Showing 192001 words to 195000 words out of 225640 words

Chapter 65 - Zaki Book 1 Hausa Novel Complete

wanda ya zama dole su girmamani ko da kuwa sun haife ni.

“Ta so muje bangaren Ammy mu gaishe su”

Ba musu na mike tsaye, ina gaba yana bayana har muka fito daga part din Mama Fulani muka nufi bangaren Ammy.

“Ba dan Mama tana jin kunyarki da nauyinki ba da yanzu ta rumgume ki tana nuna miki jindadinta da farincikinta aka my samun cikinki”

Ban ce masa komai ba, muka cigaba da tafiya, fuskarsa ba yabo ba fallasa muka nufo bangaren Ammy sai dai muna shiga falon ganin Muhseen zaune yasa ya dan canja fuska kamar be ji dadiba, ni kan har na yi farat zan fara masa magana sai na tuna cewar ina da aure a yanzu kuma ina tare da Aliyu. A saman kujera yake zaune Kamar yadda Ammy da Nana ma suke zaune a saman kujera, tun da nai sallama ya dago kansa ya kalleni sai ya maida idonsa gurin wayar be sake dagowa ba, har na zauna ina gaisawa da Ammy da Nana, Aliyu ma ya gaisa da ita, sai Muhseen ya mike tsaye ya face daga falon idonsa akan wayarsa ni kuma na bi shi da ido ina juyowa Aliyu ya watsa min harara a cikin sigar da babu wanda zai gani ya fahimta sai ni da akai wa.
Mikewa yai ya fice daga bangaren Ammy ya bar a nan, ni kuwa na tashi na koma kusa da Nana na zauna a kasa na dora kaina saman kafafuwanta, sai ta fara shafa kaina tana murmushi.



ALIYU POV.

Sam be jidadin ganin Muhseen ba ba kuma dan komai ba sai dan yana tare da Ataa, idan ya tuna cewar Muhseen ya taba son Ataa abun tana taba shi kuma yana jin babu dadi, duk kuwa da kasancewar ya aureta amman wannan kishin yana nan cikin ransa. Ko da ya shigo bangaren Mama Fulani yayi zaton zai samu Muhseen a falo ko dakin Mama Fulani amman sai ya samu akasin haka, domin kuwa Mama Fulani ce kadai a dakin zaune rike da brush din dazun tana kallon wani gurin kamar mai tunanin domin shigowarsa kadai har da zabura tai.

“Mama har yanzu laifina kike gani?”

Bata ce masa komai ba sai lasa lips dinta da tai cikin yanayin damuwa.

“Wallahi Mama Nasir ne ya kawo min wannan shawarar amman ba wai dan wata manufar nai ba”

“Ina maka murna Aliyu wannan babban abun farinciki ne da jindadi, ba zan iya fada maka ko misalta maka yadda na ke ji a yanzu ba, sai dai abun bakinciki na zan iya nuna ba”

“Saboda mi Mama”

“Kai ma ai ka sani Aliyu duk wani abun da zan musu a yanzu ko na nuna farincikina ba yarda za su yi da ni ba, kuma har abada Ataa ba xata daina ganin cewar bana sonta balle kuma abunda yake cikinta. Aliyu kunyar kaina na ke ji, kunyar kaina na ke ji sosai”

Ta fada idonta cike ta kwalla har ya fara sauko mata, murmushi Aliyu yai yana kokarin nuna mata shi be ga wani abun damuwa ba.

“A rashin sani kika aikata Mama, kuma ni danki ne, Ayusher ta sani dole ki so abunda yake cikina tunda har kina so na, na fada mata bani da kamar ke da Momy a duniyar nan, ni yanzu abunda na ke so ma idan kin yi wamka kin shirya kije ki roka min Mamanta ta bar min matata ni ba sai ta je d ita can nijar ba”

“Nijar za su tafi?”

Ta tambaya tana share hawayenta.

