Showing 177001 words to 180000 words out of 225640 words
hankalin kowa yana kaina, cikin har da Mama Fulani da Maryam da Rukaiya da Ammy da yayanta da ban san lokacin da suka shigo ba.
“Waya fada miki cewar Mai Martaba shine kakanki? Taya za mu yarda da ke?”
Dayan ya tambaya da yaren buzanci.
“Ita ta fada min, kuma na ga kamaninta a fuskarsa, idan kuma kana musu ne zan iya kai ku har inda Nana take”
“Asma'u.....ta....na...ra.... ye?”
Wannan karon Mai Martaba ne da kansa ya tambaya maganar tana fitowa da dai daya daga bakinsa cike da kasaita da izza irin ta manyan sarakuna.
“Tana raye amman bakincikin rashinka da duka danginta ya dade da kasheta, kullum mafarkina ni da ita a ina zamu ganka, ta wace hanya zan sadu da kai? Mai Martaba ba ni da kowa sai Nana aka Nana kuma vata da kowa sai kai, ban sanka ba ban taba ganinka a ido ba amman ta kwadaita min kaunarka da son ka da kuma son rayuwa da kai, kullum kukana a kanka mafarkina ni da Nana na ka ne”
Lumshe ido yai ya hade ya sauke ajiyar zuciya a hankali.
“Ki daina magana haka Mai Martaba baya son yawan magana, kuma ya kai matsayin da ba komai ake fada masa kai tsaye ba”
Daya daga cikin samarin ya fada. Sai ya bude ido ya daga masa hannu.
“Barta ta fadi iya abunda zai mata dadi, ita ma jika ce kamar kai, ita din jinin Asma'u ce Asma'u kuma jini na ce, jinina kuma na duka iyalaina ne”
Duka da yaren buzanci mukai wannan maganar daga Mai Martaba har ni har jikansa na sa. Wani irin dadi ne ya lullube ni jin yadda ya kira ni jikarsa jininsa kai tsaye ba tare da tantama ba, ba kuma tare da kyama ba. Murmushi nai na sake rumgume kafafuwana ina jin wani irin sanyi da Rahama irin ta kaka da jikasa. A take na ji amai na cika min baki da sauri nai baya ina kokarin mikewa kar ma sa shi jikin nai kofa da sauri sai dai kamin na kai tuni aman ya cika min baki ni kuma na bashi hanyar fitowa.
“Subhanallahi”
Ammy ta fada tana nufo inda nake kamin ta kawo tuni Aliyu ya zo ya rika ni, shi ya fito rike da ni harabar wajen na fara sheka amai kamar zan amayarda duka hanjina domin har ta hanci zubo min yake ban taba amai mai wahala irin wannan ba. Ina gamawa Aliyu ya zaunar da ni Batula ta dauko ruwan gora ta miko masa ya wanke min fuskata ya zuba min a hannunsa ya dura min a baki na kuskure ya zubar.
“Sannu”
Ya fada cike da tausayawa, sai na gyada masa kai ina jin wani irin jiri na dibana kaina kuma yana ciwo sosai har bana son daga idona.
“Bari na janyo mota sai muje asibiti”
“Aa bana so dan Allah”
Na fada da saurin domin har ga Allah bana son zuwa asibitin, daman can ni asbiti ba burgeni take ba, kuma ina ganin idan na bar gidan Sarkin Agadaz zai iya tafiyarsa ban sake magana da shi ba.
“Amman jikinki ya yi zafi sosai kuma.... ”
“Aliyu idan bata son asibitin ka barta tasha magani sai ta kwanta idan idan ta farka abun be sauka ba, sai a tafi asibitin”
Ammy ta fada ganin zan saka kuka saboda kawai ance aje asibitin.
“Aa ni bana jin bachin ma”
Na fada idona na cika da kwalla.
