Showing 213001 words to 216000 words out of 225640 words

Chapter 72 - Zaki Book 1 Hausa Novel Complete

kila da ace ta tafi a lokacin da be aure ni da zai fi shiga damuwa sosai, a kokarinsa na faranta da saka ni nishadi ni da abunda yake cikima kamar yadda yake fada, sai shi ma ya saka kansa ba tare da ya sani ba, ban ayyanawa a raina cewar wata rana Hamma zai so ni kamar haka ba, kuma zan rayu a gidansa daga ni sai shi sa abunda zan haifa inda da rai da rabo.
  Kusan kullum ina waya da Nana wacce na ke kira da Mama a yanzu saboda canjin da Hamma yai min tama tambayar lafiyata da ta Hamma na fada mata muna nan lafiya, har take fada min akwai yan'uwa da yawa da ban gani ba sai idan komai ya laba na dawo, ni dai sai dai na amsa da to amman na san yadda Hamma yake daukin cikin nan da ni ba zai iya barin nai nisa da shi ba, idan muna gida a jikinsa na ke wuni idan kuma mum taho gurin Momy idonsa na kaina da na yi wani abun da ba daidai ba sai yi kin alama da ido. Momy ma tana kula da ni har zaman da ke kusa da kofa sai ta fada min wai mai ciko bata zama a bakin kofar dakin ko kusa da kofa aaboda aljanu, ni dai abun har dariya ya ba ni sai dai ban yi a gabanta ba, ni dai ban taba jin haka ba wata kila saboda ban zauna da tsofi ba ko kuma ban yawance akan irin waennan abubuwa, wata kila kuma saboda suna son cikin ne suke ganin komai be dace nai yi ba. Shi kanshi Hamma da safe sai ya min addu'a har a cikin haka ma da dare idan zan kwanta. A ranar da muka wuni idan Momy take masa maganar karatuna sai ya nuna mata baya so.

“Momy ga ciki kuma ace tai karatu? Haba abun ai sai yai dawo, da karatunta zan ji ko cikin?”

“Wai dan wajen Fulani kanka farau ciki ne? Karatu ko na islamiya sai ta fara da shi a yanzu, saboda kula da kanta da addu'oi, ai ilmin mace yana da muhimmanci ba wai ko dan aiki ba, saboda kula da yayanka ma ta koya mu su, kuma idan babu ilmi tarbiyar ma ya kake tunanin za ayi ta? Miyasa ake son auren mace mai ilmi ba dan wannan ba”

“Momy ki ma kinsan dan wajen Fulani da Mama Fulani komai na su dabam ne, gaskiya ni ba zan iya daukar wannan ba, ke ma fa Momy kin san yadda ake bukatar abun nan yanzu kuma ki kawo wasu maganganu haba dai Momy”

“Haba dai? Yanzu kana ganin idan a gurin Kakanta take kuma ya samu labarin bata iya komai ba batai karatu ba zai zuba mata ido haka? Yanzu ka fi son tai ta zaman banza a wata bakwai ko takwas da ke tafi wanda za tai nan gaba? Ai ya kamata ka saka ta ilslamiya ko kuma na nemo malamin da zai rika karantar da ita a gida, in so shi bokon idan ta haihu sai ta yi, baka sani ba ma ko tana da burin yin wani abu da karatunta”

Momy na fadin hakan ni kuma nai karaf na ce.

“Eh ina son nai likita ko nurse abun na burge ni sosai Wallahi”

Harara ya watso min.

“Eh ba ri ki sake magana na buge miki ba ki a nan, haka nan za ki je ki yi karatun likita shekara nawa tare da maza?”

