Showing 45001 words to 48000 words out of 225640 words
koma cikin satin nan ma”
“Ba dole ni zan zauna ba, zan saka wasu ne”
Ya fada yana mata kiss sannan ya mike tsaye yana kallon kansa a madubi.
“Idan kina son Abuja za mu ko, amman ni zan dawo na karasa wani aikin”
“Fita za kai?”
Ta tambaya tana mikewa tsaye
“Yes fada min abunda zan zo miki da shi”
Hannu ta kai ta raka rigarsa tana kallon cat eyes dinsa.
“Aliyu ina za ka je?”
“Momy ke nema na”
Ya bata amsa kai tsaye, wanda hakan yasa ta sakinsa ba dan ranta ya so ba, domin zuciyarta ta fara yi mata zargi akansa, sai dai ba damar hana shi fitada kuwa karya yai mata tunda ya ambaci sunan Momy.
“Bana son komai amman ka dawo da wuri”
Ta fada cikin yanayin da ke nuna bata son fitar tasa. Sumbantar goshinta yai
“Sure”
Sannan ya juya ya fita yana wasa da keys din hannunsa. Gurin windows ta nufa ta tsaya daga can sama tana kallonsa har ya tashi motar aka bude masa gate ya fice, ajiya zuciya ta sauke zuciyarta na raya mata wani abu marar dadi, yadda ta ke ganin Aliyu yana maganar yarinyar kwana biyu ta soma rashin yarda da fitarsa, ta san ba abu ne mai sauki ya samu gabinta ba, ba kuma lallai ya tsaya neman yar talakawa kanar wannan ba, amman zuciyarta na raya mata cewar mijinta zai iya son yarinyar saboda kyauta.
“Ba lallai ne ya so ba, nasan Aliyu baya son talaka, kuma ko da ma yana son ta da gaske idan na nuna masa bana so ba zai yi ba”
Ta furta ma kanta a kokarinta na kusar da abun a zuciyarta, domin saukar numfashinta yake tarewa a duk sa'in da tai tunanin cewar Aliyu zai hada son ta da wata.
“Wadanda ma suka fita arziki, tsabta kwalliya sun kula Aliyu amman be kula su ba, balle wannan yarinyar, shi kansa ya san ba sa'ar da zai kawo ma kansa wannan a zuciyarsaba ne”
Wannan karon murmushi take tana fadin wannan maganar, kamin zuciyarta ta kawo mata wani tunanin na dabam.
“Miyasa ya ke cewa ya kamata mu taimaka mata?. Saboda yana ganin kamar ta taimake ni na samu lafiya ne! That's it,”
Wani shaukin son mijinta ne ta ji ya lullubeta, ta sani sarai Aliyu yana sonta baya son bacin raita kuma be hada sonta da son kowa ba, miyasa ma zatai wannan tunanin tun farko? Sai a yanzu take jin kamar ba ta kyauta masa ba, da tai tunanin zai iya son wata yar talakawa can kamar Ataa yar talakawa ma kuma yar aikin gidansa, ji tai kamar ta yi wani katon sabo, shi kansa ta san idan ta fada masa zargin da take masa ba zai jidadi ba, kuma zai yi fushi da ita.
ALIYU POV.
Clapperto road ya fi tsaya masa a rai, domin tana fadin sunan unguwar ya tuna da lokacin da ta fashe masa gilashin mota ya biyo titi sai gashi ya ganta ta shiga kangon gidan, sai dai be taba tunanin cewar mahaifin Rahma ne da gidan ba. A hankali yake driving dinsa har ya isa unguwar daidai inda yasan gidan yake ya tsaya, daga cikin motar ya yake kallon kwannon da aka saka aka zagaye gidan, kofar shiga gidan a rufe, hakan kawai ya samu kansa da kin son barin gurin, and baya jin zai iya fitowa daga cikin motarsa ya tambaye wani ina masu gidan ko abunda ya shafesu, yana daga cikin abunda ya tsana neman wani abu that's why sai dai ya saka a masa, but this time around yana jin kamar da kansa yake bukatar yin gudun kar wani yai masa fahimta baibai.