“Aliyu mu koma ciki ina son magana da shi”
“Ki barshi ya huta idan ya huta zai ce a kira ki ai”
Aliyu be gama rufe ba ki ba, sai ga daya daga cikin jikansa ya fito yana fada min Mai Martaba na son ganina. Da sauri na mike tsaye sai Aliyu ya rikani domin bana iya tafiya da sauri jikina kuma ba karfi ga jiri na dibata, daf da zamu shige bangaren Abbah muka ji tsayarwar mota, sai na waigo na hango Muhseen ya fito daga motar da waya a kunnensa, ni kuma na juyar da kaina muka shiga cikin falon, wannan karon babu kowa a ciki sai shi kadai da jikokin nasa. Daga bakin kofar Aliyu ya tsaya ya bar ni ni na wuce can ciki. Kasa na zube kusa da shi na zauna yana ta kallona a hankali ni kuma nai fuskar tausayi ya langwabar da kaina ina kallon kasa.
“Ina Asma'u take?”
“Tana sakkwato”
Na amsa mishi da sauri cike da kaguwar jin abunda zai sake fada.
“Ta fada miki dalilin rashin danginta a kusa da ita?”
“Ta fada min kuskuren da ta aikata, kuma ta yi nadama sai dai ta ce ba zata koma gareka ba har abada saboda abunda ta aikata maka, ta ce ta saka masarautarsu a kunya, da maka butulci ba zata sake dawowa gareka ba saboda ba zaka taba gafarta mata ba, ta yi kukan rashinka ta shiga matsalolin rayuwa ta rasa muhallin zama da abun sakawa a baki saboda butulcin da tai maka, a cikin abubuwan da ta rasa mai martaba har da lafiyarta, kuma ta alakanta hakan da butulce ma iyayenta da tai, a kullum tana fada min rayuwarta ba mai tsawo ba ce ta min umarnin na nemi danginta bayan rayuwarta kuma na roka mata gafararka da na su, ta haife mu ni da kanena shi ma har ya rasu gurin bara be san ka ba, tana bakincikin gina wata rayuwar ba tare da kai ba, da ni da ita duka rayuwarmu a titi ne sai mun yi bara muke ci, gidan kuma za mu kwanta sai dai mu raba a gidan wasu mu kwana”
Tun da na soma maganar yake ta jinke hannusa da sandar da ke hannun nasa, da alama maganganun da na ke masa sun taba masa zuciya ko kuma basa masa dadi.
“Ina Umar?”
“Ya rasu, Nana ce kawai ta rage sai ni”
Na fada cikin kuka, sai ya mika hannunsa da sauri jikan nasa ya risino yana sauraren maganar da ke fitowa daga bakinsa kadan-kadan.
“Ta fada muku inda Asma'u take ku je ku taho da ita”
A take ya karaso inda na ke yana tambayata da yarenmu.
“Ina Asma'u take?”
A take na fada masa, sai ya fice daga falon.
“Tashi kije ciki zan je masaukina”
Mai Martaba ya fada min, sai na mike tsaye ina jin kamar kar na tafi na fito daga dakin, sai na samu Aliyu a tsaye yana jirana.
“Kin yi magana da shi?”
Ba gyada masa kai.
“Eh yace zai je masaukinsa”
“To muje ciki ki huta”
“Mama Fulani ba zata bar ni na shiga dakinta ba, na kai ni gurin Ammy”
Na fada ba dan ina da tabbacin Mama Fulani zata hana ni shigar ba, sai dan na fi son Ammy da ita kuma zan fi sakewa a can. Be min musu ba ya gyada min kai sannan muka sauko tare muka nufi bangaren Ammy. Muna shiga falon Zee da Humaira suka fara min sannu na amsa musu har da Inteesar da ke ta daukin ganina.
“Ataa mun yi missing dinki sosai”
Ban ce mata komai ba bayan murmushin karfin hali da nai mata, sai Aliyu ya kalli Zee ya ce.
“Zainab kwantawa za tai a dakinki kar motsi ko wani hayani ya tashe ta dan Allah”
“Okay ya Aliyu”
Ta hannu yai min alama da na wuce sai ya bi bayana, har muka shiga dakin saman gado na haye abuna sai ya dauko filo ya dora min a gurin kafafuwana sukai sama.
