Showing 69001 words to 72000 words out of 225640 words
garin Abuja, maman ki ta saka ki?”
“Aa ni na saka kaina, bata son zuwan nama ma”
“To miyasa kika zo? Kina ganin sha'awar Abuja ne?”
“Mutum ya taba sha'awar abunda be taba gani ba?”
Ya daga kafadunsa.
“Maybe kin san wani idan yana jin labarin gari sai yaji yana sha'awar zuwa wata rana”
“Ban taba sha'awa ba, ban taba tunanin zuwa ba, ni da bani da lokacin fira ma wa zai ba ni labarin Abuja?”
“Kamar ya kina zuwa makaranta ne acan?”
“Aa na yi karatun primary daga bakin class 4 na daina zuwa har yau”
Kallon yai da mamaki.
“Mi ya hana ki zuwa”
“Ba komai”
“Ba komai hakan nan kawai zaki ki zuwa makaranta? Ba ki son karatun ne?”
“Ina so”
Shiru yai ya cigaba da tukin can kuma ya kalleni ina ta wasa da kwalbar turaren daya ba ni ya ce.
“Gashin nan na ki na son gyara kin taba gyara shi?”
“Eh ina wankewa”
“An taba wanke miki a shago?”
“Bari na biya da ke shagon da ake wankewa Ilham sai a wanke miki na ki”
“Da gaske?”
Na fada ina wara ido daman na dade ina sha'awar a wanke min gashi a shago.
“Yes yar fara”
Ya fada yana dariya ni kuma nai murmushi, ban kara ce masa komai ba shi ma be ce min sai dai ina lura da yadda yake ta kallona har muka isa gaban wani katafaren shago mai hotunan mata da gashi irin nawa su da kitso wasu kuma an gyara musu ya sauko har gadon bayansu. Sai da ya fara fita sannan ya zagayo ya bude min motar na sauko ina rike da turare sai ya mika hannunsa ya karba.
“Kawo a aje turare har mu dawo”
Ba musu na mika masa sai ya maida kwalbar cikin mota ya rufe motar sannan na nuna min hanyar shagon da hannu.
“Muje”
Ni ce a gaba shi yana baya har isa bakin kofar shagon, sai ya kai hannu ya bude min kofar na shiga sannan ya shigo shi ma, dukan wadanda suke shagon kabilu ne ba hausawa ba, da yaren turanci yai magana da su sai wata ta zo taja hannuna ta kai ni wani kebantaccen daki mai kamar falo an gyara ko'ina kamar kana gida, kujera ta ja mi na zauna gaban wani katon madubi shi kuma ya zauna a kujerar dake bayana ya dauki magazine yana dubawa. Wani garin tawul ta dauko ta dora min a wuya sannan ta cire dankwalin kaina tana fadin.
“Wow.....”
Har Kamal ya dago ya kalleni ta cikin madubi ni kuma nai murmushi sai shi ma ya mayar min. Sai da ta fara raba kaina gida hudu ta gyara ko wane bangare sannan ta saka na taso daga wannan kujerar na koma gurin wata na ta shafa mai.....
Mun kusan awa daya a shagon sannan aka kammala gyaran gashin, kamar wata ba indiya haka na fito gashin kaina ya kwanta irin yadda na indiyawa yake yi, yana ta sheki ni kaina sai da ya burge balle kuma Kamal da ke ta kallona ba ko kyata ido. Wayarsa ya saka yana ta dauka ta hoto, ita kanta wace ta gyara min gashin sai da ta dauki hoto a wayarta, sannan ya biya kudi muka fito yan matan da ake ma gyaran gashin sai kallon nawa kan suke, domin kowa ya ga nawa gashin yasan cewa nawa ne ba kamar su da ke sakawa fake ba. Wannan karon ma shi ya sake bude min motar na shiga ya rufe sannan ya zagaya ya shiga mazaunin direba ya tashi motar muka hau titi.
“Kina da kyau sosai Mamana”
Ya fada ba tare daya kalleni ba, ni kuma na kalleshi ban ce komai ba ya maida dubana gurin titin.
