Showing 33001 words to 36000 words out of 225640 words

Chapter 12 - Zaki Book 1 Hausa Novel Complete

matar nan da na ke yi ma aikin yar mai kangon gidancan ne wanda ya kore mu, ina ganin gaba daya danginsu basa da mutumci ko kadan”

Na fada cikin muryar da ke Nun a gajiye na ke ga kuma yunwa da na ke ji rabon da na saka wani abu a cikina tun karin safe da na sha koko da kosai. Sama-sama mu kai fira da Nana ta nuna min rashin jindadinta na dadewar da nai a can sannan muka kwanta ni da ita.
   Yau ma kamar jiya na tashi da wuri saboda matar nan ta fada min na rika zuwa tun karfe bakwai na safe, na san idan na tsaba lokaci wani abu zai iya biyo baya, waina na siyowa Nana ta karya sannan na fito na wanke kwanon da ta ci na maida na janyo ruwan rijiya na yi wanka na saka doguwar rigata ta atamfata kodaddiya, ban damu da saka dankwali ba, na fita waje na daddaka bakin gawayin na shafa a fuskata, na saka Hijab dina na fito na leda dakin Maman su Farida na gaisheta sannan na saki labulen dakin har na kama hanyar fita sai ga Farida ta fito sanye da uniform din makaranta tana cewa na tsaya mata.

“Har kin shirya zuwa aikin tun da safe haka?”

“Wallahi matar da na ke aiki gidan ta ne bata da mutunci ko kadan, tace na rika zuwa bakwai kin ga idan na tsaba zata iya korata gaba daya”

“Gaskiya kan bata da mutunci, tun da har zata rike ki ki kai karfe daya na dare sannan ki dawo, ni wallahi da za ki biye ni da kin yarda maman Salma ta sama miki aiki a Abuja, acan take samawa mutane kuma Wallahi albashi mai tsoka”

“Kai anya Farida zan iya zuwa har Abuja? Kin ga Nana ai bata da wanda zai kula da ita sai ni”

“Amman ai dan neman lafiyarta da abincin ta za ki yi, kuma idan ya wadace ku ya kamata ki dauke ta kuje har garinku ki nemi danginku, zama a nan babu kowa a tare da ku ba zai amfana muku komai ba”

“Nima ina tunanin haka, amman na fi son sai Nana ta samu lafiya tukuna”

“Allah ya bata lafiya, nawa ne suka dauke ki aikin?”

“8k ne”

“8k mi zai miki? Ai wannan kudin zai iya karewa a abinci kawai, gaskiya kara ma Abuja nan ance can fa irin manyan gidajen nan har 30k 50k ana bawa mutum, kin ga da kin hada na wata uku ai ya isashe ki”

“Da gaske Farida”

Na tambaya cike da kwadayin tabbatar da zancen nata.

“Wallahi haka Maman Salma ta ce min”

“Ai ba zuwan ba, kin ga dama ace Lukman yana da rai dazan samu sauki wanda zai kula min da Nana amman yanzu bata da kowa ai sai ni, ita kanta ba zata yarda na tafi ba”

“Gaskiya haka ne, amman indai ina nan ni kaina ai zan iya kula da Nana kin sani, ko da ba zan cire mata kewarki ba zan rage mata shi, ko ba zuwa aiki ba ai dole wata rana za ki yi aure ki tafi ki barta, ko da yaki kin ki bari ma aga fuskar na ki kullum sai boyo kike”

Na yi murmushi ina kallonta a yayinda muka kawo a hanyar da za mu rabu.

“Farida kenan, ni ban taba kawo wa kaina tunanin aure ba, ban taba lissafa kaina a cikin matan da za a iya aure ba”

“Saboda?”

Ta tambaya cike da mamaki. Sai na sake yin murmushi a karo na biyu na ce.

