Showing 72001 words to 75000 words out of 225640 words
yana masa yawo a zuciya wanda be taba jin irinsa a rayuwarsa, har numfashinsa na fita da karfi wani na tura wani, ji yake kamar yaje ya bude motar ya fito da Kamal ya shake shi a gurin, sai kuma wata zuciyar ta hana shi, lokacin da Kamal ya fito motar ya budewa Ataa ta fito ya daga masa hannu yana masa sannu ji yai kamar ua narke a gurin saboda zafin rai da wani bakim haushi daya kama shi. Bayan Kamal ya wuce Ataa ne ta gagara shigowa gidan sai ya juya ya koma ciki ya tsaya, sai gata ta shigo hannunta rike da kudi dayan hannunta da ledodi gashin kanta ya kwanta luf kana ganinsa kasan ya sha gyara gwanin sha'awa. Be san lokacin daya isa gabanta ya kware mata ido.
“Ina kika fito?”
Ya tambaya muryarsa har rawa take.
“Kamal ne ya are ni”
Ta fada tana turo baki. Hannu yasa ya fisge ledar hannunta da kudin ya bude gate din ya fice ita kuma ta fashe da kuka ta durkushe a gurin. Kai tsaye ya tsallaka titi ya tura gate din gidansu Kamal ya shiga, kadan suka kusa yim karo da juna domin Kamal din ma ya nufo gate, sai Aliyu ya jefa masa ledar da kudin.
“Kar ka sake daukar ta ku fita, har ka bata kudi, ba irin yan matan Abuja ba ne, ka je can ka nemi sa'ar ka wannan aiki ta zo ba shashanci ba”
Da mugun mamaki Kamal yake kallon Aliyu yana karantar abunda ke zuciyarsa da kuma mamakin bacin ransa akan ya fita da ita har yana fada masa abunda be taba ba ko da wasa.
“Fita kawai nai da ita”
Aliyu ya nuna shi da yatsa.
“Na fada maka ba irin yan matanka ba ne, wannan na zama na farko kuma na karshe”
Aliyu na fadar hakan ya juya, sai Kamal yai murmushi.
“Zai zama na farko amman ba na karshe ba, miye naka a cikin dan na fita da ita? Kaji haushi ne?”
Aliyu ya tsaya cak kamin ya juyo yana masa wani kallon wulakanci.
“Abun kunya ne ma ace ka fita da yar aikin gidanmu, har ka kaita saloon a gyara mata gashi what a shame”
Kamal yai murmushi ya matso kusa da shi.
“Abun kunya ne dai kai a ganka kana fada kan yar aikin gidanku! Ni daman ai nasan daraja talaka ba kamar kai ba, miyasa kake fada akan na fita da ita?”
“Ba zan taba barinka ka lalata mata rayuwa ba”
“Na lalata mata rayuwa? Like seriously?”
Kamal ya fada yana dariya. Harara kawai Aliyu ya watsa masa ba tare da ya sake cewa komai ba ya juya dan ya fahimci bata lokacinsa kawai zai yi a nan.
“A da bana son ta kawai burgeni take, amman wannan abun da kai sai ya saka min son ta Wallahi”
Kamal ya fada yana bin Aliyu da kallon haushi. Aliyu be juyo ba har ya fice daga gidan cikin zafin rai yana tauna hakoransa har suna kara..
ZAKI
By Khadeeja Candy
25...
A gurin tunda bachi yai gaba da ni ban sake sanin inda nake ba sai kusan magariba, domin na farka ne a lokacin da ake daf da gabatar da sallah magariba, da sauri na sauka saman katifar naje Garden da katuwar rigata da tai min yawa nai alwala na dawo nan sai na rasa hijab din da zan dauka na saka nai sallah domin komai nawa na cikin jakar ya jike shakaf sai kawai na zauna a gurin na rumgume hannayena ina kallon kasa, ji nai an jefo min abu wanda hakan tasa ni zabura na tashi tsaye da sauri, Aliyu ne ya jefo mij Hijab hannunsa a jike da alama alwala yai shi ma, ban ce masa komai ba na dauki katon Hijab din na zuba na soma rama sallah la'asar sannan na gabatar da magariba. Bayan sallah isha'i Muhseen ya bude kofar ya shigo daure da plate din abinci da ruwa a kofin ruwa ya dire min a gabana, tuwon shimkafa ne miyar ganye da tea mai zafi a kofin.