Sai da ya hango wani tafe kusa da motarsa sannnan ya sauke gilashin motar ya bude baki kamar baya son magana ya ce.
“Malam ina masu gidan nan?”
Mutumen da aka tambaya ya tsaya daidai gilashin motar Aliyu yana kallonsa ya ce.
“Mai ainahin gidan kake tambaya?”
Aliyu yai shiru na yan mintuna kamar ba zai sake cewa komai ba.
“Wata fulanin yarinya na ke tambaya”
“Oh Ataa buzuwa ga inda suka koma can, gidan na shiga kwanar akwai wani karamin gida ba sosai ba, ka tambaya suna can”
Mutumen na gama yi ma Aliyu kwatan gidan da ke nesa da wannan, Aliyu ya daga gilashin motarsa ba tare da yai ma mutumen godiya ba, ba kuma tare da ya sake cewa komai ba. Har mutumen ya ji haushin bata lokacinsa da yai yana masa bayani. Inda mutunen ya kwatanta masa ya nufa amman ya ki ya shiga kwanar ya tsaya yana hangon gidan da yake sa ran shine mutumen yake nufi. Idan ma ya ganta mi zai ce mata? Shi ya fi tsaya masa a rai, yasa ba zai iya bata hakuri ba, and ba zai iya tsayawa yi mata bayani ba, then miye na neman inda take har ya nemi ganinta.
‘No idan na ganta da ido na tabbatar tana nan zan saka wani ya zo yai mata bayani, ba ni da hannu a ciki’
Zuciyarsa ta raya masa, gamsuwa da wannan yasa shi shiga kwana ya tsaya daidai kofar gidan, babu wanda zai aika ciki and wa zai ce a sallamo masa ma idan ya aika din? He decided ya danna horn idan an fito fine idan ba a fito ba kuma ya kama gabansa. Sau biyu ya danna kan yai na uku Farida ta leko ganinta yasa shi sauke gilashin motar yana aika mata da wani kallo. Tabbatar da kofar gidansu ake horn din yasa ta koma ta saka Hijab dinta ta fito ta nufo inda yake fake da Motarsa yana kallon kofar gidan na su.
“Ina wuni?”
Ya gyada mata kai alamar ya amsa gaisuwar gaisuwa sannan ya motsa bakinsa kadan ya ce.
“Wata buzuwa na ke nema ance suna nan”
Gaban Farida ya fadi, jin cewar Ataa yake nema, gashi daman daga ganinsa ba zai yi mutumci ba, abunda ya fara zuwa a ranta mi Ataa tai masa da ya zo nemanta, mi zai mata? Miyasa yake nema? Duk a lokaci daya tai ma kanta wannan tambayar.
“Sun tashi daga nan”
Ya sake kallonta kasa da sama ba tare da yace mata komai ta shiga masa bayani domin itama kanta tana jin kamar zai gano karyarta ne.
“Eh mai wacan gidan ne ya ce sai sun tashi, saboda an fada masa maciji ya sari maman Ataa, da aka kaita asibiti suka dawo nan shine ya sa aka watsar da bukkarsu aka koresu ya zagaye gidansa, sai suka dawo nan shekaranjiyar nan suka koma Kaduna”
“Ba su gida ne?”
“Ba su da gida daman bukka ce suke kafawa da mutumen ya koresu suka zauna nan na kwana biyu sai kuma shekaranjiya suka koma Kaduna”
“Kaduna wane unguwa?”
“Na'am...”
Tai shiru tana ta tunanin unguwar da zata fada domin ko a sokoto ba ko wace unguwa ta sani ba balle kuma a Kaduna da bata taba zuwa ba.
“Rijiyar Zaki... ”
Ya sake kallonta da kyau gashi fuskarnan tashi babu annuri duk sai tsoro ya kara kama ta.
“Aa ba can ba unguwar mai malala... ”
“Malali?”
Ya gyara mata jin kamar ba ta fada daidai ba.