“Ba ni wannan lokacin da zan tsaya na yi fira da wani namiji ba, kullum tunanina ina abinci zai shigo, yanzu kuma tunani ina kudi za su shigo na nemawa Nana lafiya, bayan haka maza basa son yarinyar da bata da arziki a gidansu, sun fi son aure yar masu kudi ko mai rufin asibiti, amman irina idan aka ce za amin aure na san daga ni sai tabarma za a kaini, wanda na san hakan zai iya janyo min wulakanci da kankanci a gurin mijin da yan'uwansa”

Kallon hawayen da suka cika idona ta tsaya yi sai ta rumgume itama idonta cike da kwalla.

“Za ki yi aure kawata, In-Sha-Allah za ki auri mutumen da zai dauki dawainiyarki har da ta Nana ma, na saka ki gaban mota yai ta yawo da ke a garin nan”

Na sake ta ina yar dariyar zancenta.

“Farida kenan, wa zai yi mace irina haka? Mace da batai boko ba, bata waye ba, bata iya komai ba sai bara da roko a titi? Babu wanda zai so auren makaskanciya”

“Ataa karki yanke kauna daga rahamar Allah, dan jarrabe ki a haka ba shi yake nufin ba za ki samu jindadi a gaba ba”

“Na sani, kawai ina duba yanayin rayuwar ne, duniyar ta canja ba kamar da ba ne, ke dai ki tafi makaranta kar ki yi latti”

Daga haka muka rabu ita ta wuce makaranta ni kuma na kama hanyar zuwa gurin aikina, ina ta kwadayin zuwa makaranta amman ba hali, lallai karatu da samun wanda zai tsaya maka ka yi karatun gata ne.
Ina tafe ina ta sake sake na har na isa, yau kan ni kaina na san na yi rana zuwa domin a kafa na zo kamar yadda a jiya din ma na dawo a kafa duk kuwa da irin tazarar da ke tsakanin unguwar mu da ta su. Sai da nai knocked gate din sau biyu sannan aka saka bude min gate din na gaishe shi kamar yadda na yi jiya sannan doshi cikin gidan, na yi mamakin tararda kofar falon abude wata kila wani dalilin ne ya saka suka bude kofar. Ni dai na shiga da sallamata duk da nasan ba za a amsa min ba, haka kuwa akai domin mai gidan nan na hakince saman cushion amman be amsa min ba duk da idonsa na kaina har na karasa tsakiyar falon na gaishe shi nan ma be ce min komai ba. Ban damuwa ba, domin a tsakanin jiya da shekaranjiya kawai na fara sabawa da halinsa da dabi'unsa, matarsa ta fda min baya son yawan kallo, sai dai na lura shi din yana da kure mutum da ido har ka soma tsarguwa sai kuma ace wai kai ba zaka kalleshi ba, lallai masu kudin nan akwai su da rashin adalci da takura rayuwa. Abu na biyu na lura baya son yawan magana kuma yana da kyama sosai fiye da matarsa, ga kamshi a duk inda ya wulga ko ya zauna, kamshin turarensa ne ke yiwa mutum sallama tun gabanin shi yai maka, akwai kwarjini sosai idan kana kallonsa, haibarsa tana fitarta da siffar zatinsa da ainahin kyauwunsa, ban taba ganin murmushinsa ba, a tunani murmushi kamar ba zai yi ma fuskarsa kyau ba, duk kuwa da kasancewar yana cikin sunnar Manzo na, sai dai nana jin wannan miskilin ya ta6a ďa66aka sunnarsa ta murmushi balle kuma har ta kai shi ga yin dariya.
Gurin da na dauki tsitsiya jiya na nufa na dauka tare da mopper na nufi kitchen, can na ke ra'ayin na fara gyarawa tun da na ga shi yana zaune a falon, waya sani ita ko bata tashi bachi ba, balle na gyara bedrooms. Ina cikin aikina na ji tsayarwar mota a harabar gidan, sannan na ji sallama da muryar da na ke kyautata zaton kamar na san mai ita, sai da na gyara kitchen din tsaf sannan na riko tsintsinyar ya fito daga kitchen da zimmar gyara dinning area da falon idan magajin izzar ya tashi.
Arba idanuwa sukai da mummuna mutum wanda zan iya kiransa da bakar jaddara, da bana son na sake saka ta a idona har a bada, Doc Asim ne sanye da suit ya dora labcoat sama yana zaune akan kujerar da ke fuskantar wacce Rahma take zaune ita da mijinta...



