Showing 129001 words to 132000 words out of 225640 words

Chapter 44 - Zaki Book 1 Hausa Novel Complete

kamat balaraba”

“Allah sarki Allah ya jikanshi, ashe Ataa shi ta biyo domin na lura yata ta fiki kyau sosai, bari na leka bangaren Daddynsu na bar shi shi kadai”

Daga haka na ji ficewar Momy faga bq din ni kuma na taso na share ragowar hawaye na fito na zauna kusa da Nana na rumgumeta, cewar Ni kadai na rage sai ita ya taba min zuciya, ban taba tambayar dalilin zuwan mu nan ba, da kuma rashin kowa a nan ba, domin ban tana kawowa rai komai ba, kuma na lura kamar Nana bata damu da hakan ba, sai yanzu ina da bukatar ji domin na lura yan'uwa suna da rana ko da kuwa talakawa ne na tabbatar da ace wani nata yana kusa da ita da bayan ni da Doc Asim be isa ya mata haka ba. Da yare buzanci ma kalleta ina murmushi na ce.

“Nana idan kin kara jin sauki sosai za mu tafi gida can Agadez gurin danginki ko?”

Sai ta girgiza min kai.

“Aa ba zan taba zuwa ba har abada, Babana ya yi fushi da ni, na bashi kunya ba zan iya komawa garin nan ba har abada, sai dai ke kije idan na mutu”

Ban sake cewa komai ba ganin hawaye a idonta, tabbas ba dadi ne ya saka ta baro garin ba, wata kila wanin abun ta aikata ko kuwa korarta yai oho.Da rana Amina ta kawo mana abincin rana jalof din taliya da kifi an saka mata koren wake da wasu abubuwan da na zan iya tantance su ba, sai kamshi take mai ya kwanta gwanin sha'awa. Bayan mun gama ci na shiga bandakin nai wanka daman Nana tun da ta gama karyawa safe tai nata, ina fitowa na dauki rigar dazun na saka n zauna kaina babu dankwali daman na fi sakewa a haka. Can da la'asar sai ga Amina ta sake dawowa, wai na fito ana kirana ban saka komai ba na fito daga ni sai doguwar rigar jikina na biyo bayanta na yi zaton Momy ce take kirana sai na ga wani mutum cikin shiga ta kamala zaune a amman wata kujera hannunsa rike da wata katuwar waya.

“Zauna nan”

Na zauna a empty chair da Amina ta nuna min sai ta wuce ciki, ni kuma na gaishe da mutumun ya amsa min da fuskar far'a, ya soma tambaya inda na tsaya a karatuna na boko daga nan na gane cewar malamin boko ne.

“Aji hudu na tsaya a yakubu mu'azu, ban sake yi ba”

“Kin iya karanta hausa?”

“Eh na iya karanta hausa ko wace iri, da numbobi”

“Ban iya ba”

Sai ya miko min wayar hannunsa ya ce na karanta hausa. Gata ne a rubuce a take na soma karanta ta sai dai ina yi ina gargada wani gurin kuma sai ya gyara min idan na fadi wani abun ba daidai ba sai yayi ta min dariya, bayan na gama ya bani turanci ya ce na karanta sai na kafaranta da hausa ba tare da san ma'anarsa ko fassararsa ba, nan ma ya sha dariyata ni kaina na yi dariyar kaina domin duk turancin da ya nuna min da hausa na ke karanta shi. Muna cikin haka Aliyu ya fito tare da Momy ashe wai yana cikin gidan ni ban ma sani ba. Mutumen ya shiga masa bayani

“Ba laifi tana da kai kuma ta yi kokari sosai, yanzu hausar ce za a dora ta akai sai kuma turancin da zamu fara daga farko domin shi tace bata iya komai a ciki ba”

“To yayi kyau”

Ya fada fuskarsa ba yabo ba fallasa, sannan ya saka hannunsa aljihu ya ciro kudin da ban san ko nawa ba ne ya mikawa mutumen.

“Ga wannan ka hau mota za mu neme ka?”