“Sannu”
Ya fada yana taba kaina.
“Na gode”
Na fada ina kallonsa da fafaren idanuwana.
“Amman Babyna da gaske mahaifin Mama ne? Hakan na nufin kakanki ne kenan?”
Na gyada kai. Mamaki ne karara a fuskarsa kamar zai sake tambayata sai kuma yai shiru ya zauna gefen gadon kusa da ni.
“Akwai abubuwan mamaki a wannan maganar ta ki, amman lafiyarki ta fi muhimmancin a gareni, runtse idonki ki ja numfashi da karfi ki sauke a hankali ki saki tunaninki za ki samu bachi yanzu nan”
Yadda ya fada min haka nai a take kuwa bachi yai gaba da ni daman bachin ne a ido na.
ALIYU POV.
yana ganin ta yi bachi ya taso ta baro mata dakin tare da jan kofar a hankali ya kulle, part din Mama Fulani ya dawo a inda ya same ta cikin falon ta kasa zaune ta kasa tsaye, tana ganinsa sai tai saurin zaunawa tana kallo kofa ko zata ga Ataa ta shigo, da ta bata shigo ba sai tai kasa da murya kar wani ya ji kamar ba daga ita sai shi ne a falon ba.
“Aliyu na ce wai ita wannan Ataa daga ina take? Na ga ta rike kafafuwan sarkin Agadaz tana kuka suna buranci, na ce ko ta masa aiki ne a can kamin su dawo nan da zama?”
“Aa ta fada min cewar kakanta ne shine ya haifi mahaifiyarta”
Mama Fulani ta daki kirji tana zaro ido.
“Kakanta? Kaka kaka kaka fa? Kakanta fa? Ai idan mai fada ba shi da hankali mai ji yana da shi”
“Amman Mama Ayusher ba zata min karya ba”
“To ni kuma sai na yarda tunda gani fulanin mahaukata ko? Yarinya yar titi yar bara rana daya zata ce ita jikar wannan mutumen ce sai kuma sai na yarda ko? Jikarsa zata zo ta mana aiki? Har tai bara? Na yarda dai ta masa aiki a can Masautarsu, oh na ma tuna ina jin babarta baiwa ce su bayin Masautar ne”
“Wata kila kuma da gaske take yi Mama, tun da har kika ga ya kyaleta kuma ya aiko a kira ai kin san yana da alaka da ita, kuma bana zaton Ayusher zata karya, wata kila wata kaddararce ta saka suka tsinci kansu a cikin wannan halin rayuwar”
“Uhm Aliyu baka da wayo wallahi taya za 'ayi tana jikar sarki ta zauna a nan ko tai bara? Ai da kowa sai ya jiya, kuma ko dukansu yake kullum sai sun zauna a inda yake, yanzu ma ina ga aiki suka masa ko kuma bayin masarautar ne shiyasa lokacin da ta ji sunansa hankalinta ya tashi ita dai ta ganshi”
“Ko ma minene dai za a warware shi very”
Mama Fulani taja wani dogon numfashi ta sauke tana girgiza kai.
“Kai ba haka ba ne, sam ina... Ba za zai yiyu ba”
Ta kasa yarda da abunda Aliyu ya fada mata taya ma zata yarda wai wata Ataa jinin wannan sarkin ce. Sai dai wani abun amman bata yarda ba, Aliyu ya mike tsaye ya nufi kitchen kenan sai ga Abbah ya shigo yana gyara babbar rigarsa.
“Hajiya Fulani za mu je sokoto yanzu nan”
“Sokoto kuma? Gurin me?”
“Mai Martaba ya ce aje a dauko masa mahaifiyar Ataa, da jirginsa da ya zo da shi za a aje kin ga ko tunda gida ne ai da ni za a aje”
“Mahaifiyar Ataaa?”
Ta fada tana dukan kirjinta har da wani kashe ido take.
“Mahaifiyar Ataa fa kace Alhaji?”
