, nagode sosai da ƙaunar ku gareni"
_(INNALILLAHI WA INNA IALAIHI RAJI'UN ina amfani da wannan damar gurin miƙa saƙon ta'aziyya ga Ɗaukacin zuriyar Hajiya Aisha Muhammad (Baba) bisa babban rashi da mukayi na rasuwar ta ina fatan ubangiji Allah ya jiƙan ta yai mata rahama, ya kai haske kabarainta, ubangiji Allah ya duba zuriyar da ta bari, ya bata ladan ɗawainiya da iyalI da tayi tsawon ranta, ubangiji Allah ya jiƙan kafatanin wanda suka rigamu gidan gaskiya Musulmi, idan tamu tazo Allah yasa mu cika da kyau da imani_)
IN THE MEMORY OF LATE HAJIYA AISHA MUHAMMAD, I DEDICATED THIS PAGE TO LATE HAJIYA AISHA MUHAMMAD (BABA) MAY ALLAH SUBHANAHU WATA'ALA, GRANT HER JANNATUL FIRDAUSI AMEEN _
148_149
Gaba ɗaya Bulama bega alamar Nasara a tattare da wannan shari'ar ba, wata zuciyar ta dinga rayamasa kawai yaje ya kashe Widad ya huta, wani sashin ya gargaɗeshi akan aikata hakan.
Haka ya koma gida jikinsa a sanyaye, babu alamar Nasara sam, yana zuwa ya tarar da Hajiya Sarah da Ramadan suna hira a falo, sedai da yayi sallama maimakon Ramadan ya amsa sema tsaki daya ja, suka kalleshi gaba ɗaya tace "Ramadan, are you out of your sense? Mahaifin naka kakewa haka? Ina yabo ka salla zaka kasa alwala?"
Nan da nan Ramadan ya shiga hawaye, "Mummy nayi dana sanin kasamcewarsa mahaifina wallahi, baki san halin mutumin nan ba mugune azzalumi macuci"
Buɗe baki sukayi suna kallon Ramadan, Yace "Mummy ina abun kunya ina abunda Daddy ya aikata? Saboda tsabar abun kunya wai 'yar' yar uwarsa, wadda take kamar a gareshi yake bi, Mummy Ramlah fa kuma ta tabattarwa da Fahad tana ɗauke da cuta me garkuwar jiki"
Gab ɗaya suka kalleshi a razane, Bulama yace "waye ya gaya maka wannan maganar banzar?"
"Karka ƙara kiran ta da maganar banza, dan ba ƙarya akayi maka ba, ko basu sani ba dama yau nayi niyyar zuwa in fayyace musu komai, ɗanka Fahad shine ya shafamin wannan ciwon, ni kuma nai alwashin shafa maka, dan haka ka bimciki lafiyarka, daga kai har matarka, daga yau kaida ɗanka seku shiga taitayinku ku kiyayi yaran mutane"
Kuka Hajiya Sarah ke ƙoƙarin yi, amma ta kasa ta dinga binsu da kallo, yayinda Ramadan ya daskare dan mamaki, Bulama yace "wallahi ƙarya kikemin, ni ban aikata haka ba, wallahi ƙaryane"
Ramlah tace "wannan kuma ya rage naka Bulama, nayi hakane dama dan tarwatsa kan iyalinka kamar yadda a sanadinka duk mun ɗaiɗaice babu wanda be abun kunya ba, gara a raba ai, ace kowama yayi"
Ta kalli Hajiya Sarah tace "Hajiya Sarah kece abar tausayi, Kasancewar kin zauna da baƙin kumurci tsayin shekaru baki san waye ba, ki gaggauta bincika lafiyarki, idan baki kamu ba shikenan, idan kuma kin kamu se ince Allah ya bamu lafiya baki ɗaya"
Ta juya ta bar musu falonsj, ta fics tana fita kuwa Hajiya Sarah ta yanke jiki ta faɗi cike da ɗimuwa Ramadan da Bulama sukayi kanta, sedai Ramadan yace "karka sake ka taɓamin uwa, Kuma insha Allah zaka ga sakamakonka tun a nan duniya, macuci mara imani kawai"
Ramadan ya shiga kiciniyar ɗagota, Fahad kuwa yana ta bayan ɗakin, yana laɓe yaji komai ya zame ƙasa ya zauna yana kuka, tabbas Ramlah ta rusa musu farinciki gaba ɗaya, farinciki na har Abada makuwa, ya shiga tunanin me zeyi wanda ze fanshe wannan cin mutunci da tayi musu?.