“Ai ansan ina da aure kuma zan rika saka hijab har da niqab ma”

“Ba za ki yi shirun ba? Ba ki san kyaunki hadari ne ba, kuma ba ki da wayo da za ki iya tattalin abunki balle har ki kare martabarki, ni ko ko tafin kafarki aka kalla aka yaba Wallahi zafi zan ji”

“Allah ya sauwake maka wannan bakin kishin daya cika maka zuciya, amman karatu kan dole ne tai yarinya ba za tai zama haka ba, kai ma da yarka ce ai ba zaka barta haka ba”

“Momy za tai karatu, karatuna yana cikin burin da na ke da shi akan Ayusher amman sai ta haihu ta yaye abunda ta haifa ya yi kwari sannan a fara maganar karatun shi ma idan bata samu wani cikin ba”

“Yanzu a maimakon zaman da za tai ai sai ka sakata ta fara daga matakin farko kamin ta haihu dan yai kwari ta san wani abu ka ga ci gaba kawai za tai”

“Momy mun ma kusa barin garin nan Abuja za mu koma”

“Ai a Abujar na ke nufin ka saka ta ba a nan ba, daman can sun fi makarantu masu kyau ai”

Na jidadi sosai da Momy ta tunatar da shi burina da kuma abunda na ke ta mafarkin samu shekaru da yawa, domin na ga kamar shi ya manta idan ma be manta ba to yana son shashantar da abun saboda kar dansa ko yarsa su wahala. Ni ko ban ga abun wahala a ciki ba domin bana jin komai ko aman da nake na dade ban yi ba sai dai yawan cin abinci da na ke sosai kuma akai akai.

“Shikenan Momy daman can na san ai ba ke ce Mama na ba, shiyasa ba ki goyon baya na, da Mama tana nan da yanzu ta saka baki ta tsaya min”

“Daman can ai kai ba dan ba ne, balle kuma yanzu da na samu yata ta, ga su Husna da Amina da Siyama sun ishe ni ga kuma Muhseen a gafe”

“Na kusa komawa gurin Mahaifiyarta na barki da su”

“Ai da ma kabar ta nan ta yi karatu ta koyi abubuwa da yawa kamin nan”

Dariya yai dan yana jin kamar ba da gaske Momy take ba, ni dai na yi yar dariya dan san Momy ta fada masa abunda ba zai iya ba ne.

“Tashi mu je gida”

Ya fada har lokacin be daina dariya ba, ita kanta Momy dariyar take dan ta san abunda ta fada ba mai yiyuwa ba ne a gurin Hamma. Muna shirin barin gidan kiran Wayar Mama ya shigo wayata da zumudi na daga na kara a kunne, ba ma kamar da ta fada min cewar gobe zata zo sai da n daka tsalle na dire saboda murna da yaren buzanci na ce.

“Haka nan kawai za ki zo Mama?”

“Aa saboda maganar likitan nan ne, gobe za a zauna da shi da ni da ke da wasu yan'uwana da Mai Martaba zai hado mu da su”

“Daman maganar tana nan?”

“Tana nan mana ai kinsan ba za a bari ba, tun kwana baya suka kira suna fadawa Mai Martaba suna son ganina da ke sai ya nemi a dan daga mana kafa saboda an yi ma mijinki rasuwa ni kuma bana ma kasar a yanzu”

“Amman na jidadi Allah ya kawo ku lafiya Mama”

“Amin sai mun iso”

A haka muka rabu ina ta jindadi zan ga Mama daman na yi marmarinta saboda na sabu da ita ban ma dauka zan iya daukar tsawon lokaci kamar haka ba tare da ita a kusa da ni ba, kuma har hankali ya kwanta haka.

“Mama ta ce tana nan zuwa gobe”

“Na sani ai”

Hamma ya fada abun sai ya bani mamaki sosai daman ya san da zancen zuwan be fada min.

“Ya akai ka sani?”

“Daddy ya fada min, kuma ina son ki ga Mama a ba zata ne shiyasa na kyale ban fada miki ba”

Na yi murmushi, Momy kuma ta yi dariya tana kallonmu cike da burgewa. Na y zaton zai ji kunyar Momy ya bar ni na bude motar da kai sai gashi ya bude duk kuwa da kasancewar Momy na tsaye bakin kofar falo tana kallon mu, sai da na shiga sannan ya rufe yai mata key ya danna horn aka bude mana gate.
Sai da muka fara tafiya sannan ya kama hannuna yana murzawa a hankali ba tare da ya kalleni ba.