_____________________

Page biyu ya rage mana mu gama free pages In-Sha-Allah. if you want to subscribe pay 300 to 0314795884 Abubakar Hadiza Gt Bank. sai ku turo shaidar biyan wato screenshot ta wannan number 08036126660, ko kuma katin mtn na 300 ga marasa account ta wannan number 08036126660. yan nijar za ku tura 500fc na line Orange ko Airtel ta number nan +22790165991 sai ku min magana ta wannan number 08036126660 Za'a saka ku Group.


Thanks 🙏🏻
Ku ziyarci YouTube channel dina, ku danna min subscribe kuma kui sharing. 👉https://www.youtube.com/channel/UCpAkml0pIh6MUnzt9nLh_qQ


*Z A K I*

By Khadeeja Candy


1️⃣4️⃣

Bana bukatar na tambaye abunda ya kawo shi gidan, kasancewarsa likita, da kuma yanayin da naga Rahma na tabbatar bata jindadi, sai dai ina tabbacin ba su san ko waye Doc Asim ba, shiyasa har suka kira shi har cikin gidansu, akwai yiyiwar ya sake samun damar sake cutarsu kamar yadda ya cutar da ni. Kallonsa kawai da na ke ina jin kamar naje na shakeshi ya mutu.

“Ke lafiya kika tsaya kallon mutane ba za kije ki yi aikin ba?”

Rahma ta daka tsawar data saka ni dawowa hayyacina. Sai mijinta yai saurin rike hannunta yana alama da tai shiru kar ta wahalar da kanta gurin magana.

“Karku yarda da wannan mutumen Wallahi azzalumi ne macuci, mugu wanda ba zai taba gamawa lafiya ba”

Da sauri Doc Asim ya dago yana kallon inda nake tsaye da mugun mamaki, da alama sai yanzu ya san da tsayen da nai jikin kofar.

“Wacece wannan?”

Ya tambaya yana kallon Mai gidan da ke kallona shi da matarsa.

“Ba ka gane ni ba?”

Na fada kana na saki tsintsiyar hannuna na juya na koma kitchen din na cire Hijabina abun ka da marar dankwali sai gashi na sauko har gadon bayana, na zuba omon da ke gurin na wanke bakin fuskata na juyo na fito a fusace na karasa har kusa da inda yake zauna na nuna masa fuskata.

“Ka ganene yanzu? Bayan ni wace yarinyar ka cuta? Bayan ni wace macen ka sani mai kama da ni?”

Miyewa yai tsaye ya wanke min fuska da mari.

“Ba ki da hankali ke kin taba ganina ne?”

Tasss na mayar masa da martanin marin da yai min cikin zafin rai, duk da kasancewar ya girme ni a shekaru da jiki.

“Na mare ka da hujja sai ka samu damar sake saka yan sanda su kulle ni a cell kamar yadda ka sa aka min saboda ina talaka”

Yadda muryata take fita kadai ta isa ta karantar da kowa irin daci da dafin bakincikin da ke raina, ga wasu zafafan hawaye da suke sauko min, ina yi ma Doc Asim wani irin kallo mai guba. Mamaki ya hana shi motsi sai sakin baki da yai yana kallona, Rahma ce ta mike tsaye.

“Ke ashe baki da hankali ba ki da tarbiya? Za ki daga hannu ki mari babban mutum mai daraja kamar Doc Asim? Kina yar talaka?”