“Eh eh can fa, kusa da wani gida mai jan gini zaka ga bukkarsu a gurin”
Hannunsa ya saka ya dauko katinsa da ke cikin motar ya jefara kasa.
“Ga kati nan idan kin samu labarin gaskiyar inda take ki aika min sako ta number, ko kuma ki tura min number ta”
Dukawa tai ta dauki katin tana fadin.
“Su da ke neman abunda za su ci ina ma zata samu waya, amman miyasa kake nemanta ta maka wani abun ne?”
Ko ba ita ba be ji zai amsawa kowa wannan tambayar balle kuma ita da yake gani ita da banza duka daya. Gilashin motarsa ya tayar ya soma driving a hankali ya bar a gurin tsaye tana kallonsa har ta daina hangosa.
Daga Clapperto road ya dauki hanyar arkilla wato family house dinsu wajen Momy. Yanzu kan ya gane dalilin daya kai Ataa asibiti, wato maciji ya tsari mahaifiyarta a can ne Doc Asim ya ganta ya cire mata kodar, amman abunda ya fi tsaya masa a rai zancen bukkar nan, how on earth za ace akwai mutumen da be da gidansa kansa, even ma ace mutum be da gidan kansa ai akwai gidajen haya da zaka iya biyan kudi ka zauna, amman ya za ace a bukka suke zama, samun kansa ya kasa yarda da abunda yarinyar nan ta fada masa. A daidai gate din gidansu ya tsaya ya danna horn sau daya kan kace kwabo aka bude masa gate din ya shiga, a harabar gidan ya faka motarsa ya fiddo wayarsa ya kira Doc Asim, ringing daya ya picking a tunanin Doc Asim zai masa maganar ciwon Rahma ne ya ce ya tashi ko wani abun dabam amman a mamakinsa sai ya ji ya aika masa da wata tambayar ta dabam.
“Yarinyar da ka cirewa mhaifiyarta koda miya kawo ta asibitin ka?”
“Maciji ya tsari mahaifiyarta, suka zo bata da kudin magani ta ji ana zancen koda ta ce zata siyar”
“Ba siyarwa tai ba Asim, cirewa tai da karfin tsiya, da siyar tai yi kudin da zaka bata za su isheta tai rayuwa na wani lokaci”
“Ina shaidar siyar da ita da tai, kuma be kamata wannan ya dame ka ba, kai dai ka ce kana son koda kuma an samo maka ba an wuce guri ba”
“Da na ce ka kawo min ban ce ka zalinci wata ba ai, maciji ya sari mamanta sai ki amfani da wannan damar ka yaudare ta ko? Mahaifiyarta tana raye ko ta mutu”
“Ba ni da masaniya yanzu”
Aliyu ya kashe wayar tare da bude motar ya fito, yana tuna lokacin da yake tare da kanwarsa Humaira har take mikawa Ataa hannu ta ce ta bata wayarta da ta dauka. Be samu kowa a falonsu ba, kai tsaye nufi dakin Momy da yake hangowa a bude, yana shiga ya sameta tana gyaran gadonta, da sallama ya shiga ya zauna a kujear da ke facing din gadonta.
“Momy yau ke kike gyaran gado da kanki?”
“To yau duk da wuri suka fita, kuma har yanzu ba su dawo ba”
“Ai ba kullum za su rika aiki ba, su ma suna bukatar hutu, da dai kin samu mai aiki ai su ma sai su hutu”
Zaunawa Momy tai tana kallonsa.
“Shi gyaran gado shara wanke wanke girki har wani aiki ne? Idan ba su koya a gida ba so kake su je su yi ma mazajensu irin na matarka? Ai ba kowa ne namiji ne irin ka ba”
Yayi murmushi.