“Har yanzu baki bani labarin dalilin zuwanki Abuja ba”
“Aiki na zo yi"
Na fada ina shafa gashin kaina da ke burgeni ina jin kamar ba nawa ba ne.
“Mu yan asalin yola ne, fulanin yola ne mu, mahaifina ma'aikacin gobnati ne mai rufin asiri, a hannunsa na taso ina da yayye maza biyu da mace daya ni ne na hudu kuma ima da kanen biyu mata, a unguwar da nake zaune babban yayanmu da Matarsa ne a gidan da kuma Mahaifiyata da kannena sai dai kowa bangarensa dabam, yayana dan majalisa ne a nan Abuja”
Na kalleshi.
“Ka ce min kai talaka ne ashe ba haka ba ne”
“Yes ni talaka ne kamin yanzu, a lokacin da muke yola mun sha wahalar rayuwa, domin mahaifinmu ya rasu a lokacin da muke da bukatarsa, karatu ya so ya lalace sanadin hakan, amman talakawan nan da nake fada min na unguwarmu su suka hada kudi suka komai na makaranta domin suna ganin kimar mahaifina sosai, dattijon arziki haka suke kiranshi, da taimakon da suka min na kawo a inda na ke a yanzu, kin ga ko ai dole na san darajar su”
Yana fadar hakan ya faka motarsa gefen titi ya juyo ya kalleni.
“Fada min ke fa?”
“Ni ba yar kowa ba ce, babana ya rasu ina da kane Lukman shi ma ya rasu, daga ni sai Mamana muka rage”
“Ayyah sorry"
Ya fada cikin yanayin da ke nuna tsantsar tausayinsa a kaina.
“Kika ce ke kika kawo kanki aiki a nan miyasa?”Ban boye masa komai ba face zancen cire kodar mahaifiyata shi ma saboda ina tsoron kar Mama Fulani ta ji ne ta koreni dan sanan ba zata yarda cewar danta ya cirewa mahaifiyata koda ba, sai nai ma Kamal wata karyar da cewar ulcer ce take damun mahaifiyata na ke nema mata kudin magani, tsantsar tausayin da na gani a idon Kamal da fuskarsa ban taba ganinta a fuskar wani mai ganin tausayina kamar haka ba. Da kansa y ciro tissue paper ta gaban motarsa ya miko min.
“Share hawayenki”
Na karba na share hawayen da suka ki su tsaya min saboda tuna da irin rayuwar da na baro da kuma kalubalen da ke gabana.
“Kin yi kokari sosai Ataa kin zama jaruma, aiki a titi kula da mahaifiya ba abu ne mai sauki ba ko a gurin babba balle ke da ba zaki wuce 16 to 17 years ba, amman ina yan uwanki ba ki da kowa wanda zai iya kula da ku bayan rasuwar mahaifinku? Ya kamata ace sun kula da mulallinku ba su bar ku kuna ta bara ba”
“Ban san inda kowa nawa yake ba, mahaifina be taba firar kowa da ni ba, haka ma Mamana bata taba fada min wani abu daya shafi danginta ko dangin mahaifina ba, iyakar abunda na sani suna nijar”
Ajiyar zuciya ya sauke yana ta kallona sannan ya tashi motar ya hau titi muka cigaba da tafiyar, be sake ce min komai ba sai kallona yake har muka isa gida, a bakin gate din su Mama Fulani ya faka motarsa ya mika hannunsa baya ya dauko ledodin da aka saka masa a bayan mota ya miko min.
“Ungo wannan na ki ne”
Kin karba nai.
“Aa Mama Fulani zata iya min fada idan ta gani?”
“Ai ni na baki kuma yanzu da na aje motata a gida zan shigo cikin gidan a nan zan ci abinci rana”
Na saka hannu biyu na karba, sai ya saka hannunsa aljihu yan bandir din dari biyu ya miko min.
“Ungo wannan ki aje mana, za mu fara tarawa kudin maganin Mama”
Kallonsa nai baki a sake sai nai saurin girgiza masa kai.