“Eh ita fa kin san tana gidan Momy”
“To ina jin wata babbar sata suka masa lokacin da sukai zama gidansa, ina lokacin da suke bayinsa sun masa wata katuwar sata ko kuma hasara, shiyasa Ataa take kuka tana rike kafafuwansa so take ya yafe musu”
Mama Fulani ta fada tana gyada kai.
“Amman abunda shi jikan nasa da suka zo tare yake fada mana wai Mahaifiyar Ataa ita ce yar Mai martaba”
“Aehhhh ya fa ka ce?”
Ta tambaya da karfi tana zaro ido.
“Eh Wallahi ni kan na ce ai sun warke”
“Aa ba wani zancen warkewa ina jin dai yana nufin yarsa ta gari tun da shi sarki ai baban kowa ne, balle mutane masu nijar kasan yadda suke da junansu”
“Ko ma minene dai ai shi Mai Martaba zai fada da kansa, yanzu haka har ya wuce gidansa da ke nan yana jiranta, da ko be yi niyar zuwa gidan ba hotel ma zai sauka ni ne dai na dage ya sauka a nan ashe kin ga abo ne,sai muj dawo”
Abbah na fadar hakan ya juya ya fice da sauri. Mama Fulani ta rumfume hannayenta a kirji sai girgiza kai take.
“Aa ina ai ba zai yayu ba sam”
Duk abunda suke Aliyu na jikin kofar kitchen din rike da ruwa yana sha, shi kanshi mamakin abun yake ya san Ataa ba zata masa karya ba, kuma yadda ya ga Sarki ya nuna mata kukarwarsa ya san dole akwai alaka mai karfi a tsakaninsu, gashi kuma yanzu har ya ce aje a taho masa da ita, sai dai be san taya ta bar gidansu ba mi ya faru har suka tsinci kansu a cikin wannan rayuwar.
Gaba daya Mama Fulani kasa sukuni tai zuciyara na son yarda kuma tana jin yarda idan ta duba wasu abubuwan da suka faru, abun na ta cinta kamin su Abbah su kai har ta kira Momy ta labarta mata abunda ya faru, ita ma kanta Momy ba karamin mamaki tai ba jin abun kai tsaye kamar daga sama a take mamaki ya cika ta. Bayan ta gama da Momy kuma ta koma tana tatauna maganar da su Maryam da Rukaiya Maryam ce tai saurin yarda yayinda Rukaiyah kuma ta tsaya kwankwato.
“Idan kuma da gaske ne fa Mama? Kina ganin da ba jikarsa ba ce zai kyaleta ta rike masa kafa kuma tai ta masa kuka haka har kuma ya ce a aje a dauko masa mamanta? Gaskiya ina ganin gaskiya ne”
“Ai sarakuna suna da wannan karancin, kin san ai wasu suka rika kafafuwan manyan mutane saboda neman gafara ko kuma tubarraki, amman ba gaskiya ba ne”
“Gaskiya ni ma ban yarda ba, ai ko da mai unguwa kake da alaka sai an ji balle kuma mutum irin wannan, ai ko kama ma ba su yi ba”
“Eh ba su da kama fa, yauwa Rukaiya ashe kin gane, ina jin dai ba yin sa ne ada can da”
Haka sukai ta tattauna maganar a tsakaninsu daga Mama Fulani har Maryam da Rukaiya da kuma Baby wacce bata ce komai ba mamaki suke suna Ala ala abun ya zama ba gaskiya ba. Aliyu kan yana ta an ya tare a bangaren Ammy yana cin abinci shi da matarsa wacce bata dade da farkawa ba.
Ya jidadin yadda ta farka zazzabi ya sauka duk kuwa da kasancewar bata sha magani ba a lokacin da zata kwanta.
ATAA POV.
Na farka da tunanin Nana a can cikin mafarkina kuma abunda ya faru dazun nai mafarki, babu komai a raina sai son ganin irin yadda Nana za tai idan ta ji cewar na hadu da Babanta ko kuma Mahaifiya ce aje a taho da ita. Ina ma ace ina can na na ga irin kukan farinciki da za tai da kuma irin rudewar da za tai. Ina cikin wannan tunanin Batula ta shigo sai nai saurarin share hawayena.