“Momy ita ma fa saboda ciwo ne, bata saba da wahala ba”
“Kula da gida da miji shine wahala? Wasu na can Allah kadai ya san abunda suke kamin su samu su ci ma, wasu ba su kaita ba amman suna can sun iya kula da miji, kai yanzu baka san dadi mata ba sai ka samu mai kula da kai”
“Rahma ma tana kula da ni Momy, ke ce ba ki gane ba”
Tabe baki Momy tai
“Dazu mun yi waya da Fulani ashe taje dubai har ta dawo ban sani ba, ta kirani tana ta min fada wai na dauke mata yaro”
“Eh ta kirana kwanan baya tace min zata je dubai ashe tafiyar ba mai dadiwa ba ce, ai mun kusa zuwa Abuja Rahma ma ta fara min maganar”
“Ya dai kamata kan ka koma gurin aikinka, kuma kasan Fulani ba son take kai nisa da ita ba”
“Zan koma”
Sai yai shiru for some minutes sannan ya kalli Momy ya ce
“Momy wai ashe akwai mutanen da basa da gidajen zama har sun kashe bukka? I find it so hard to believe”
“Ban fahimta ba, wa ya fada maka?”
“Mamy yarinyar nan da na ke fada miki, wai ashe gidan da take zaune gidan baban Rahma ne, sai maciji ya sareta da ya samu labari sai ya koreta sanadin hakan aka kai mahaifiyar asibiti ina jin a can ne Doc Asim ya cire mata kodar aka sakawa Rahma, wai can din bukka suke kafawa su zauna”
“Dan wajen Fulani ina ka samu labarin nan?”
Momy ta tambaya jikinta a sanyeye. Sai yai shiru kamar baya son fadawa Momy cewar ya je nemanta ne.
“Just tell me i want to help her, ina zan samu ganin yarinyar nan? An zalince da yawa, tana neman gurin zama ace kuma an yi ma mahaifiyarta haka, mahaifiyar ma tana da rai ko ta mutu? Kuma ace mutumen da ya koreta a gidan macijin ya tsareta a gidan an dasawa yarsa kodar mahaifiyarta, yarinyar nan ba zata taba mantawa da ku ba Dan wajen Fulani kun cucece ta”
Momy ta fada hawaye na sauko mata, zuciyarta ta cika da tausayin Ataa duk kuwa da kasancewar bata taba ganinta ba ko sau daya. Aliyu ya baro kujerar da yake zaune ya zauna kusa da Momy.
“Momy trust me, Wallahi ba da sanina akai mata haka ba, duk laifin Doc Asim ne, nima ta ba ni dan tausayi....”
Momy ta kalleshi.
“Da? Dan tausayi fa ka ce Dan wajen Fulani, sai ka ce ba musulmi ba, irin wannan yarinyar ai kamata yai ma a kwato mata hakkinta”
“Gurin wa?”
Ya fada yana kallon Momy. Sai ta share hawayen da suka zubo mata ta ce.
“Seriously yarinyar nan ta ba ni tausayi, yarinyar da take irin wannan rayuwar sai kuma a sake jefata a wata rayuwar ta wahala, ku kuna cikin farinciki ita an saka ta a kunci”
Ya busar da iskar bakinsa, ba dan tausayinta yake ji kamar yadda ya ce wa Momy ba, tausayinta ne gaba daya ya cika masa zuciya, be taba jin tausayin wata halitta mai sunan dan'adam ba kamar yadda ya ji yana tausayin Ataa a yau, and the most annoying part is be san inda take ba, waya sani ko sanadin hakan ta kara shiga wani halin.
A unguwar yai sallah la'asar sannan ya nufo gidansa, yana ta sake saken zuwa kaduna daga can ya bi ta Abuja ya gaishe da Mama Fulani, sai dai daya tuna da cewar idan ma yaje din be san mi zai ce mata ba sai duk wani karfin guiwa na shi ya zube daga ya yanke shawarar samun wani ya bincika masa a can Kaduna din.
ATAA POV.
Ina zaune a inda Maman Salma ta tafi ta bar ni ban tashi ba su kuma ba su kula da ni ba, ina zaune a guri har na iya gane anyi sallah azahar ta hanyar agogon falon daya nuna karfe 2. Ban san wa zan yi ma magana ba cewar ina son nai sallah ba, domin ban ga fuskar kowa a cikinsu ba, duka yan matan ko wacce ji take da kanta dan ko kallo ban ishe su ba, bana jin cewar idan nai musu magana za su amsa min, ina zaune a gurin ina ta rokon Allah ya kawo min mafita sai ga Inteesar ta shigo sanye da uniform din Islamiya tana kallon inda na ke.