Hajiya Halima ma gidan Alhaji Haruna ta tafi, bayan jin irin katoɓarar da yayi mata akan Amal, taje ta sameshi shida Salma da uwargidansa a falo, da gani wata matsalar ce na family issues suke solving, taje musu afujajan kamar wadda tayi gobara a ka, tana zuwa ba sallama ba gaisuwa bakomai ta haushi da bala'i.
"Wallahi Haruna ka bani mamaki, nayi mamakin abunda ka aikatamin, ashe fyaɗe kayiwa Amal? Daga aikota ta kawo maka takadda dan baƙin zalunci, wallahi baka isa ba zakaga matakin da zan ɗauka akanka"
Uwargidansa ta bisu da ido, dan ita bata da wani baki sosai, Salma kuwa tace "ba shakka, biri yayi kama da mutum, shiyasa yarinyar nan ta dinga bibiyar ka? Tana turon saƙonni da ɓoyayyiyar lamba ashe dagaske ne abuika aikata? Ko kunya ba kaji ba gaka da yara mata, amma kayiwa wata fyaɗe?"
Cikin inda inda Alhaji Haruna yace "Ni, Ni wallahi ƙarya takemin ita ta kawo kanta"
Salma tace "kai ko kunya bakaji ba kake cewa ifa ga kawo maka kanta? Allah wadaran halinka nayi dana sanin Aurenk, Wallahi da in Auenka gara ace Yusuf ɗina na Aura dukda rashin asalinsa, dan nasan baze taɓa wannan akuyancin ba"
Hajiya Halima tace "Haruna ka bani kunya, ka bani mamaki ka cutar min da yarinya, gaba ɗaya kun kassaramin rayuwata data yarana, wancan ya ɓata kunce a kasheshi, wannan kai ka lalata ta, waccan kuma Bulama ya lalata ta ɗansa ma yayi, sun saka mata HIV, na rasa dame ma zan kiraku, kun cuceni kai da Bulama dukda kasancewarsa ɗan uwana Allah ya isa wallahi "
Tai maganar tana kuka, Alhaji Haruna ya saki tumbi yana kallonta, duk damfara da satar da 'yarta tayi masa bata gani ba se shi zata kalli abunda yayi mata.
Ya kalleta sama da ƙasa yace "Malama ki fita ki barmin gidana, kije can ku ƙarata, ita bata gayamiki abunda tayimin ba, se wanda nai mata, kije kiyi duk abunda zakiyi, kinzo kin ɗagamin hankali a cikin iyalina"
Hajiya Sarah ta kalleshi tace "ni kakewa haka? Ni kake kora daga gidanka? Kamin wannan mummunan abu sannan ka Kalleni kace in bar maka gida?"
fice daga gidan, zuciyarta na ƙuna gaba ɗaya yaranta sun lalace gaba ɗaya.
Salma taje gabansa ta tsaya tace "wallahi banga amfanin zama da fasiƙin mutum irinka ba, dan haka ka sakeni malam"
Alhaji Haruna yace "Ai Aurena dake har abada tunda iyayenki kwaɗayayyune, sunga kuɗi sun auramin ke wallahi bazan sakeki ba dan ina sonki"
"karka sake ka zagarmin iyaye, kuma wallahi seka sakeni tunda ba tare aka haifemu ba, macuci me abun kunya kawai"
Ya tureta yai wucewarsa yace "kanki ake ji, wadda taga zata zauna shikenan, wadda bzata iya ba ta ƙara gaba, amma saki kam babu shi"
Cikin kuka Salma tace "wallahi ƙarya kake seka sakeni, wallahi bazan cigaba da zama sa fasiƙi ba"
Uwargidan kam bata iya magana, sedai kuka dayake irin ta da ɗin nan ce, tun auren ƙuruciya gashi babu wani isashen ilimi a tare da ita.
Lamarin mahaifiyar Nurat fa sam babu sauƙi a lamarin, dan sati guda kenan babu wani cigaba, gaba ɗaya Nurat ta ɗaga hankalinta akan halinda mahaifiyarta ke ciki, jin mahaifintane yai sanadiyar faɗowar mahaifiyarta daga bene yasa taji gaba ɗaya ya fita daga ranta, ko san ganinsa ma batayi, gashi idan yazo Asibiti dubata 'yan uwanta suyi ta haɗe masa rai, ko sabgarsa basa shiga, Nurat kam an sallameta tuni amma taƙi barin Asibitin, idan tana buƙatar wani abuma gidan su Khalil take tafiya, gidan yayar mahaifiyarata kenan.