“Eh ta fada min tun shekaranjiya cewar Mamanta tace za su tafi ta ga dangi tare da Sarkin Agadaz za su tafi idan zai wuce, da na yi nijar bin ta muje tare, yanzu kuma na canja sha'awara gaskiya idan tai tafiya mai nisa da wani ganin dangi jagalgala cikin za ayi, kara dai tai hakuri sai idan ya girma sai mu tafi tare ko kuma idan ta haihu”

“Gaskiya ni ma ban bada goyon bayan ta tafi yanzu ba, taya zata fara yawo da karamin ciki ma?”

“That's why I love you Mama, kina da mugun fahimta, yanzu dai ki yi wanka sai ki je ki yi magana da Mamanta ki roka min ita”

“Aa ba zan iya ba”

“Zaki iya”

“No-no Aliyu i can't ai da kunya nai maganar a yanzu ma, duk abunda zan yi kar suke kallona, jiya mahaifiyarta ta kasa sakewa da ni, itam Ataa ba so zata tai b Wallahi balle har tai tunanin abun kwarai zan mata”

“Mama pls for me? Ai za ki iya min komai ko?”

Ta gyada kai cikin damuwa.

“To pls ki yi magana da ita as my mother kuma saboda grandchild dinki ba wai as abunda kika aikata cikin rashin sani ba”

Yawun bakinta ta hadeye ta tashi ta nufi bandaki cikin yanayin damuwa.



*Manage pls*
“Ina ganin zai fi kyau idan ka hakuri ka bi matarka Aliyu, ko kuma ka kira Momy ko Ammy ka rikesu su yi ma mahaifiyarta magana idan zata yarda ta barta na wani lokacin idan cikin yayi kwari”

Tana zaune bakin gado take fadin wannan maganar bayan ta fito daga wanka, Aliyu ya dago kansa daga kan wayarsa ya kalleta.

“Ko na bita hankali ba zai kanwata ba Wallahi, kuma kin san ba ni wanda zau shige min gaba yai min ruwa da tsaki a wannan lamarin sai ke”

“Ba zan iya ba Aliyu, Wallahi ina tsananin jin kunyar kaina balle kuma na hada ido da Ataa ko mahaifiyarta, da ace komai be faru ba da yanzu ba haka ba”

“Amman Mama”

“Aliyu ba zan iya ba, dan Allah ka je ka samu Ammy ko Abbahku kai masa wannan maganar”

Ta amsa masa kai tsaye da dukannin gasjiyarta, taya ma zata iya zuwa ta ce zata roki abar Ataa saboda cikinta? Yarinyar da ta gama wulakantawa ta aybanta. Ai wannan ya zama rashin kunya ma. Aliyu be sake cewa komai ba, ya mike tsaye ya fice, har ga Allah baya son tafiyar Ataa a garin nan yanzu ya san duk yadda zai bata kulawa a nan dole a can sai ya daga mata kafa wani abun ma ba a gaban idonsa za tai ba, gashi tafiya ce ba nan kusa ba, waya sani ma ko ace sai taga kowa da kowa tukuna za su dawo? Ba wai baya son haduwarta da danginta ba ne, shi yadda za a jigilgila cikin ne baya so. Yana son cilasta Mama Fulani tai ma Nana magana ne saboda bakinta da na Nana ya hadu a wani gurin na nunawa Ataa kulawa, ko da ba zata yarda ba akalla yasan Nana zata san cewa Mama Fulani ta damu a yanzu, and hakan da za tai a yanzu matakine na murje ido ta nuna komai ba komai ba ne yadda za a zama abu daya, amman ya saka samun hakan daga gareta, ya sani abunda Mama Fulani ta aikata ba daidai ba ne, shi kanshi baya ganin laifinta ko ganin kuskurenta har sai yanzu da yake kokarin gyara na shi kuskuren. Cikin mota ya koma ya zauna ya kira wayar Nasir tana yin ringing  yai picking kamar mai jiran kiran.

“Babban Baby gani a hanyar gidanka fa da Madam”

“Gurin me?”

