Showing 183001 words to 186000 words out of 225640 words

Chapter 62 - Zaki Book 1 Hausa Novel Complete

abin ma na shiga nai wanka ina fitowa ya shiga kamin ya fito har na shirya daman can shine ba mai wahala ba ne, shi ma agaggauce ya shirya muka fito tare muka shiga motar. Ba zan iya fadar ungwar da muka je ba, domin ban san ko'ina a cikin garin Abuja ba, sai dai zan iya kwatanta da unguwar manyan mutane domin ta wani bangaren ma tana kama da Las Vegas irin rayuwar nan ta ba ruwa ko da kowa. Gaban wani katon gate Aliyu ya faka tsaya ya danna horn sai ga wasu manya kuma kanttin maza sun bude masa gate din, da sauri na rike hannun Aliyu sai yai murmushi ba tare daya kalleni ba, manyan motoci a cike a gidan na alfarma, bayan motocin ya faka motarsa ya fito ya zagayo inda nake ya bude min na fito daker domin ni gaba daya tsoro ya gama kama ni. Hannuna ya rika ya nufi wani guri da ni da alama shi m be san kan gidan ba, domin kuwa sai da ya kira wayar Abbah ya fada masa mu na waje sai aka turo dogare ya zo ya tafi da mu.
Cikin wani irin katon falon muka shiga mai kama da fada, komai na falon mai tsada ne da tsari irin manyan sakuna. Ganin hoton Mai martaba sarkin Agadaz yasa hankalina ya kwanta na fahinci cewar a gidansa ne muke, na yi zaton a falon za mu tsaya sai na ga mun shiga wani falon mai kamar wacan, haka muka wuce falo uku sannan muka iso cikin wani madaidacin falo, a nan na hango sarkin hakimce a akan kujera, babu rawani a kansa kamar jiya sai dai yana sanye da alkyabar sarauta irin mai tsadar nan ga takalmin sarauta kafarsa, Daddy's Rahma na gefe zaune kasa daga dama kusa da Abbah, da sauran jikokinsa, Nana kuma na gabansa kanta a kasa tana ta sheka kuka gwanin ban tausayi da alama gafararsa take nema.
Karasawa nai gurin Nana na zauna na dafata Aliyu kuma ya zauna kusa da Abbah yana mikawa mai martaba gaisuwa shi kuma ya daga masa hannu kawai.

“Ina jin kunyar ka Mai Martaba saboda abunda na aikata, ban san cewa na aikata babban laifi ba har sai da na rasa a kusa da ni na fara shiga damuwa da bakinciki......”

“Shin abunda kika be zame miki darasi ba?”

Mai martaba ya tambaya da kansa.

“Ya zame min, na rasa komai saboda babu kai a rayuwata, na rasa gata na rasa muhallin, abincin da zan ci sai na yi bara mai martaba, gida gida na ake bi ina rabawa na zauna, har na kai ga wanda aka ga wanda aka wulakanta ni kamar karya, kuma maciji ya tsare ni, Ataa tai ta dawaniya da ni da ta kai ni asibitin sai akai amfanin da rashin kowa na mu aka cire min koda aka sakawa yar wanda ya wulakanta mu saboda rashi, Mai Martaba da koda daya n ake rayuwa saboda rashinka da kuma dangina a kusa da ni, Mai Martaba aka a kulle Ataa a gidan yan sanda saboda ba mu kowa, na rasa na da na biyu da na haifa a gurin baran kudin neman min lafiya, Mai Martaba shin duka wannan ba darasi ba ne? Da ban bijire maka ba da ban ki bin umarninka ba da duka wannan abun be same ni ba, ba ban bata maka rai bada nawa bacin rai be kai haka ba, da ban gudu na barka na bar dangina ba da wani be isa ya wulakanta mu ba”

Ta fada cikin daga murya tana kuka sosai nima kukan na ke ina rike da hannunta.

“Da duniya tai miki wa'azi miyasa ba ki koma cikin danginki ba?”