“Hamma....”

“Babyna bana son Hamma nan”

“To ai ance ba a fadar sunan miji”

Murmushi yai ya kalleni sai ya kai hannun nawa a bakinsa yai min kiss.

“Then fada wani suna mai dadi, not Hamma sunan ma dariya yake ba ni”

“To me zan ce?”

“Ki kirkiro da kanki mana”

Na yi shiru ina ta nazarin sunanshi da zan bashi bayan Hamma da Aliyu.

“Z a k i”

Kyalkyalewa yai da dariya ya faka motarsa gefen titi ya riko fuskata yana kallona.

“I love you so much Girl ke duk abunda zuciyarki ta nuna miki shi ne daidai”

Na yi dariya, sai ya hada goshina da shi ya goga min hancinsa yana ta kallon cikin idona, hakan yasa na rumtse idon sai na ji lips dinsa saman nawa. Hakan yasa nai hanzarin bude ido sai yai min murmushi ya dauke bakinsa ya rike fuskata yana ta watsa da yatsansa a lips dina sai wani lumshe ido yake yana ta kallon bakin nawa yana hade yawu.

“Wani suna mai dadi dai, ba Zaki ba wanda ba za ki ji kunyar kirana da shi a gaban kowa ba”

“To amman ba yau ba sai na yi dogon tunani”

Dariya yai ya shafi fuskata ya tashi motar, kamar kullum yau ma sai da ya biya ya siya mana kaza da yoghurt sannan muka isa gida.
Sai da muka fara cin kazar sannan ya hada mana ruwan wanka muka shiga mukai tare.

“Ni fa na fi jindadin yin wanka ni kadai”

Na fada bayan mun fito ina daure da tawul kamar yadda shi ma yake.

“Wanka tare yana kara soyayya da kauna da rashin kyamar juna, Annabi ma yana wanka da iyalansa, kuma duk abunda yai ko ya ce ayi yana da fa'ida sosai a garemu da falala, kuma yana yi saboda ya zame mana abun koyi sosai, ni kin ga yanzu na saba yi da ke idan ina yi ni kadai ma bana jin dadi”

Dariya nai, na nufi gaban madubi ina gyara gashin kaina, sai ya zo bayana ya tsaya, yana kallona ta cikin madubi da cat eyes dinsa.

“Gaskiya na yi dacen mata”

Ya fada yana kai hannunsa ya shafa wuyana zuwa dantsen hannuna da yatsansa, wani yar na ji hakan yasa nai saurin juyowa, sai jin dariyarsa nai.

“Ba ki da wayo, ai ta nan ta fi min sauki ma”

Ya fada yana dauka ta cak ya nufi gadonsa da ni.




*AG cera ya zo domin ya temaki garkuwan jiki da kuma lafiyar jiki. Sinadari ne wanda ze magance matsaloli da dama wadanda suke hana garkuwan jiki aiki yadda ya kamata ko kuma yake rusa garkuwan jikin ita kanta.
Cututtukan zamani daban daban sun sa mutane gaba kuma magance su yana da wahala; irin ciwon Sugar, hawan jini, ciwon sanyin kashi, ciwon gabobi da sauran su. Haka ma cutukka irin wadanda suka shafi fatar jikin wadanda sun hada da kyasfi, pimples, takurewar fata, rakainuwar fata da kuma haske da kyallin fata duka ana shan AG cera kuma yana temakawa wajen magance illolin nan. Mutane masu fama da rashin karfin jiki wajen kwanciya da iyali da kuma mata masu fama da yawan ciwon mara lokacin al'ada ta karshen wata suma baa bar su a baya ba. A takaice dai AG Cera yana temakawa wajen magance cuttukka daban daban wadan ke damun mutum. Domin karin bayani ku tuntuni mu a wannan number +60167474649 ko kuma ku ziyarci shafin mu http://agnutritioninternational.com.*
Na farka cike fa far'a da kuma farincikin zuwan da Mama za tai, ban taba tabbatar da na yi missing dinta sosai na sai da na farka da kewarta. Hamma ya shirya mana abun karyawa ni kuma na gyara gidan a wauta taa na zata gidan zata fara sauka sannan ta wuce gidan Momy. Bayan na gama komai muka zauna muna karyawa sai ga Momy ta kira Hamma a waya tana labarta masa cewar Mama ta zo tana gurinta.