“Ya jikin”
“Na ji sauki”
Na amsa har lokacin hawaye na sauko min.
“Ya Aliyu ya ce na tashe ki ki yi sallah magariba ki ci abinci idan zazzabi be sauka ba za ku je asibiti”
Sai da tai maganar na tuna da cewar da yamma na kwanta, ashe har magariba ta yi ban sani ba, lallai na dan yi kwanan da nauyi.
“Ki fada masa na ji sauki”
Na amsa ta ina gashi na nufi bandaki da yin alwala so na ke nai sallah sannan na saka Aliyu ya kira min Momy ta bawa Nana mu yi waya, na fara yi mata wannan albishir din kamin kowa ya mata domin an san ba za a je daukarta a yau ba idan ma anje yau sai gobe za su iya ko kuma cikin dare, waya sani ma ko za su tsaya tsaya jiran jirgi kuma ace babu jirgin sannan na da wasu hours. A gagauce nai alwalar ina fitowa sai an samu Aliyu zaune a kasa Inteesar na jera mana abinci shi kuma idonsa na kaina kamar zai cinye ni.
“Ya jikinki”
“Na ji sauki, Aliyu idan mun yi sallah za ka kira nin Nana?”
“Yes amman sai mun fara cin abinci tukuna”
hijab din Zee na saka nai sallah har yai na gama na yi addu'a idon Aliyu na kaina, kamin na juyo har ya bude fular tuwon ya soma zubawa a a plate, ina juyowa ya saka spoon ya fara diban abincin ya bani, kadan kadan na ke ci saboda warin miyar nake ji daker ma na ke iya hadewa a take warin manjan ya daki hancina sai na ji kamar zan yi ama da sauri na rufe bakina na nufi bandaki, shi kuma ya taso ya biyoni ina sheka aman yana shafa bayana yana min sannu cike da tausayawa.
*Z A K I -it's not free, pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence via 08036126660*
*AG cera ya zo domin ya temaki garkuwan jiki da kuma lafiyar jiki. Sinadari ne wanda ze magance matsaloli da dama wadanda suke hana garkuwan jiki aiki yadda ya kamata ko kuma yake rusa garkuwan jikin ita kanta.*
*Cututtukan zamani daban daban sun sa mutane gaba kuma magance su yana da wahala; irin ciwon Sugar, hawan jini, ciwon sanyin kashi, ciwon gabobi da sauran su. Haka ma cutukka irin wadanda suka shafi fatar jikin wadanda sun hada da kyasfi, pimples, takurewar fata, rakainuwar fata da kuma haske da kyallin fata duka ana shan AG cera kuma yana temakawa wajen magance illolin nan. Mutane masu fama da rashin karfin jiki wajen kwanciya da iyali da kuma mata masu fama da yawan ciwon mara lokacin al'ada ta karshen wata suma baa bar su a baya ba. A takaice dai AG Cera yana temakawa wajen magance cuttukka daban daban wadan ke damun mutum. Domin karin bayani ku tuntuni mu a wannan number +60167474649 ko kuma ku ziyarci shafin mu http://agnutritioninternational.com.*
Sai da nai aman na gama sannan ya zuba min ruwa na wanke baki ya fito daga bandakin. Inda na aje Hijab din dazun ya nufa ya dauko ya zo kusa da ni yana kokarin saka min.
“Saka muje asibiti”
Na bata fuska domin har ga Allah bana jin komai a yanzu, bana jin wani ciwon kai ko wani jiri da zafi jikin kamar na dazun.
““Wallahi bana jin komai Aliyu, aman ne kawai kuma shi ma saboda miyar ne”
“Wani abu kika gani a ciki?”
“Aa bana son miyar ganye dai?”
Fuskar mamaki yai ni kaina ina mamakin kin shan miyar ganye da na ke bayan tana cikin miyar da na ke so, gudun kar Aliyu ya zargi ko bana son cin abincin gidansu ne yasa na ce.
“Ba