“Aa ba zan karba kudi ba, idan Mama Fulani ta gani dukana za tai kuma aikin da nake saboda na tara kudin na ke za su iya idan na tara na wata uku”
“Ba za ki bari ta gani ba ai, boyewa za mu yi ki rika sakawa cikin kayanki, idan mun tara da yawa idan za ki je ganin gida sai a kaita asibitin ko?”
“Mama...”
“Ya isa, komai dai Mama Fulani zan mata magana ta daina takura miki”
“Aa dan Allah ka rufa min asiri wallahi zata iya dukana ma”
“To karba ki aje, karki bari ta gani sai ki boye abun ki ai”
Babu yadda na iya bayan karba domin ni ma kaina na san ina da bukatar kudin, dan haka na saka hannu biyu na karba cikin tsoro da firgice har na manta ban masa godiya ba, shi ya fara fita cikin motar ya zagaya ya bude min ya fito sannan ya rufe motar, wani abun da ban sani ba ashe Aliyu yana tsaye bakin gate din yana kallonmu amman ni ban lura da shi ba har sai da na ga Kamal yai murmushi ya daga masa hannu.
“Sannu dai Aliyu”
Sannan na koma cikin motar yaja abarsa zuwa gaban gate din gidansu ya danna horn aka bude masa ya shige ciki. Ina tsaye a inda ya aje ni ina kallon Aliyu da ke tsaye daf da gate din yana watso min wani kallo mai ban tsoro fuskarsa a hade kamar bakin hadari, tsakanin jiya da yau Allah ya saka min tsoronsa duk wani fitsara da nake jin zan iya masa sai na ji yai min kwarjini har na gagara karasa gurin gate din na shiga shi kuma yai tsaye a gurin yana ta kallona kamar daman can dan kallo kawai aka halliccesa. Ganin ba zan zo ba yasa ya juya ya koma cikin gidan, yana wani irin taku na masu karfi da kuzari. Sai na tabbatar ya shige ciki sannan na nufi gate din na tura kofar na shiga, sai na ganshi tsaye da alama ni yake jiran na shigo ni kuma nai tsaye a gurin dayan hannuna da kudin dayan kuma da ledodin.
ALIYU POV.
Tun ya bar gidan Mama Fulani ya saka samun sukuni da walwala a yadda yake, zuciyarsa na ta raya masa Muhseen zai iya cutar da Ataa, ya san Muhseen ba dan iska ba ne, amman ai ba a shaidun mutum a yanzu, kuma yadda Ataa take da kyau zai iya rudarsa ya jefata cikin wani halin, wanda yake da tabbacin shine silar komai tun da shi ne silar cire kodar mahaifiyarta har ta zo aiki a gidan, idan kuma wani abun ya same ta ai duk shine sila, dan haka ba zai bari rayuwarta ta lalace ba, ba zai taba yarda ta rika kebewa daga ita sai Muhseen ba, daman can tsakanin shi da Muhseen basu taba shan inuwa daya ba, saboda Muhseen yana jin haushin yadda yake da jin da nuna isa da dakama, shi kuma yana jin haushin yadda Muhseen yake da sakewa da mutane. Daga gidan Mama Fulani ya nufo gidansa cikin bacin rai, duk yadda yai kokarin ya kawar kar Rahma ta fahimci yana cikin damuwa sai ya kasa, in every minute sai ya ji kamar wani abun ne zai samu Ataa duk kuwa da yasan be barta mugun guri ba amman ya kasa natsuwa da zamanta a gidan tsakanin jiya zuwa yau.
Rahma kallonsa take har ya shigo cikin falon ya karaso kusa da ita ya zauna yana matsa kansa alamar yana masa ciwo.
“Lafiya dai, na dauka sai nine zaka dawo gida idan mun ga Doc Perry?”
Kissing dinta yai sannan na kwantar da kansa jikin kujerar ya lumshe ido na wani lokacin sai kuma ya ciro wayarsa yai danne danne ya tura mata. A take sakon ya shigo wayarta da sauri ta dauki wayar dake gefenta ta duba.