“Saboda zuciya na fada ba zaka taba yafe min ba, ba zaka taba karbarta ba, masarautar da na saka a kunya na gudu na bari, idan na shiga wahala na dawo be kamata ta karbe ni ba, ban cancanci ko kallon fuskarka nai ba Mai Martaba, amman na barwa Ya ta mawasiya na fada mata bayan raina ta neme ku ta nema min yafeyarka da duka dangina”

Shiru Mai Martaba yai na tsawon lokaci kamar baya gurin, falon yai tsif baka jin ko da numfashin kowa.

“Ban taba jin na tsani jinina ba, ban taba jin kin jinina ba ko da ko zai kashe wani ya sake kashe wani jinina jinina ne, kuma ina jinsa a cikin jinina..... Bayan neman ki da masarauta tai na kwana biyu, sai na goge sunanki a babin nema har a bada, na bar abunda kika aikata da kuma son ki a zuciyata,... Na yi tunanin idan wahala ta same ki za ki tuna da danginki ki dawo..... Da ace yau mahaifiyarki ta fadi ta mutu da ta mutu da bakincikin da kuma bakincikin guduwa ki barta, babu daren da bata begenki... Idan kowa ya taru sai ta ce kowa yana nan amman ban da Asma'u... Shin kaunar uwa kadai be isa ya saka ki nemi danginki ba......?”

Daya bayan daya yake maganar yana kallon Nana.

“Ina jin kunyar kaina Mai Martaba, ina ina nadamar abunda na aikata, bakincikin guduwa na bar ku yana nan a zuciyata, kunyar haduwa da ku ta saka na yanke kaunar daga neman yafiyarku a raye har sai bayan rai na, Ka yafe min Mai Martaba ka tausayawa min dan Allah, na sani ko yanzu ina daf da mutuwa saboda lafiyata bata ishe ni ba”

Duk da yaren buzanci suke wannan maganar ita da Mai Martaba... Shiru ya sake yi na wani lokaci sannan ya ce a katse.

“Na dade da yafe miki Asma'u, na dade da fada a gaban kowa kuma na fada a zuciyata cewar ko ina raye ko a mace na yafe miki duniya da lahira”

Da gudu ta tashi taje ta fada jikinsa ta rumgumeshi tana kuka, sai yai murmushi kowa da ke falon sai da tauyasa kuma yai murmushi ban da Daddyn Rahma da baya cikin natsuwarsa. Kuka sosai Nana tai nima nai sannan muka share hawayen mu ni da ita. Bayan komai ya lafa muna kokarin shiga natsuwar mu ne. Mai Martaba ya sake gyaran murya da yaren hausa da baya fita sosai ya ce

“Na yi hakan nan ne a gaban ku saboda ku ma ku zama shaida kuma nasan dukanku za ku son jin gaskiyar alakata a Asma'u to yanzu kun ji, ina son kowa ya zama shaida na yafewa Asma'u abunda tai min, Allah ma ka zama shaida na yafe mata duniya da lahira”

Tsakanin ni da Nana sai na rasa wa yafi wani farinciki ni ko ita. Daddyn Rahma ya daga hannunsa alamar yana son yai magana da kai martaba sai gumi yake cikin asiri.

“Mai Martaba na ce kan sai zancen nema mata hakkinta a gurin Doc Asim na cire mata koda da yai”

Kallonsa nai yadda yake maganar muryarsa har rawa take.

“Allah sarki ashe rana zata zo irin wannan dakai da bakinka zaka bude baki ka ce a nemawa Nana hakkinta? Bayan duk irin cin mutunci da wulakancin da kai mana? Waenne kalar mutane ba ka turo sun zo sun watsa mana kayanmu sun koramu ba saboda kawai mun raba a kangon gidanka ka ce mu muka janyo maka maciji a gida ka karemu ka wulakanta mu, idan har za a hukunta Doc Asim to har da kai za a hukunta domin kodar da aka cirewa Nana yarka aka sakawa”

Na fada cikin kuka. Sai shi ma ya fashe da kuka sosai kamar ba shi ba.