“Zata zo ta ga Ataa ne kasan ba su taba haduwa ba, and tana son taya ta murna samun ciki”

Yar dariya Aliyu yai shi kanshi Nasir sai da yai dariya sannan aliyu ya dora da.

“Bana gida ni da ita muna nan gurin Mama, Nasir ina son magana da kai”

“Ayyah bari na sauke ta gidansu yayarta zai na same ka a can”

“Alright”

Aliyu ya kashe wayar yana ta kallon garden gidan da ke facing din inda motarsa take fake. Fita yai daga motar ya nufi bangaren Ammy sai kuma ya samu kansa ya kasa shiga ciki sosai yake jin kunyar Nana shi kanshi har Mamakin abun yake, domin ko iyayen Rahma yana sakewa da su da su ne kai tsaye zai iya nuna musu baya son matarsa tai nisa da shi balle kuma ace tana da ciki abunda yake kauna.
Har ya ciro wayarsa ya kira Ataa sai ya tuna da be saka mata line a ciki ba, a take ya aikama Nasir text, sannan ya juyo zai dawo part din Mama Fulani kuma sai ya hango Muhseen ya shiga can sai kawai ya nufi gate yana ta sake sake a ransa, he can't face Nana kai tsaye ya fada mata haka and idan Mama Fulani ba zata iya zuwa tai magana da Nana ba ba zai iya rokon Ammy ba, domin a ganinsa idan har Nana da Mama Fulani ba su samu fahimtar juna ba shi kan shi yana cikin matsala. Bakin gate din ya fito ya tsaya yana danna wayarsa, number Rahma ya kira tai ringing har ta katse ba a daga ba, ya sake kira ba a daga ba ya san wannan baya rasa nasaba da fushin da take da shi, sai kawai ya aika mata da sako. Jin motsin mutum da yai bayansa, zuciyarsa ta raya masa Ataa dan yasan ita kadai zata masa haka duk duniya sai kawai ya saka hannunsa ya rikota ta baya ya juyo da ita, sai ta saka dariya.

“Mi ya kawo ki nan?”

“Naga lokacin da ka zo gurin Ammy ai sai kuma ka  koma”

Kallonta yai sai kuma ya kalli gate din gidansu Kamal a take zuciyarsa ta raya masa cewar Kamal zai iya fitowa ya ganta, and abunda ya fi tsana a yanzu wani wanda ya tana son Ataa ya ganta ko, a duk lokacin daya tuna cewar Ataa ta furta masa cewar tana son Kamal sai ya ji ba dadi.

“Koma ciki nima Nasir na ke jira”

“To mu jira shi tare miyasa ka fasa shigowa ciki?”

“Kunyar Mama na ke ji, ke ma ki je ciki Mama Fulani na son magana da ke”

“Ni?”

“Yes shiga gida mana”

Ya fada mata calmly yana kallon cikin kwayar idonta, wani irin kaunarta yake ji cikin ransa.

“I Love you”

Ya fada mata a hankali, sannan kama hannunta ya rika sai kuma ya saki ya tura hanninsa ya bude mota kofar gate din, har ta juya ta shiga Muhseen ya fado masa a rai sai yai saurin bin bayanta.

“Babyna karki je yanzu zo ku yi magana da ke a mota”

Gaba yai zuwa gurin motar ta biyo, jinginawa tai jikin motar shi kuma ya tsaya daga gabanta yana kallonta from head to toe wani dadi yake ji wai cikinta ne a jikinsa.

“Babyna gobe Mama za ta tafi ko?”

“Eh amman da ni zata tafi ai”

“Ni kuma ki yi yaya da ni?”

“Sai na je da kai”

“Ba a zuwa da babba yawo”

“Sai ka zauna har mu dawo”

“Za ki iya tafiya ki bar nan?”

Sai tai shiru, tai kasa da kanta.

“Babyna kin ga kina da ciki? Kuma cikin nan sabo maganin ma yanzu za ki fara sha idan na siyo, kuma kin ga ciki yana son kulawa musamman sabo, bana son ki yi tafiyar nan dan Allah”

Ta lake kafada tana turo baki.