“Za mu iya bari zancen Doc Perry for now? Bana son zuwa gurinsa”
Kallonsa tai bayan ta gama karanta sakon.
“But why? Wata kila ma mafita ce ta zo mana, waya sani ko waraka ce”
Dagowa yai ya zauna daidai yana kallonta.
“Rahma akwai abunda ban taba fada miki ba, ban so wannan maganar ta fito daga bakina ba, amman ban san iya lokacin da zan yi ta aje ta ba”
Kara matsawa tai kusa da shi da maida hankalinta gurinsa tana kallonsa kunnuwanta cike da kwadayin jin ko mienene daman yau ta fahimci yana cikin damuwa.
“Minene Aliyu akwai wata matsala ne? Fada min”
Wani dogon numfashi yaja ya sauke ya shafa fuskarsa cikin yanayin da ke nuna yana cikin damuwa, daman kuma a cikinta yake.
“Rahma ban sani ba ko zaki fahimta, ban san yadda za ki kalli abun ba, kuma ban san yadda za ki kalleni ba”
Saurin kama hannunsa tai.
“Fada min kawai Aliyu minene matsalar?”
“Rahma duka tsawon lokacin da muka dauka matsalar daga ni ne..”
Da sauri ta rufe bakinta sai kuma ta girgiza masa kai hawaye na cika idonta.
“Ba daga kai bane Aliyu sun ce ba mu da matsalar komai ba daga kowa ba ne, suna cewa za mu iya haihuwa a duk lokacin da Allah ya kaddara”
“Na boye miki ne saboda bana son ki damu, amman maganar gaskiya matsalar daga ni ne, a duk inda muka je ina sakawa likitocin su ce mu duka ne bama da matsala amman serious matsalar daga ni ne”
“Aliyu ba haka ba ne... ”
Ya rika fuskarta.
“Haka ne, kin san ba zan boye miki komai ba, ba zan miki karya ba, be kamata na kyale ki ki yi ta wahala akan abunda daga ni ne ba, na san idan muka je gurin Doc Perry dole zai fadi gaskiya domin shi baya karya”
“Duka shekarun nan da muka dauka da gaske matsalar daga kai ne? Ko kuma daga ni ne kake boye min?”
“Daga ni ne”
Hawaye ne ya sauko mata sai ta kwantar da kanta jikinsa.
“Miye amfanin fada min a yanzu Aliyu? Miyasa ba ka cigaba da boyen sirrin ba?”
“Saboda bana son ki yi ta wahalar da kanki akan abunda na san ni ne silarsa”
Rumgume shi tai ta fashe da kuka.
“Ba amfanin bayyanawa Aliyu, kai na ke so ba abunda ban gani ba, jin wannan kuma ba zai hana mu cigaba da neman haihuwar ba, wata kila gaba mu dace ba mu san inda rabo yake ba, da matsalar daga kai ne wata kila zan mu iya dacewa ka samu waraka”
Shafa kanta yai yana kara janta a kirjinsa ita kuma ta fashe da kuka mai tsanani har ya rasa ta ita zai fara rarrashinta. A haka suka kwana tana ta kuka, wanda yake tunanin wata kila da yace matsalar daga ita ne wata kila ma ba zata damu kamar yadda ta damu haka ba.“Kamal dai soja abokinka?”
Nasir ya fada cikin tsananin mamaki, Aliyu be ce masa komai ba, daman kuma ya san ba zai amsa basa ba, sai dai tunda yaji yai shiru ya san cewar Kamal din ne.
“Ina ya hadu da ita?”
Nasir ya sake tambaya, sai Aliyu ya fito daga gurin ya nufi kofa rai a bace, cikin sauri Nasir ya ce
“Aliyu ina za aka je?”
“Na zuba musu ido su lalata mata rayuwa?”