Ramadan kam Asibiti ya kai mahaifiyarsu, ya kira Iman dake makaranta suka zauna a gurinta dan kula da ita, dan ta samu shock ne a wannan lokacin.
Bulama kuwa bayan tafiyar Ramlah ya bita har gida, yana zuwa lokacin Hajiya Halima ta dawo da baƙincikin gidan Alhaji Haruna, yazo yana wani muzurai yace "Ina Ramlah take?"
Hajiya Halima ta kalleshi tace 'ban sani na, azzalumi ma cuci burinka ya cika, gaba ɗaya yaran sun watse Bukar saboda muguntarka da rashin imani"
Bukar yace "saboda son zuciyarki dai, da son Abun duniya"
"Ni kake gayawa haka?"
"Na gayamiki ɗin, ai ba ƙarya nayi miki ba, mugun son Abun duniyarkine ya janyo miki da kwaɗayi"
"Lallai Bulama ka cika butulu azzalumi, to wallahi zan taka bakin faranti komai ya watse"
"kar Allah yasa ki fasa takawar, kije kiyi duk abunda zakiyi, ai idan ta tashi watsewa tare zata watse mana, kuma ki sani idona idon Ramlah sena saka an kashe ta"
"ka daɗe baka sa an kasheta ba, kayi maza karka fasa"
Ramlah ta fito daga sashensu tana tauna cingan, kallo ɗaya za kamata kasan 'yar wisi ce, ta kalli Bulama tace "kai ka isa kasa a kasheni, ai base kunyi barazanar taka bakim faranti ba, kuji da abunda ke tunakaroku, Asirinku na daf da tonuwa a kotu, a nan yakamata ku maida kai mussman ma kai, ba wai zaka kasheni ba, dan ni na diha na kasheka da ranka tuni"
Ta ƙarasa maganar tana ɗura ruwan roba a cikinta, ta juya ta wuce dining dan cin Abinci, Hajiya Halima ji take tamkar tayi hauka, komai ya dagule mata, ta rasa meke mata daɗi.
Bulama ya fita da sacacciyar gwiwa jiki ba ƙwari, yanzu duk wannan barazanar da kwarinin dayake ana tsoronsa duk babu.
Tunda Ramadan ya ɗau mahaifiyarsa daga gidan basu sake komawa ba, har Allah yasa ta farfaɗo, aka ɗibi jininta aka gwada amma ba'aga ƙwayar cutar ba, akace bayan watanni uku zasu dawo sake yi, se kuka take tana tunanin wans irin lamarine wannan, ɗa ya nemi mace ta bashi kanta, kuma ta koma tabi mahaifinsa saboda Taɓarɓarewar ƙarshen zamani.
Daga Asibiti kai tsaye, Adamawa Ramadan ya tafi da Mummyn, saboda can ne ainihin garinsu.
Bulama yaje Asibiti aka ɗibi jininsa, da niyyar yasan a wani mataki yake, yana da cutar ko babu? Amma yakasa tsayawa a gaya masa sakamakon saboda fargaba ya gudu.
Haka abubuwa suka cigaba da damalmalewa azzalumai, basu fargaba lokacin komawa kotu yayi, ga kawunansu a rarrabe, kowa yana kallon kowa a banza, ga yadda suka dinga zaluntar junansu.
Yau kuma Barrister Hafiz ne ya fito ya gabatar da kansa, tunda Bulama ya ga Barrister Hafiz cikinsa ya ɗuri ruwa ya zuba ido yaga meze faru.
Barrister Hafiz ya fito ya gabatar da kansa, yace "Sunana Barrister Hafiz, lawyer me zaman kansa, ina ɗaya daga cikin lawyoyi gidan Alhaji Nasir Daula, kuma ina ɗaya daga cikin lawyoyin da zasu bawa wanda ake ƙara kariya, kimanin shekaru goma sha biyu baya, tun bayan da ayyana cewar kaso bakwai na dukiyarsa akwai me ita, yasa aka dinga bibiyarsa da 'yarsa akan lallai a karɓi wannan dukiya, har kawo ga kashe matarsa da akayi, wanda ba' a ƙarabi ta kan case ɗinba tsawon shekaru, a tare dani akwai shedu da hujjoji da zasu tabattarwa da kotu wanda ake ƙara bashi da hannu gurin yin garkuwa da 'yar gidan Alhaji Nasir Daula, ko kuma shi Daula kansa "
Ya ƙarasa inda Yusuf yake tsaye, ya kalli Yusuf yace " Malam Yusuf, ko zaka iya gayamana yadda akayi ka fara aiki a gidan Alhaji Nasir Daula? "
Yusuf ya ɗanyi shiru yana kallon Barrister Hafiz, Barrister Hafiz ya jinjina masa kai alamar ƙwarin gwiwa.