“Ni gaskiya ina son na ga yan'uwan Mamana kuma su ma za su so ganina ai”

“Ciki be so jigila ai da yawan zirga zirga idan yana yaro, ba za ki iya kula da shi yadda ya kamata ba”

“Ai sai muje tare idan ba ka yarda da ni ba”

“Daman ai ya kamata na je saboda na san iyalinki kuma su ma su san ni amman wannan cikin ne ya saka na canja tunani”

“Ni gaskiya ina son na je, kuma Nana ba zata ji dadi ba idan ban je ba”

“Ba na ce ki daina ce mata haka ba?”

“To Mama”

“Idan na ce zan biku yanzu ai ya zama rashin kunya, kuma idan muka je can ba guri daya za mu tsaya ba, kin ga dole kije nan kije nan ana nuna miki dangi, Wallahi Ataa cikin nan a jikiki kawai yake amman jinshi na ke a cikin cikina, ni da akwai yadda za ayi da an maida min shi ke kije ki yi ta abunda kike so, ba ki san yadda na ke jin cikin nan ba ne”

Ya fada cikin yanayin damuwa, domin har ga Alla shi gani yake idan tai wata wahalar zai iya rasa cikinsa. Dariya tai masa sosai kamin ta ce wani abu suka ji horn a bakin gate din gidan, mai gadin ya bude wanda hakan ya bawa Nasir shigowa cikin gidan da motarsa. Ataa ta maida dubanta gurin motarsa har ya faka motarsa kusa da Ta Aliyu ya bude ya fito, Aliyu can't take his eyes on Ataa sai da Nasir ya fito daga motar sannan ya juyo yana kallonsa.

“Madam congratulations”

Aliyu ya kalli Ataa wacce tai kasa da kanta tana jin kunya shi kuma yai murmushi yana saka hannunsa aljihu.

“Ina wuni”

Ta gaisheshi cike da kunya.

“Lafiya kalau ya jikin na ki”

“Na ji sauki”

ta juya da sauri ta nufi bangaren Mama Fulani a lokacin ne Muhseen ya fito daga part din ita kuma ta shiga.

Aliyu ya bude motarsa ya dauko takadar maganin ya mikawa Nasir.

“Zaka saka a binciko mana wannan, na so na siya asibiti kuma ban samu dama ba”

“Ka ce kana son mu tattauna”

Nasir ya fada bayan ya karbi takadar.

“Yeah zancen tafiyar nan ne Nasir bana son zuwanta, kuma na rasa yadda zan shawo kan abun, ga shi kuma Mama Fulani ta ki yarda tai magana da Mahaifiyarta, and you know Momy ba za tai ba”

“To kai miye damuwarka da zuwanta? Ba abun farinciki ka ne ba sai ka je ka ga danginta su ma kuma su ganta”

“Na sani ai, Nasir cikin anan kasan karami ne”

“Aliyu ba akanka aka fara ciki ba, wannan ba ma reason ba ne kuma ka san ba ka isa ka samu Mahaifiyarta da wannan maganar ba, dama daya ce da kai ka bita ku tafi ka ga danginta idan ma da kai ba za a barta ta dade ba, sai ku dawo abun ku sai kuma ta haihu, amman idan za ka iya convince dinta da yarda ta zauna then fine”

“Ai ba zata yarda ba ne”

“Kai ma ai kasan yadda take dauki ganin yan'uwanta kamar yadda kake daukin cikinta”

Aliyu yai murmushi domin shi kadai ya san abunda yake ji akan cikin nan nata.

“Gobe fa za ayi tafiyar”

“Shirinka ai ba shi da wahala sai ka shirya kawai ka bi su”

“Babba da ni”

“To ya ka iya kauna ce sila”

Dariya Nasir yai yayinda Aliyu kuma yai murmushinsa da ya saba.

***      ***      ***

After fitar Aliyu Mama Fulani ta dauki wayarta ta kira Momy ta labarta mata abunda ya faru tana rokon ta yi ma Nana magana saboda ta fi ganin kimarta sama da ita, kuma tana ganin kamar ran Aliyu ya bace saboda ta ce ba zatai maganar ba.