“Kana da tabbacin bata nata rayuwa za su yi? Daga Kamal har Muhseen ba irin samarin nan ba ne”
“Bana iya shaidar kowa sai kaina, idan ban taka musu burkiba lalata mata rayuwa za su yi, akan mi zai dauke ta ya fita da ita? Waya bashi izinin ma?”
“Ai ba yau aka saba ba, dan mace ta kebe da wanda ba muharraminta ba ba wani abun ba ne, naga gidanka ma namiji ne yake muku girki ya gyara gidan”
“Nasir baka da hankali kai ma, Rahma ai babba ce ta san ciwon kanta, ba zata bari wani ya yaudareta ba, wannan kuma karamar yarinya ce tunaninta be kai can ba”
Yana fadar hakan ya saka katinsa kofar ta bude masa ta fice. Nasir ya bishi da kallo yana murmushi.
“Aliyu kenan, at least dai yarinyar nan ta sa ka fara motsi kamar na miji, sai yanzu kasan da muharramin?”
Ya fada yana cigaba da murmushin tare da zaunawa saman kujera ya cigaba da aikinsa.
Kai tsaye gida ya nufa gudu yake amman yana jin tafiyar ta masa nisa yau, a kada horn daya yake danna amman daya bisa bakin gate din sai da ya danna horn ya fi hudu a lokaci daya, har mai gadi sai da ya ji tsoro yai tunanin ko wani abun ne ya faru. Daf da kofar falon ya faka motarsa ya fito cikin zafin ran da be san ta ina yake fito masa ba ya shiga cikin falon ba ko sallama, Rukaiya ya samu kwance a kujerar tana lasar waya tana dariya da alama chat din ya mata dadi.
“Ke ina Ataa”
A firgice ta tashi zaune domin hankalinta yana kan wayar bata ma san da shigowarsa ba.
“Na'am tana, tare muka fita shopping shine sai Kamal ya ce na bashi aron ta ta taya shi shopping idan suka gama zai kawo ta gida”
“You're very stupid”
Ya fada yana kara matsawa kusa da ita cikin wani irin yanayin bacin rai marar misaltuwa, tana ganin hakan ta tashi da gudu ta nufi upstairs tana kiran sunan Mama Fulani, ta san baya dukansu ko ba su ba abu ne mai wahala ya saka hannunsa ya daki mace amman a yadda ta ga bacin rai a fuskarsa a yau ta san komai zai iya faruwa. Da sauri Mama Fulani ta fito daga dakinta dankwalinta a hannu yana tambayar ba'asi. Cikin kuka Rukaiya ke fada mata abunda ya faru sai ta nufi downstairs tana kallon Aliyu tare da fadin.
“Ta fada min ai, Kamal ne ya ce a ara masa ita”
“Ya za ara masa ita kamar wata sutura, idan wani abun ya same ta fa? And you.... ”
Ya fada yana nuna Rukaiya sai kuma ya juya ya fice sai huci yake kamar wanda yai gudun ceton rai. Mama Fulani ta saki baki tana kallon ikon Allah.
“Wannan yarinyar ta zama fitini ta zo ta koma garinsu ba zata zauna a gidan nan ba, gaba daya Aliyu ya canja ganin yarinyar nan, shi da babu ruwansa da kula da mace? Ji abunda yake?”
“Ba sai an koreta ba Mama, Wallahi kamaninta za mu canja, kyau ne yake rudarsu”
Maryam ta fada daga can upstairs din da take tsaye.
Gate din Aliyu ya nufo ya tsaya yana ta jin kamar ya kira Kamal a waya sai kuma wata zuciyar ta hana shi, yana tsaye a gurin sai ga Motar Kamal ta karyo kwanar yana ta kallonsa har ya karaso kusa da su sai dai ba sosai ba, ya faka motar, sai kuma yaga yana magana da Ataa a cikin motar baya iya jin abunda yake cewa, amman wani irin abun yake ji yana masa yawo a cikin jinin, ji yake kamar ana tafasa hanjin cikinsa komai na jikinsa rawa yake har gumi ke karyo masa a take idonsa suka canja kala, bacin rai ya bayyana karara a fuskarsa, wani abu yaji