Karba yai yana godiya ya karbi wayarsa da ke hanuna yai min sallama ni da Momy fuskarsa da murmushi ya nufi gate.

“Be yi ba ba ne?”

Bayan ya wuce Momy ta tambaya.

“No na cika sakewa bana son namiji mai sakewa da mace sosai”

Ya fada yana kallona.

“Ba na ce ki daina fitowa haka ba?”

“To ai hijab din ya yi datti duka kayan sun yi datti”

“Je ki sako Hijab dinki”

“To ba ya wuce ba?”

Na fada ina turo baki. Harara ta yai sai Momy ta ce.

“Ataa yata idan Aliyu ya ce ki yi abu ki rika yi ki daina masa garda kin ji? Je ki saka wata kila rakiyarsa za ki yi”

“Tau”

Tashi nai naje na saka hijab din na dawo, ko da na dawo yana cikin mota ya bude front seat da alama ni yake jira, shiga nai na zauna da gangan na ki rufe motar sai ta ya mika hannunsa ya janyo ganbun ya rufe sannan ya soka taka motar daman tuni aka bude masa gate.Ba mu yi wata lafiya mai nisa ba, muka iso gaban wata katuwar makarantar islamiya, wani irin dadi ne ya lullube na kalleshi da sauri.

“Saka ni za ka yi?”

Sai yai min banza kamar be san da zama a cikin motar ba, ya bude motar ya nufi wani bangare na makarantar ya bar a ciki, be dade ba ya dawo ya bude min murmushi motar da kansa na fito na tsaya a kusa da shi ya wani hade rai irin kar na ga damarsa din nan, wani malamin ne ya zo ta takardu ya ya tambayi sunana da sunan Baba lafiya ta da sauransu sai ya rubuta a form din hannunsa dabya bukaci number waya sai Aliyu ya bada tasa.

“Shikenan yanzu sai uniform za a siya mata da kuma hotonta da za a laka a jiki”

“Ana siyar da uniform din a nan”

“Akwai muma siyarwa dinkaken ma ne”

Be tambayi nawa ba yake ba kawai ya saka hannunsa aljihu ya ciro kudin masu dan dama ya mikawa mutumen.

“A bata uniform din ka rike canjin ka cire kudin form din hoto kuma za muje ayi yanzu, dan Allah ka saka ido akanta bata iya komai ba, tun daga farkon fari za a fara koya mata komai”

“In-Sha-Allah ba ka da matsala, ba ri a dauko mata uniform din”

Komawa yai cikin makarantar ya dauko uniform din cikin wata farar leda ya miko min na karba ina wani irin murna kamar na zuba ruwa a kasa na sha. Sannan na koma cikin motar shi ma Aliyu ya zagayo ya shigo yayi mata key.

“Na gode na gode sosai Allah ya saka maka da alheri”

Be amsa ni ba ko inda na ke be kalla ba, ni kuma ban damu ba farincika ya gama cika zuciyata gaba daya, daga ilslamiyar ya wuce da ni gurin daukar hoto aka dauki hotona aka ba shi, fiye da kudin hoton ya bawa mutumen, abunda na lura da shi idan zai maka alheri ko ya baka hakkinka sai ya ninka maka ko kuma ya baka abunda ya fi yawan nawa, na yi zaton daga nan gidan za mu koma sai ya nufi AGG da ni, ban taba shiga shagon ba tun da nake ganinsa sai dai kawai na bi an wuce amman har bara na yi a gurin shagon lokacin da nake tsananin bukatar kudin nan.
Yana gaba ina binsa a baya sai rabon ido nake ina kallon kayan shagon ina ta kalle kalle da kansa yake zabon kayan ciki, yawanci gowns ne na abaya da riga da skirt na kanti, sai takalmi masu kyau ta ki hudu, sai da ya biya kudin sannan suka saka masa a mota muka fito muka shiga motar ya dauki hanyar wata plaza da ni, wannan karon a motar ya barni ya shiga ciki domin be bude min dan na fito kamar yadda yai min dazun ba, ni kuma na zauna a cikin motar har yayi abunda zai yi ya fito wani na riko masa manyan ledodi.A bayan mota aka saka masa musu sannan ya shigo motar yana cin wani abu mai kamar chocolate kuma ba chocolate ba, ya ci kusan rabi sannan ya miko min sauran sai na karba na saka gefen hijab dina na goge kufan bakinsa sannan na ci, ido ya saka min yana ta min kallon rainin wayo sannan ya tashi motar muka kama hanyar gida ana kiran sallah magariba.
A harabar gidan ya faka motarsa ya bude boot din ni kuma na bude na fito rike da uniform dina zan tafi bq sai na ji ya ce.