“Wallahi Allah ya sani idan na san cewa ku zuri'ar Mai Martaba ne ba zan taba muku haka ba, Wallahi ko shara kuke agidan Mai Martaba ba zan iya wulakanta ku ba, walle har ace jininsa habawa..... Ba hali na ba ne, ko korar da aka muku ni sau daya na fada na ce a fada muku ku nemi wani gurin ku zauna, Wallahi Hajiya ce tai ta turawa aka rakura muku, ita ma kuma basan cewa jinin Mai Martaba ba ne da ba zatai muku haka ba, Wallahi tun jiya da na fada mata abunda ya faru tana can kuka take yanzu haka..... ”

Yadda yake kuka abun ko kyau babu domin babban mutum be sha'awa da kuka ballantana shi da yake wani rakeken kato, ni dai sai kallonsa n ake da takaici a raina.

“Wanene Doc Asim to?”

Jikan Mai Martaba ya tambaya cike da mamaki. Ni kuma sai na amsa masa

“Wani ne, wani likita ne wanda na kai Nana asibitinsa lokacin ba mu da kudi sai ya ce zai mata tiyata kyauta ya cire dafin maciji a jikinta ashe yaudarata yai ya cire mata koda, ya bani wata takardar na saka hannu ashe ta siyarda kodar ce ban sani wai saboda ba ni da ilmin komai, sai da ya tambaya ba mu da kowa na ce nasa eh shine ya cire mata koda, haka mukai ta jinya bata warke ba, sai na kaita wata asibiti aka duba aka ce kodarsa ce ya cire na kai kararsa gurin police yasa aka rufeni wai ina son bata masa suna, sanadin hakan Nana ta tashi mutuwa har sai da Allah ya kawo wannan Aliyu ya taimake mu ya kaita asibiti ya ba mu ci da sha da gurin zama”

Har lokacin da nake maganar cikin kuka Daddyn Rahma ma kuka yake yi.

“Wannan ba tsakanin mu da shi ba ne, tsakaninsa da Shugaban kungiyar likitoci ne”

Shine abunda Mai Martaba ya fada a takaice fuskarsa na nuna bacin ransa karara....



*Z A K I -it's not free, pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence via 08036126660*

*Ina mata son rage kiba? Ina mazan da kiba ta hana su sukuni? Ina masu jikin yai kyau kamar na yarinya? Ina masu fama da kujera ko wani ta bo a fuska? Ina masu fama da hawan jini? Masu diabetic? Ag cera an gwada yayi an tantance ingancin babu shakku ko kadan. AG cera ya zo domin ya temaki garkuwan jiki da kuma lafiyar jiki. Sinadari ne wanda ze magance matsaloli da dama wadanda suke hana garkuwan jiki aiki yadda ya kamata ko kuma yake rusa garkuwan jikin ita kanta.*
*Cututtukan zamani daban daban sun sa mutane gaba kuma magance su yana da wahala; irin ciwon Sugar, hawan jini, ciwon sanyin kashi, ciwon gabobi da sauran su. Haka ma cutukka irin wadanda suka shafi fatar jikin wadanda sun hada da kyasfi, pimples, takurewar fata, rakainuwar fata da kuma haske da kyallin fata duka ana shan AG cera kuma yana temakawa wajen magance illolin nan. Mutane masu fama da rashin karfin jiki wajen kwanciya da iyali da kuma mata masu fama da yawan ciwon mara lokacin al'ada ta karshen wata suma baa bar su a baya ba. A takaice dai AG Cera yana temakawa wajen magance cuttukka daban daban wadan ke damun mutum. Domin karin bayani ku tuntuni mu a wannan number +60167474649 ko kuma ku ziyarci shafin mu http://agnutritioninternational.com.*
Wani irin sama yake da kafafuwansa yana boxing da hannu kamar wani karamin yaro, sai kuma ya sauko saman gadon ya nufo ni da wata irin far'a ya daga ni sama yana juyawa da ni, kamin ya rumgume.