“Wannan aikin ai na ki ne Fulani, ke da danki akwai wanda ya isa ya shiga tsakaninku?”

“Da dai ace duka sannan be faru ba da zan iya yin komai amman yanzu bana da wannan yancin”

“Ki manta da abunda ya faru, dukan abunda ya faru kin aikata ne a cikin rashin sani da kuma rashin tunani, daga d'an ki har ke kun yi wa talaka da talauci wata gurguwar fahimta ne, ba ku ganin kimar wanda ba shi da shi matukar mutum talaka ne ba shi kima ba shi da yanci a gurinku, shiyasa bana son munana kiyayyah ko tsananta soyayyah wata rana wanda kake ki ne zai dawo masoyinka wanda kake so kuma ya zama makiyinka, tun daga lokacin da Nasir ya labarta min zancen samun cikin na ga ba ki kirani ba na san ba ki cikin jindadi, ba kuma na samun cikin ba sai na kunyar abunda kika aikata, a yau duk wata naira da izzar dukiya da kike takama da ita Fulani Ataa ta damata ta shanye tun da kuwa Kakanta ne mai wannan arzikin, kuma na jidadin hakan wata kila da ba ta haka abun ya zo ba da har yanzu ba ki gane cewa akan kuskure kike ba, wata kila da har gobe ba zaki yi nadama ba balle a ranki kiji ko cewar kin aikata wani abu da ba daidai ba, na tabbatar da Ataa ta yi arziki ne ta hanyar d'anki da har jibi sai kin mata gori kuma kina ta kallinta kallonta da wannan tambarin na talauci wanda ba ita tai ma kanta shi ba, amman da Allah ya so nuna miki isarka da ikonta sai ya kawo wanda daga ke har Rahma za ku zauna a karkashin inuwarsa kuma ku wayi gari jininsa kuke wulakantawa”

Tun da Momy take maganar Mama Fulani take hawaye ko wani harafi da za a hade da dan'uwansa ya bada ma'ana sai da ya taba zuciyar Mama Fulani.

“Abunda ya faru ya riga ya faru, ki manta da komai ki maida komai ba komai ba, ki murje ido ki nunawa Ataa kulawa da kauna, domin su ne kadai abunda take bukata a yanzu, har yanzu akwai abubuwan da Ataa ta rasa, ilmi, iya mu'alama da mutane, zamantakewar rayuwa, girki da kuma zaman aure, Ataa yarinya ce da har yanzu bata wayancin wasu abubuwan ba, za ki iya maye mata gurbinsu a yanzu cikin hikima za ki nuna mata soyayya da nadamar abunda kikai, ko ba yanzu na sani dole wata rana za ki so Ataa ko ki zauna da ita dan dole tun da danki take aure, Fulani wannan ya iashe ki izna talaka ba abun wulakantawa ba ne, ko da ko ba ta irin sigar da Ataa ta zo miki ba, ba ki san inda wani talakan zai taima ke ki ba, ita rayuwar duniya makaranta ce dukiya da talauci kuma dukansu jarabawa ne ya kamata ki gane wannan”

Mama Fulani ta gyada kai kamar Momy na gabanta. Sannan ta saka hannunta ta share hawayenta .

“Na gane, amman har yanzu ina jin tsoro kuma ina kunya sosai”

“Wallahi ki gode Allah daya nuna miki haka tuna a yanzu ba sai da kika fada wata mummunar rayuwar ba, kuma ya saka miki saduda a take, daman can ban ga wani abun dagawa a dukiyar da zaka mutu ka barta ba, da arzikin da ba zai iya hana ka ciwo ko tsofa ba balle kuma mutuwa, yanzu dai abunda ya fi ki tashi da kan ki kije ki yi magana da mahaifiyarta ki yi kamar komai ba faru ba, ni kaina bana ra'ayin zuwanta gidan a yanzu, domin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login