“tashi ki ci abinci”
Na tashi ina ta leken kofar daya fito.
“Idan Mama Fulani ta gani zata maka fada”
Murmushi kawai yai ya matsar min da plate din.
“Bana son tuwon”
“To ga Tea
Ya dauki kofin ya mika min, ni kuma na karba na kai a bakina, ina cikin sha Mama Fulani ta shigo ta kofar gaba sai nai saurin aje kofin na mike tsaye shi ma ya mike tsaye yana kallona da mamaki kamar be ga mahaifiyarsa.
“Muhseen ban ce karka sake shiga zabgar yarinyar nan ba? Ban isa da kai ba ne”
“Haba Mama wane irin ba ki isa da ni ba kuma? Amman zancen na fita hanyarta be taso ba, haba Mama ke ma ai ya kamata ki fahimci wani abu”
“Na gane me? Muhseen kana da hankali kuwa? Kasan abunda kake yi? Abun kunya kake son ka dauko mana? Yar aikin gidanku? Ai ko ganin ka akai kana mata magana abun kunya Wallahi a garemu kaskantacciyar yarinya kamar wannan?”
Shiru yai ba ce komai ba sai ta juya ta fice daga gurin, ni kuma na koma na zauna na kasa sanye tea din.
“Kar abunda Mama tace ya dame ki haka take wani lokacin idan ranta ya bace, shanye ki ba ni kofin”
Daga idona nai na kalleshi.
“Idan kana min abunda Mama Fulani bata so, zan ka iya samu matsala da ita, kuma ni ma zaka ja min wata matsalar, wata kila ta koreni ko ta dake ko wani abun dabam”
Lankwashe kafafunsa yai ya zauna gabana yana kallona tare da soma min magana a hankali.
“Ban taba zabar abokin rayuwa a wajen mu'amala ta abota ko ta aiki ko wani abun ba, ban taba gabatar da wata mace a matsayin wacce na ke so ba, duk da kasancewar akwai matan da zan gani na ji sun kwanta ko kuma su nuna ra'ayinsu a kaina, a talaka da mai kudi duka daya ne a gurina, domin duka mutane na dauke su, banbanci kawai su suna da kudi mu kuma bama da su, abota da talaka ko auren talaka ko zama da talaka ba zai taba damuna ba, matukar ni zuciyata ta kwanta da mutumen”
Shiru yai yana murmushi sannan ya cigaba
“Mama tana da wani hali da ni kaina bana son shi, ni kaina bana son irin rayuwar da take na kin jinin talaka, dana daya daga cikin dalilin daya saka ba mu jituwa da Aliyu, ita kanta Mama ta fin jin natsuwa da Aliyu fiye da ni, domin be rago komai a halinta da yanayin rayuwarta ba, har mamakin mu ke yadda ke yau ya sassauta miki ya doki Maryam saboda abunda tai miki, bayan be taba saka hannunsa ya dake kowa a gidan nan ba, sai da na fi alakanta hakan da zalincin da Maryan tai miki, domin baya son ya zalinci wani ko ya ga an zalince, sai dai fa ba shi da mutunci kuma hakan ba zai saka ya sake maka ba”
Hannunsa ya kai ya kama hannuna.
“Wata kila da ke zan iya canja musu rayuwa, wata kila da ke zai saka Mama ta fara daukar talaka da daraja, wata kila da ke Aliyu zai zubar da wannan halin nasa na nunanin talaka ba komai ba ne, kina da abubuwan da ke so a jikin mace, fari kyau gashi kurciya hankali ladabi da kuma kuzarin aiki, kin kwanta min sosai a raina Ataa tun ranar dana fara ganinki, dan talauci ba zai saka na kyamace ki ba, ko na kasa nuna kaunata a gareki ba, wata kila idan kika shigo cikinmu Rukaiya Baby Maryam Ahmad Aliyu Mama da duk wani wanda baya ganin darajar talaka zai daina ko ya rage, idan na samu sa'a kika so ni....”