“Laa ba nan za ta sauka ba?”

“Shikenan sai ta sauka nan saboda ga ta ita mai ya ko?”

“Amman na dauka nan zata sauka, har ina shirye shirye girka mata wani abu”

“To an hutar da ke”

Ya fada yana jan hancina. Sai nai murmushi.

“Ita ma zan mata magana na ce tai maka maganar karatuna”

“Oh magana kika yi ma Momy tai min magana ko?”

“Aa Wallahi ita tai dan kanta,kawai dai ina son karatun ne kuma kai na ga kamar ba ka so”

“Ba wai so ne bana yi ba, yana ganin kamar karatun a yanzu zai iya zame miki matsala ko wahala”

“Wallahi ba wani Wahala bana jin komai fa kalli”

Na yafa ina daga rigar da ke jikina, sai ya kalli cikin ya kalleni yana murmushi.

“Ai a jikinki ake gani ba, nan gaba na ke miki nuna”

“Idan na ji da wahala nan gaba zan daina”

“Daman ai kin iya raki ai”

“Amman ni ai ina da kokari bana raki a komai ma”

“Ko”

Ya tambaya kamar mai magana da yar shekara uku babu dariya ko murmushi a tare da shi.

“Idan mun koma Abuja zaki fara zuwa islamiyar su da bokon da ke can, amman idan cikin ya kai wani mataki za ki saurara da zuwan har sai kin haihu, sannan ki cigaba”

Ban san lokacin da bar inda na ke zaune ba, na fada jikinsa ya rumgume shi ina murna.

“Da gaske Hamma”

“Ba na ce ki daina ce min Hamma ba?”

Ya fada yana jan lips dina.

“Ni dai amsa min da gaske?”

Ya gyada kai sai na kara rumgume shi saboda murna har da yi masa kiss a gefen fuska, shi kansa abun sai da ya bashi dariya. A ranar sai farincikina ya zame uku, na zuwan Mama da na case din Doc Asim da za ayi ga kuma zancen Karatu da Hamma yai min. Kowa ya ganni a wannan lokacin ya san ina cikin farinciki, har muka yi wanka muka shirya ban daina sake saken yadda zan fara karatun nawa ba.
Bakar a baya na saka shi kuma ya saka wani koren yadi mai kyau mai kamar boyal kuma ba boyal ba, ya saka bakar hula da bakaken takalmi karka so ganin mijina a wannan lokacin yayi kyau sosai fuskarsa har wani annuri take kamar wani ango, ni kaina sai da na kusa shashantar da kaina gurin kallonsa.

“Ashe kai ma kana da kyau”

Ya dube ni da duba irin na wasa da kuma mamaki.

“Oh dacan ba ki taba ganin kyau na ba sai yau? Ko dan ina yawan fada miki cewar kina da kyau?”

“Aa gaskiya yau dai sai naga kamar kana da kyau”

Hannu ya kai ya rikoni ya matse min kunne.

“Na fiki kyau yarinya ni da yan mata ke hari ma, ke ma ba kyau ne ya janyo ki ba, kina ga dan yaro kyakkyawa kika lake min har da addu'ar Allah yasa na so ki, shiyasa na kasa zaune na kasa tsaye sai da na kawo ki gidana”

Ban san lokacin da dariya ta subuce min ba, duk kuwa da irin zafin rikon kunnen da yai min.