“Ke Ammy na kiranki”
Ta fada min sai kuma ta nufi Anty Maryam tana fadin.
“Anty Maryam makaranta zanje yanzu ba kudin na siyo miki tuwon madara”
Ni dai ban jira na ji abunda Anty Maryam din zata fada mata ba, na mike tsaye na nufi kofa na fita da sauri kamar zan fadi. Hanyar da naga Maman Salma ta bi farkon zuwan mu na bi na shiga part din Ammy da sallama, sai ta amsa min da far'arta kamar dazun har hakoranta biyu na makka na bayyana, na sake gaisheta ina risinawa kasa.
“Lafiya kalau ya ma sunanki?”
“Aisha amman Ataa ake kirana”
“Masha-Allah ashe Mamana ce, fatar dai kin iya yankan allayahu ko?”
“Na iya”
“Da kyau to shiga kitchen gashi can sai ki yanka min ki wanke kinji ko?”
“To amman ban yi sallah ba”
Sai ta nuna min bandakin da ke falon.
“Shiga can ki yi alwala”
Na nufi inda ta nuna min, a lokacin da na shiga sai na samu komai tsaf kamar ba a taba shiga bandakin ba, a kasa nai alwala domin na hango akwai hanyar ruwa a gurin sannan na fito na shimfida dankwalina kusa da kofar bandakin nai sallah, sannan na nufi kitchen ina shiga na samu allayahu a kwando na dauka na gyara na saka wuka na yanka kananan sannan na wanke mata na aje kamar yadda ta bukata na fito daga kitchen din.
“Na kare”
“Yauwa sannu ko, za ki iya tafiya”
Na juyo ina ta jin kamar nai zamana a part dinta ko ba komai zan fi sakewa fiye da part din Mama Fulani da ba su san darajar mutane ba. Haka na dawo part din cikin rashin jindadi da na dawo ban samu kowa a falon ba sai tv, a inda na zauna dazun na sake zama sai na raba da kujera saboda na jidadin jinginawa, haka na zauna a gurin har la'asar ba a bani abinci rana ba, da akai la'asar ne na unkura zan tashi sai na ji an turo kofar falon an shigo, waigowar da zan yi sai na ga Muhseen, murmushi ya sakar min ya karasa inda take nake yana fadin.
“Tun da na ganki na ke ta tunanin inda na san fuskar nan take, sai yanzu na tuna da na taba ganinki asibitin uduth ko? Kin tuna?”
Na dan yi shiru alamar tunani sannan na gyada masa kai alamar na tuna.
“Good girl, ashe zan sake ganinki, kin ci abinci?”
Na girgiza masa kai alamar ban ci ba.
“To kin yi sallah?”
Nan ma kan na girgiza masa sai yai murmushi.
“Ba ki magana ne hala?”
Na yi shiru ban ce masa komai ba, na yi kasa da kaina.
“Za ki sha wahala idan kika ce kunyata za ki ji, ga toilet can je ki yi alwala sai ki zo ki ci abinci”
Ina nufar inda ya nuna min sai Mama Fulani dake saukowa ta daka min tsawa.
“Karki kuskura shiga toilet din nan, yarana su shiga ke ki shiga akan me?”
Tsayawa nai cak ina kallonta kamar yadda shi ma yake kallonta.
“Sallah za ta yi fa Mama”
“Ko mi za tai taje can a tab din garden ta yi karta shiga mana toilet”
Kamar zai sake cewa wani abu sai kuma ya kalleni ya ce.
“Idan kin fita daga falon nan za ki ga wani gurin ai kin san Garden ko?”
Na gyada kai.
“To can za ki je”
Na juya na fice daga dakin ina hangen yadda Mama Fulani