“Wa za ki bar wa wadannan kayan?”

Dawowa nai na dauki ledodin na yi zaton cikin falonsu za a shigar masa da su sai na ji ya ce.

“Leda ukun ne na ki biyu Mamanki ne”

Na zaro ido ina bude baki.

“Da gaske da gaske”

“Da karya”

Na fada ba tare da ya kalleni ba ya rufe boot din ya nufi sashen Momy, wani tsalle nai na dire rai na fes, a gaskiya yau Aliyu ya burge ni domin na kura shi ma yana da mutunci kamar Kamal sai dai Kamal ya fishi son mutane da far'a. Nana ma ta yawa sosai da ganin kayan da kuma halin Aliyu daman tun muna asibiti take ta yabonsa tana ganin kirkisa sosai, wannan karon har da cewat tana mamakin yadda hake ga hidima da ni haka. Bayan sallah isha'i Nana ta ce na je na masa godiya kuma na ce ita ma tana masa godiya. Rigar jikin na cire na saka daya daga cikin Egypt abaya da ya siya min na saka na yafa mayafinta sannan na nufi part din rigar sai kyalkyali take ko'ina na jikinta.

Da sallam na tura kofar falon na shiga, sai Momy ta amsa min da far'arta Aliyu yana zaune saman cushion ya hade rai sosai kamar an masa wani abu, ina juyowa sai na Muhseen tsaye yana sakar min murmushi.

“Laaa Ya Muhseen”

“Pretty na”

Ya fada yana kallon yadda rigar ta karbe abun ka da farin mutum ya saka babaken kaya.“Yaushe ka zo?”

“Yanzu nan, jiya na ban ji a waya ba kuma ina da bukatar ganinki shiyasa na zo, ya kike?”

“Lafiya kalau”

Na amsa ina dariya kamar an min wani abu, ni dai har ga Allah ina son mutum mai far'a da dariya kamar Kamal da Muhseen, sai dai Kamal ya fi kwanta min sama da Muhseen din kuwa da kasancewar shi ma yana min far'a sosai, kusan sai na ce duka suna burgeni kuma ina son su.

“Kin yi kyau pretty na rigar ya karbd ki”

Ya fada yana rika rigar nawa ya buda ta tai fadi.

“Eh dazun Aliyu ya siya min ita Nana tace na zo na masa godiya”

Yanayin fuskar Muhseen na ga ta canja sai ya dan wara ido yana zolayata.

“Hop kin daina sake jikinki dai domin na lura ana sake miki da yawa”

“Sake jiki kuma?”

Momy ta tambaya sai ya kalleta

“Yes, lokacin da take Abuja a garden take wanka, a gareji take canja tufafi sai da na mata magana”

Juyowa Aliyu yai ya kalli Muhseen yana lilo da kafarsa wacce dayar ki saman daya.

“Ka ganta kenan? Shiyasa ka ce kana son ta?”

“Idan ma haka din ne ai ban yi illa ba”

Tasowa Aliyu yai daga saman kujerar da yake zaune yana fadin.

“Ataa ba ki da hankali kuma kurciya na damunki, Momy kina ganin abunda na ke fada miki ko? Ya ganta tana wanka ta na canja tufafi kuma shi ne yanzu a tsaye a gabanki har kina amsa dariya? Wallahi baki san ciwon kanki sam”

Muhseen yayi murmushi har zai yi magana sai muka hi Aliyu ya kyalkyale da dariya mai karfi wacce ban taba zaton bakinsa na iya irin wannan dariyar ba.