“Ba yin kaina ba ne talaucin, ke ma da Allah ya zabi a gidan masu arziki ba yin kanki ba ne, ba wata gwaninta kikai wa Allah ba ya zabe ki ya bar ni, saboda kawai ina talaka ba shi yake nufin ni ba mutum ba ce, a gurin ki Doc Asim yake mai daraja amman a gurina konanniyar ashanar bola ta fi shi, zan fi jindadin sunan mutuwa fiye da sunan wannan azzalumin, ganin bakin duhun zai fi min ganin wannan mutumen”

Na fada ina nuna shi da yatsana, mamaki ya cika Rahma, mijinta kuwa kallona kawai yake sai kuma ya kalli Doc Asim kamar mai son tantance abu. Doc Asim ya jinjina kai yana kallona yai kwafa.

“Ni kika mara? Sai kin yabawa aya zakinta, ni ban sanki ba ban san inda kika fito ba amman sai na nuna miki ko wanene ni”

“Babu abunda zaka nuna wanda ban san shi ba, na sanka na san zalincika tun har ka iya cire kodar mahaifiyata ba tare da saninta ba, saboda kawai ka maida ni zahila marar galihu, ka sa na saka hannu kai mata aiki ka cire mata koda, kuma kasa aka kulleni a gidan yan sanda saboda na nemi hakkin mahaifiyata, to wane zalinci zaka nuna min da ya wuce wannan? Idan kashe ni kaka son yi, to mutum baya mutuwa biyu, domin ni na dade da mutuwa tun daga lokacin da kasa mahaifiyata ta rasa lafiyarta, sanadin haka na rasa kanena, to me zaka min yanzu? Duk abunda kake jin zaka iya yi kaje kai, ba a duniya za a tabbata ba, akwai kiyamar Allah zata tsaya, kuma ni da kai za ku amsa ko wace tambaya daga Ubangiji...”

Na karasa ina fashewa da kuka tare da juyawa da zimmar zuwa na dauki tsintsiyar na cigaba da aikina, sai naji muryar mijin matar nan yana wata irin magana mai rikitarwa.

“Kardar kodar da aka dasawa Rahma take magana....?”

Juyowa nai idona na hawaye na nuna Rahma.

“Kodar Nana ka sakawa wannan matar? Matar da mahaifinta ya koremu a kangon gidansa saboda mun taba a gidan? Matar da mahaifinta be san daraja talaka ba? Matar da mahaifinta yasa a ka wulakanta mu? Ita ka sakawa kodar talaka? Talakar ma wacce ya wulakanta? Ka cuce ni ka cuci nana Allah ya isa tsakanina da kai, da kai da duk wanda yasa kuka aikata min wannan aikin ba za ku ga da kyau ba, Wallahi Allah ba zai barku ba”

Na fada cikin daga murya iya kar karfina, sam na manta da a gidan wani mai kudi nake, yau duk wani tsoro da fargabar gudun laifi ya fita a raina, daga Rahma har mijinta da Doc Asim yau kananan mutane na ke kallonsu kuma azzalumai.

“Uban waye yace ki siyar? Akan mi za ki rika fada mana magana son ranki cikin gida? Ubana sa'arki ne da zaki rika saka ko a maganar ki?”

Rahma ce ke wannan maganar tana matsowa kusa da ni, har ta ka hannu zata mare ni sai mijinta yai saurin rike duka hannayenta ya matsar da ita jikinsa yadda ba zata iya ko da kwakwaran motsi ba.

“Talauci ba hauka ba ne Rahma, kuma ba kaskanci ba ne, jarabawa ce daga Ubangiji, ba kuma zan sake yarda marar sanin darajar dan adam irinki wacce ta more da kodar mahaifiyata ta sake wulakanta ni ba, kin ci riba da ni tun da nayi aikin kwana biyu a karkashin ki, amman ba za a koma ba, ya zama na karshe, sai dai ki wulakanta wata amman ba ni ba, kuma tun da har kuka zalinmu lafiyar nan da bata yi amfani komai a jikinki ba”