“Oh Allah na”

Ya fada yana matseni har ina jin zafin matsar saboda yadda ya rike ni da karfi.

“Aliyu minene?”

Be bani amsa ba, ya sake ni ya fadi yana sujada, sai kuma ya dago ya ya rike ni yana ta kallon fuskata murmushi ya gama cika masa fuska, hade bakina yai da na shi ya fara min abunda ya saba wato kiss sannan kuma ya cire bakin ya daga kansa kama.

“Wayyo Allah na, baby ban san abunda zan yi ba yau, kar na haukace”

Har lokacin da yai wannan maganar kansa a sama yake yana kokarin maida ni kirjinsa ya rungume. Ni dai sam ban gane dalilin wannan farincikin ba, da farko ganin layin biyu yasa na tsorata na fara tunanin ko dai ina da wani ciwon ne sai dai yadd Aliyu yake far'a yasa na daina zargin ciwo sai dai kuma ban kawowa raina komai ba, sai mamaki kawai na ke.

“Baby i love you, I love you Tomorrow, i love you everyday, i love you so so very much”

Na san abunda I love you, da everyday da tomorrow take nufi, kuma na jidadin furtasu a gareni da yai hakan yasa ni na rumgumeshi da duka hannayena, ina jin kamar nima na fada masa haka kuma ina jin kunya. Ji nai ya dago kaina yana ya sumbatar ko'ina a fuskata da jiki kamar mahaukaci sai kuma ya sake rumgume, sake ni ya sake yi fara rawa a gurin yana jujjuyawa kamar wani mace, sai kuma ya rikoni yana cilastani ni ma nai rawar.

“Very Very soon Baby za ki zama uwar Baby”

Ya fada yana rike da fuskata har da wani turo min bakinsa yake kamar nai yi yarinya karama magana da zolaya.
Uwar baby kuma ban fahimce shi ba.

“Kamar ya”

Juyar da ni yai ya zamana bayana ne a kirjinsa sai ya saka dayan hannunsa yana shafa cikina.

“Kamar haka, idan kin haihu”

Zaro ido nai sai yanzu na gane komai barobaro da sauri ya juyo.

“Ina ciki kenan?”

Juyar da ni yai ya rungume.

“Muna da ciki dai Baby not just you, ko ma na ce ina da ciki Baby i love you”

Ya fada saitin kunnena. Sai na fashe da kuka.

“Aa yanzu kowa sai ya san abunda ya faru ko? Idan aka gan ni da ciki”

“Daman ai an san dole wani abun zai faru”

“Amman dai akwai kunya kuma ciki da wahala”

“Ba wani wahala, kunya kuma ai tunda kika yarda kika zauna gidan miji ta wuce”

Ban san dalilin rashin jindadin cikin ba, sai ma tsoro daya kama ni yo ni ya ma zan yi na haihu? Kuka na fara bana wasa ba tun yana rarrashina a hankali har abun ya koma bashi tsoro.

“Haba Babyn wannan fa abun farinciki ne, wannan shekarar ina cikin ta tara da aure amman ban samu haihuwa ba sai yanzu, Momy Mama Fulani Abbah Daddyn da duk family and friends da sisters idan suka ji dadi za su ji kuma su so ki sosai”

“A a nidai ba yanzu ba nidai bana ma so gaba daya”

Zaunar da ni nai saman gadon ya zuba min ido yana ta kallona.

“Dan girman Allah Babyna ki daina kukan nan, kar kukan ya cutar da abunda ke cikinki”

“Ba zan iya iya kallon kowa ba idan nai ciki, kuma ba zan iya haihuwa ba”

“Ciki ai kin riga kin yi, yi hakuri ba za a sake wani cikin ba”

“Da gaske?”