“Da zafi sosai da zafi”

Na fada a lokacin da yake jan kunne nawa zuwa gurin motarsa.

“Yau ke za ki bude min motar na shiga”

“Saboda me?”

“Saboda ni ne Sarki”

“Amman ai kai ka saba bude min”

“Lokacin da kina sarauniya ba”

“Yanzu fa”

“Ni ne sarkin”

“Taya?”

“Gashi nan ke ma kin yaba kyau na”

Dariya nai na daka tsalle na cire hular kansa na watsa da gudu gaban motar sai ya biyoni ya gudunsa.

“Ke ba ki da kai ya za ki fara gudu da ciki”

Jin hakan yasa na tsaya sai kawai ya karaso kusa da ni ya karbe hularsa ya sake rike min kunne.

“Na gane ba ki jin magana Babyna”

Haka ya janyo ni har gurin motarsa ya bude min na shiga ya rufe sannan ya zagayo ya shiga mazaunin direba ya tashi motar muka dauki hanyar gidan Momy.
Ina shiga dakin Momy yai kan Mama da gudu na rumgumeta ina murna. Matan da ke tare da ita sai suka saka dariya suna ta kiran wai na cika kurciya, Momy ma dariya take tana fadin haka muke ni da Husna da Siyama kusan halin mu daya Amina ce kawai mai hankali, sai da muka dade a dakin muna fira ni har na manta da Hamma sai gashi ya shigo dakin da kunya ya gaishe su tare da musu fatar an zo lafiya sannan ya fita. Wani abun haushi abun mamaki Mama ta yi ma kowa tsaraba, a gidan sun daga kan Daddy har Momy da Amina Husna da Siyama kai har Hamma sai da ta siyo masa wata dakakkiyar shadda yar Agades amman ban da ni, nikan Nonon Ragumi ne kawai tai min tsaraba da shi. Misalin biyu saura na rana muka fito zuwa inda ake bukatar ganinmu, ni da Hamma a mota daya Mama kusa ta shiga wata mota da yan'uwanta maza suka zo da ita daga can inda suka sauka.
Ko da muka isa gurin biyu daidai, wani katon gurine mai kamar ma'aikata, yan'uwan Mama maza da Hamma suka shiga gurin da aka tana da domin sallah, ni kuma da Mama da wata yar'uwarta da ake kira da Mama Lattu muka shiga wani dan fili mai kamar dakin karatu mukai na mu sallah.
Ba mu zauna a dakin ba sai uku daidai domin bayan gama sallah sai da aka jira isowar wasu daga cikin wadanda za a zauna da su. Maza da mata ne da yawa a dakin za su kai su goma a dakin, sai wasu kujeru da aka jera can dabam wadanda aka nuna mata aka ce mu zauna, duk irin kusancina da Hamma na kasancewar mijina hana shi shiga akai a gurin, da kuma yan'uwan Mama sai aka hana su shiga, wai da mu kawai suke son su fara magana.
Inda Doc Asim yake zaune da dabam da inda muke zaune, sai kallona yake kamar be tana ganina ba, na kalleni ya kalli Mama wata kila mamakin rayuwarta ya kashe shi ko kuma mamakin kawo kararsa yake oho, sai dai a yanayin da ya ganmu daga ni da har Mama ya sam yanzu ba kamar da ba ce domin ta canja zane. Da turanci suka fara magana kamin dayan ya fara yi da hausa yadda ni da Mama za mu fahimta.

“Doc Asim ka san wannan?”

Sai ya kalleni ya gyada kai.

“Eh na santa”

“A ina ka santa?”

“Ta yi zaman jinya asibiti tare da mahaifiyarta a lokacin da ta siyar min da kodar mahaifiyarta”

“Ke kin sanshi?”

“Eh

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login