Be karasa ba nai saurin fisge hannuna ina kallon cikin idonsa da mugun tsoro, ba tsoro na a dake ni ko amin wani abu ba, tsoro na kalamin daya fito daga bakinsa ji nai kamar kunnuwana ba za su iya dauka ba, kalmar ki so sai ta shiga a zuciyata tai min fadi sosai har ta sakar min nauyi a kirji.
“Kwantawa zan yi”
Na fada muryata na gargada a take na soma jin zazzabi na dawo min, be sae ce min komai ba, bayan yawun bakinsa daya hade ya dauki plate din da cup ya fice. Da sauri na kwanta saboda nauyi da naji kirjina yayi na kife ina ina fitar da numfashi daker, wani be taba fada min magana mai nauyi kamar wannan ba, a cikin talakawan yan'uwana babu wanda ya taba fada min haka, ban taba kawo wa raina wani zai so ni ba, shiyasa ni ma ban taba jin son kowa a cikin raina ba.
“Idan na samu sa'a ki ka so ni....”
Kalmar tana ta maimaita kanta ta cikin kunnuwana, a take na fashe da kuka ina jin wani sabon al-amari da ban taba ji ba, kuka na rika yi sosai kamar wacce aka daka ko aka fadawa wata bakar magana, sai na ji ina da bukatar mahaifiyata a kusa da ni ji nai kamar ace Nana tana kusa da ni na rumgumeta ta rarrashe ni amman ba dama.
ALIYU POV.
Sai da yai sallah magariba a unguwar sannan ya isa gida yana ta jin babu dadi a abunda Maryam tai ma Ataa and ganin Muhseen na bata magani ma it pain him domin yana ganin kamar cutar da ita kawai Muhseen zai yi, yana da tabbaci zai iya kare kansa daga duk wani abu da zai kusantar da shi daga Zina amman ba shi tabbaci wani zai iya kare kansa daga hadawa hallakar zina, ba kuma duk wannan yake damunsa ba, babban damuwarsa zuwan Ataa gidan saboda nemawa mahaifiyarta maganin kodar da aka cire mata wanda shi ne sanadi duk da ba da saninsa da amincewarsa aka cire ba, yanzu kuma idan wani abun ya same ta ai duk saboda shi ne. Babban plan din da ke gabansa na ya taimaki mahaifiyar Ataa ne ya nema mata magani ta samu lafiya sannan ya nemi yafiyarsu wata kila zasu yafe masa, amman ya kasa tunkarar Ataa kai tsaye da hakan, saboda tana fada masa magana son ransa a duk lokacin da yai maganar mahaifiyarta shi kuma girma kai da jin kai ba zai barshi ya iya tsayawa ya fahimtar da ita ba.
Horn daya yai aka bude masa gate ya shiga cikin gidan ya faka motarsa a inda ya saba fakawa, sannan ya bude motar ya fito ya nufi kofar shiga falon, wutar falon a kunne take sai dai tv a kashe kamar yadda ya fita ya barshi amman ya an gyara komai na falon wanda hakan ke nufin mai gyara gidan ya zo ya gyara ya tafi, dakin Rahma ya fara nufa ya tura ya shiga, sai ya same ta kasa kwance ta dafe cikinta zuwa awanzunta tana wani irin daukar rai kamar zata mutu, wayarta na nesa da ita a kasa, da alama kubucewa tai a hannunta ta fadi kasa, hawaye na ta fita a idonta. A firgice ya karasa kusa da ita ya rikota yana taba fuskarta.
“Rahma minene?”