Ina kawai nan na nufi kitchen din a fusacw na dauki Hijab dina na saka na fito fuuuu na fice daga gidan kamar iska. Kan kace kwabo har na kai gate na bude na fita raina na min mugun zafi zuciyata na ciwo sosai. A rayuwata ban taba ganin mutane masu son kai da tsantsan zalinci kamar likitan nan da mutanen nan ba, babban bakincikina sun ci riba da ni na aikin da nai a karkashinsu, wanda hakan ya fi komai yi min ciwo.
Tun da na kama hanyar gida sai na nemi kukan zuciyata da na ido na rasa, wani karsashin da karfin zuciya dana ruhi suka rufe ni, na jaddawa kaina nemawa Nana lafiyata ta rayu ko dan bakincikin masu son ganin bayanta, a yau na gane ba kuka na ke bukata a yanzu ba, lokacin kuka da bakincikin abunda ya faru a baya ya kare, wannan lokacin na fuskartar gaba ne da inganta rayuwata da ta Nana, na yarda abunda ya tafi baya dawowa amman abunda be zai zo za a iya tarbarsa gabannin ya zo, zan jure ko wane kalar wulakanci da cin zafi daga duk wanda zai iya zama dalilin samun lafiyar Nana.
A kullum idan zanje gida ina zuwa da kasala da jin gajiyar tafiyar, amman a yau na isa gida da karfi kamar daman can ban yi tafiyar ba, ban yarda Nana ta fahimci komai ba, na shiga dakinta na zauna ina ta kokarin yin far'ar da take ta zo min.

“Lafiya kika dawo da wuri haka Ataa?”

“Nana sun koreni daga aikin”

“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u, sun kore ki kuma? Me kikai? Mun shiga uku”

“Ba mu shiga uku ba, kuma da yardar Allah ba za mu sake shiga uku ba, ina tunanin ma kamar wata hanyar zata sake bude mana?”

“Kamar ya? Yanzu ina za ki sake samun wani aikin”

“Farida ta fada min cewar Maman Samawa tana samawa mutane aiki a abuja, kuma a can ana biyan kusan 30k ko sama da haka, kin ga cikin wata biyu ko uku na hada kudin maganinki”

“Aa ni ba zan yarda kije can nesa ba, ban san iya abunda zai iya samunki ba, kuma nan wa zai kula da ni idan ki ka tafi?”

“Farida ta min alkwarin kula da ke, idan har za ki iya hakurin ciwon nan na ki zauna asibiti na tsawon wata biyu, zaki iya hankurin rashin ganina na wata daya, idan na samu lokaci sai na zo na ganki ni dai amincewar ki na ke bukataka kamin nai ma maman salma magana, ina son lafiyarki Nana, sai da lafiyarki zan iya neman dangina, hankalina kuma ya kwanta, dan Allah ki amince Nana”

Na fada ina kama hannayensa sai naga yanayinta da fuskarta sun canja.

“Ko daga nan zuwa wani gurin za ki je, ina jin tsoro Ataa sai naga kamar ba za ki dawo ba, bana son ki zo yi ta wahala da gawa waya sani ko ba zan kai wani lokacin ba”

“Da ba zaki kai wani lokacin ba, da baki rayuwa bayan wannan lokacin da akai miki tiyata ba, kuma babu wanda yasan rayuwa da mutuwar wani sai Allah, kina karya min guiya, ki rika nuna min cewar zamu rayu ni da ke ko da mu kai muka rage a duniya, dan Allah Nana ki barni nai wannan jihadin, ki bar ni na samun wannan faricikin da ladar”

Magangannun nai ta mata ina lurar da ita har na samu ta aminta duk da kasancewar ba ta so haka ba. Bayan sallah azahar na ja Farida muka kama hanyar gidan maman salma da shiga mu kai sallama muka gaisheta, sannan Farida ta koro mata da bayanin da ke tafe da mu, wani abun mamaki da jindadi sai tai murna da hakan har take labarta mana cewar daman

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login