Yusuf yace "Abokin aikina Abbas, shine yazo ya sameni da maganar ga aikin da ake so inyi, shugabanmu yace a bani umarnin yin wannan bincike, da farko naƙi amsawa, daga baya naga tunda aikinane bazan iya cewa a'a ba, tunda ni na ɗau alƙawarin aiki, Abbas shine ya kaini gidan Alhaji Nasir Daula da kansa, yana zuwar musu gidan a matsayin Sani me yankan farce, kuma yana mutunci dame gadin gidan "
" waye me gadin gidan? " cewar Barrister Hafiz.
Yusuf yace " Isa ne"
"muje kotu na saurarenka"
"Bayan an kaini gurin 'yar gidan Daula, tace min sena saka hannu akan wata takadda kafin in fara aiki da ita, na karɓa na saka, tace min saka hannun da nayi tamkar na saka hannu a contract ɗin mutuwana ne, da farko naji tsoro se ban nuna ba saboda tunda aiki najeyi, bazan janye ba saboda abunda ta faɗa "
Barrister Hafiz ya jinjina kai yace " ko Isa megadi yana gurin nan? "
Isa megadi ya miƙe, aka masa umarni daya fito, ai kuwa ya fito yazo ya tsaya.
Barrister ya kalle shi yace " me zaki iya cewa akan abunda Yusuf ya faɗa "
Isa megadi yace" tabbas lokacin da ake neman direban da ze dinga jan 'yar Alhaji Daula a mota, Sani me yankan farce, wanda se da aka fara shari'a naji sunansa Abbas kuma ɗan sandane, shine ya kawo Yusuf gidan nan, kuma daya kawo shi me gidan yana matuƙar ƙaunarsa saboda haƙurinsa, kuma duk rashin yaddarta ita uwarɗakin nasa tana yadda dashi sosai"
Barrister Hafiz yace "Isa megadi zaka iya komawa"
Kafin Barrister Hafiz ya kuma gabatar da sheda, Barrister Sadik yace yana da tambayoyin da zewa Yusuf, Alƙali ya bashi dama, yaje gaban Yusuf ya tsaya yace "Kamar yadda ka bayyanawa kotu cewa, 'yar gidan Nasir Daula tace maka aiki da ita tamkar signing ne akan contract ɗin mutuwarka, meyasa ka amince kayi aiki da ita, ko duk cikin shirinka ne na saceta"?
"Objection ya megirma me shari'a, Barrister yana ƙoƙarin saka wanda ake zargi yayi confessing ne ko kuma tambayarsa yake?"
Alƙali ya buga guduma yace "Order, Barrister Sadik cigaba da tambayoyinka"
Yusuf yace "Ni ɗan sanda ne, kuma dama rayuwar ɗan sanda na tsakanin rayuwa da mutuwane dan kare rayuwa da dukiyar wasu, shiyasa ban razana na janye ba, saboda aiki nake"
Barrister Sadik yace "kace bincike kaje yi gidan Alhaji Nasir da kuma bawa 'yarsa kariya, wane irin bincike?"
"Kamar yadda Barrister ya faɗa ɗazu, ana kai musu farmaki, saboda dukiyar da yace batasa bace, an bani aikinne dan gano suwaye da kuma bawa Widad kariya"
Barrister Sadik yaga idan ya cigaba da tambayoyin nan, tabbas Yusuf ze ɓallo ruwa, dan haka ya koma ya zauna.
Barrister Khalil ne ya shigo cikin kotun da hanzari, fuskarsa babu annuri idonsa jajawur, ya tsaya yace "ina me neman afuwar kotu, na gaza halartar kotu da wuri, hakan ya biyo bayan neman wata sheda da bata zo hannunmu akan lokaci ba, sunana Barrister Ibrahim Khalil, lawyer me zaman kansa ina cikin tawagar lawyoyi dake bawa wanda ake tuhuma kariya, idan kotu ta bani dama, zan fara gabatar da shedu da hujjoji, amma kafin nan ina son yiwa wanda ake ƙara tambayoyi"
Aka bawa Khalil dama, Khalil yaje gaban