“Magana ta fito Muhseen kana son Ataa saboda ka ganta a sirara, Wallahi wannan nuna mata rashin daraja ne da raina mata hankali, what a shame lallai kai yaro ne kuma wawan duniya tun da har tsiraicin yake maka sha'awar kallo what a sad”

Yana fadar hakan ya fice yana dariya dariya irin sosai din nan kamar ba ta hankali ba.ALIYU POV.

Duk wata dariya da yake na fuska ne kawai amman ransa cike ya ke da bacin rai da bakin cikin jin cewar Muhseen ya taba ganin Ataa tsirara wani abun yaji marar misaltuwa har yana jin kamar kirjinsa zai rabe biyu, sai kuma ya ji kamar ya danne Muhseen ya cire masa idanuwa. Be san abunda ya kawo shi yau ba ma, gashi yana cewa ba za a tafi da Ataa abuja ba saboda shi da Kamal shi kuma yazo yanzu.
Yana faka motarsa harabar gidan sako na shigowa wayarsa, ganin sunan Rahma yasa shi budewa domin baya cikin mood din saurare kowa a yanzu.

_I'm sorry akan abunda ya faru, Mommy ta yi fushi ne sosai shiyasa amman dan Allah ka yi hakuri, kuma ina neman izininka zan tafi Dubai jibi_

“Really?”

Ya furta bayan ya gama karanta sakon.

“You will regret this Rahma ke da iyayenki”

Ya fada sannan ya bude motar ya fita zuwa cikin gidansa, haka ya kwana a gidan cikin wani irin yanayi na bacin rai tsakanin wanda Rahma tai masa da abunda Muhseen ya fada sai ya rasa wanne ya fi masa zafi. Ko da ya tashi da safe kansa kamar zai tsage sabar bacin ran daya kwana da shi jiya, he feel unsafe sai da yai wanka ya shirya cikin wasu tufafin ya dauki hanyar arkilla tun da farar safiya haske ma be gama bayyana ba. Ko da ya shiga falon babu kowa sai ac da wutar da aka kunna, but he got lucky yau Momy a part din ta tai sallah asuba after Daddy ya tafi masallaci ita kuma ta dawo part dinta tai sallah, daman ta kan yi haka wani lokaci wani lokacin kuma acan take yin sallah ta. Tura kofar dakinta yai ya shiga ba dan ya tabbatar tana ciki ba, idan ma bata ciki shi zai kwanta a nan ne for a while hankali zai fi kwanciya ace yana gidan fiye da yana can dabam. Zaune ya same ta saman carpet karbin a hannunta tana ja. Ita kanta ta yi mamakin ganinsa da safen nan.

“Lafiya dai?”

“Lafiya kalau Momy ina kwana”

“Lafiya Kalau, amman ba lafiya na ka zo da safen nan”

Ya yi shiru na wani lokaci sannan ya ce.

“Momy wai Rahma ta turo min sako zata je Dubai”

Da mugun mamaki Momy ta kalleshi.

“Dubai? Da izinin wa?”

“Wai izini take nema”

“Uhmm Wallahi Rahma nan ta maida wani sholobiyo, daman tun farko kai ka nuna mata fita ba da zininka ba ai, yanzu kuma ganshi ba nan, maganinta kamin ta dawo ka auri wata Wallahi”

“Yes nima abunda na kwana da shi a raina kenan”

“Haka ma za a mata, kuma idan zaka bi nawa Ataa na ke son ka aura wacce ta raina take ganin ba komai ba ce”

Kamar saukar Aradu haka Aliyu ya ji maganar Momy, Ataaa Ataaa Ataaa Ataaa sunanta na ta maimaita kansa a kunnensa, da sauri ya kalli Momy.

“Momy Ataa?”

“Yes”

“Amman..... ”

Sai kuma ya mike tsaye ya saka hannayensa aljihu ya daga kansa sama yana shakar iska kamin ya sauke ya juyo ya kalli Momy.