Dariya yai ya gyada min kai. Sannan na sausauta kuka shi kuma ya tashi yaje debo min ruwa. Yana fita na daga rigata na leka cikina sa nai sauri na rufe.


ALIYU POV.

Ya sauko downstairs wayarsa a hannunsa yana kiran Nasir, wannan karon be jira Nasir ya fara magana ba kamar yadda ya saba yana kiran daukar kiran Aliyu ya ce

“Congratulations to us na kuma zama Daddy nima na yi ajiya a cikin Ayusher”

“Wowooooooooooooo Aliyu are you serious? Oh my God”

“Na rantse da Allah Nasir har ban san irin farincikin da zan yi ba, na rasa abunda zan yi Wallahi ji na ke kamar na hadeye Ayusher a yau”

“Wannan abun murna ne a garemu gaba daya ai, amman Momy ta ji da Mama Fulani?”

“Ban fadawa kowa ba sai kai, nima yanzu na ga result din”

“Ni zan yi musu albishir karka ce zaka fada musu na san baka da kunya”

“Ai na zancen kunya a nan Nasir, wane irin kunya a gurin farinciki? Ai ba wannan zancen shi dan na fada na ce tana da ciki kuma wani abun kunya ne? Ita ma yanzu ta gama kuka wai idan suna ji zata ji kunya”

“Ai kai ba saka gane ba ne saboda ka saba yin abu normal ne”

Murmushi Aliyu yai ya kashe wayar, har ga Allah shi be ga abun kunya a fadar matarsa ta yi ciki ba, shi ba duk abunda ya san idan ya aikata ba haramun yai ba to be ga abun jin kunya a ciki ba, da dai zina ya aikata ko wani alfasha shine abun jin kunya, domin shi ya fi dacewa ka ji kunyar Ubangijinka sama da na kowa. Freezer ya bude ya dauko ruwan gora ya zuba sai da ya sha dan ya ji yanayin sanyinsu kar su cutar da abun cikinta sannan ya sirka da wasu ruwan sai ya dauko kofin ya dawo dakin da take. Inda ya barta a nan ya same ta zaune da kansa ya kai mata ruwan a baki yana bata a hankali har ta sha rabin kofin sannan ya aje ya zauna kusa da ita ya zuba mata ido. Be san abunda zai mata ba, rumgumatar ba zai wadatar da shi ba, kallonta ba zai wadatar da shi ba, saurarenta ko yi mata wani abu ba zai wadatar da shi ba, yana jin cewar hadeye ta kawai zai yi ta zauna tana cikin cikinsa ita da abunda ke cikinta sannan hankalinsa ya kwanta sai dai kuma babu wannan damar ya rasa inda zai sakata tsabar farinciki.
Haka yai zaune ya sakata a gaba har aka kira sallah la'asar sannan ya sumbaci goshin nata da cikin ya fita zuwa masallaci, daga masallacin ya wuce restaurant ya siyo musu abinci, ya so ya kira ya tambaye ta abunda take so amman babu yadda zai yi tunda bata da waya. After restaurant ya wuce wani babban shago ya siyo mata sabon phone mai tsada wacce ake yayi sannan na nufo gida, ko da ya shigo ya ji motsinta a kitchen sai ya nufi kitchen din kai tsaye taliyar indomie ya tarar tana zubawa a plate tana murmushi.

“Yunwa na ke ji sosai shi ne na dafa indomie”

Ta fada masa ganin ya tsaya yana kallonta da murmushi.

“Wow yau Gimbiyata ta yi aiki da kanta bari na dan dana na ji, ashe kin iya girki ko?”

“Eh na iya tuwo na iya dafaduka na iya dafa taliya na iya sararafa kanzo na iya shimkafa da miya kuma na iya da wake, amman ban iya amfani da wacan abun ba sai na daka a turmi”

“Wow amman dai ai ba sai kin yi aiki da yawa haka ba”

Ya karasa kusa da ita

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login