“Momy seriously?”

“Yes don't you like her?”

“I do, but.....”

Sai murmushi ya subuce masa ya shafa kansa.

“Momy ke kike fada min wannan da kanki? I can't believe this”

Murmushi Momy ta yi.

“Do you love her?”

Shiru yai na wani lokaci yana sauraren yadda zuciyarsa ke mugun bugawa with full farincikin da be daga ina yake sauko masa ba.

“Momy wasa dai kike min?”

“Indai tana son ka da gaske na ke yi”

“Zata so ni mana Momy ai ita bata san so ba, zan koya mata komai Momy trust me”

Ya fada yana dukawa ya kama hannayenta duka biyu ya rike, shi kanshi sai yanzu yake jin cewar son Ataa yake yi, duk wani abun da ya dade yana jinsa akanta sai yanzu kullin ya watse a jikinsa da zuciyarsa, domin tun da ta zo duniyarsa sai yake jin kullum kamar a takure yake.
ZAKI

By Khadeeja Candy

39...

Kamar an diga man kuli a cikin ruwa mai mugun sanyi haka Aliyu yaji jinin zuciyarsa ya taso yayi tsama saboda kalaman Muhseen.

“Kai Pretty wai kin duba madubi yau ko? Gaskiya Allah ya iya hallita”

Cewar Muhseen yana kara kallon yadda uniform din yai mata mugun kyau kasancewarsa Maroon color, ga gashin kanta data sakawa ribbon ya sauko har bayanta gwanin sha'awa. Ko wace kalma ta Muhseen Aliyu hade ta yake da yawun bakinsa, ba kuma iya yawun ne kawai yake hadewa ba har da abunda yake ji yana taso masa yake dannewa, shi kanshi ya san yayi abunda ba zai iya ba, yana tsaye wani na yaba kyau matarsa.

“A a ba mu da madubi ai”

Ataa ta fada tana murmushi.

“Zo na nuna miki kanki a wayana”

Ya zauna a kujerar da ke kusa da shi yana ciro wayar daga aljihunsa na gaba, bata zauna din ba ta juyo ta kalli Aliyu wanda idonsa ke kan wayarsa tunawa da yace ta daina sakewa Muhseen.

“a a bari na je na duba a Mota”

Ya fada sannan ta fara takawa zata wuce Muhseen ya bi bayanta da kallo komai na jikinta motsi yake a cikin uniform din kasancewarta mai tubultubul kuma uniform din ya dan kama jikinta din jiki ga shi bata da komai a ciki, da gangan yai hanzarin kai hannunsa ya kama gashin kanta ya juyo da ita ta rika yatsun hannunta.

“Pretty ina zoben da na baki...?”

Bata amsa shi ba tai saurin fisge hannunta tana kallon Aliyu hankalinta a tashe kamar wacce za ayi ma wani abu.

“Muhseen....!”

Aliyu ya daka masa tsawa a cikin muryar da shi kan shi be san da zamanta ba.

“Karka sake kuskuren yabon kyau Ataa balle ka ce zaka kai dan iskan hannunta ka taba ta, wannan ya zama na karshe ina nufi na karshe....”

Magana Aliyu yake ma Muhseen cikin tsawa yana nuna Muhseen da yatsansa kwayar idonsa gaba daya ta canja ta rine kamar ba shi ne da farin ido ba, shi kan shi Muhseen sai da gabashi ya fadi domin ya razana sosai da yanayin da ya ga Aliyu. Kamar kyalftawar walkiya haka Ataa ta bace bat a cikin falon kamin ta isa Bq har da gudunta, ganin irin tsawar da yai ma Muhseen da yake kanensa kuma dan'uwansa to ita kan ta san nata dukanta zai yi. Da sauri Momy ta fito daga kitchen tana kallonsu, kannensa ma Amina, Siyama da Husna duk sai da suka fito daga dakunansu jin yadda falon gaba daya yake amsa muryar Aliyu.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login