Kasa magana tai sai ta bude baki tana fitar da numfashi daker, da sauri ya dauke ta ya fito da ita ya saka a mota kamin ya shiga motar ya kwalawa mai gadin kira ya ce ya bude masa gate, @360 ya fisgi motar ya fita daga gidan ya dauki hanyar babban asibiti, kamin ya isa hankalinsa ya tashi sosai yana ta ganin kamar Rahma mutuwa zatai a motar, sai duk yaji tafiyar ta masa tsawo yana jin kamar ana mayarda shi baya. Yana isa emergency aka karbe ta kasancewar asibitin ta manyan masu kudi ce ga kayan aiki a take aka hau bata taimakon gaggawa, shi kuma ya kasa tsaye ya kasa zauna sai da ya ga an fito da ita daga dakin an kaita wani dakin an saka mata oxygen an saka mata wata allura a hannu, komai likitocin ne suka mata ba kamar nan da ake cewa mutum ya dauki mai jinya yaje ya kaishi a masa hoto ba, su da kansu suka dorata a wani gado suka kaita wani dakin aka dauki hoton jikinta gaba daya sannan aka dawo da ita wani likitan ya shigo ya debi jininta ya fita. A lokacin ne Aliyu ya samu natsuwa har ya kira Mama Fulani da Ammy da kuma Momy ya fada musu kamin ya kira familyn Rahma su ma ya fada musu. Zauna yai kusa da ita ya kai hannunsa yana shafa fuskarta dayan hannunsa kuma cikin hannunta yana murzawa a hankali, kallo daya zaka masa kasan yana cikin tashin hankali rudani da tsoro a lokaci daya.
Ba ayi minti talatin ba sai ga Mama Fulani da Ammy a asibitin sun zo, hankalin Mama Fulani ya fi tashi fiye da na Ammy ita kuma ba dan Rahma ba sai dan Aliyu da ta san zai tashi hankalinsa saboda Rahma, domin shi Mama Fulani take kallo ba Rahma ba.
“Jiki ai da sauki”
Mama Fulani ta fada.
“Eh da sauki gaskiya tun da yanzu sun saka mata oxygen zata samu saukin numfashin, kuma sun mata hoto ko minene za su ga ni ai”
Ammy ta ce.
“To wai miya faru ne da ita?”
“Wallahi ban sani ba, ina komawa gida na same ta a dakinta kwance kasa ta dafe cikin tana daukar numfashi”
“Allah ya sauwake"
“Amin”
Ya amsa yana picking din calling don da Mommyn Rahma ke masa, cikin sautin kuka ta ce.
“Fada min addreshin asibitin ga kanwata nan da take Abuja zata zo ta duba mana jikinta”
“Jiki da sauki fa ta samu bachi ma”
Haka ya fada sannan ya fada mata inda asibitin take ya kashe wayar, sai ga wani likita ya shigo ya ce duk su fita basa son ganin kowa akan marar lafiyar, daman a ka'idar asibitin ba a aje mai jin marar lafiya su suke masa komai ba a kwana a asibitin da sunan jinya suna da nurses da suke kula da marar lafiya da ko mai jinyar ba zai iya kula da shi haka ba. Gaba daya suka fito daga dakin suka bi bayan baturen likitan zuwa office dinsa domin ya fada musu yana son magana da iyayenta ko mijinta, a lokacin da suka shiga office din sai suka samu ba likita daya ne a ciki ba, likita biyu suka tarar yan Nigeria bayan wannan baturen da suka shigo tare da shi, a bayan teburin likitocin an laka wani katon majigi mai kamar kwanfuta an laka wasu hotuna a jikin abun. A visitors chairs suka zauna shi kuma likitan ya nufi inda computer take ya cire hotunan jiki ya dauko wasu ya laka da wani dan pen na hannunsa ya nuna musu inda matsalar Rahma take yana musu bayani da halshen nasara. A bayanin da likitan yai da wanda sauran likitocin sukai babu wanda Aliyu ya fahimta, ba dan baya jin turancin ba, sai dan jin abun wani banbara gwai, wai kodarta ta kone as how kodar mutum zata kone? Ba ma lalacewa ba? And duk duka yaushe aka saka mata kodar da za a ce ta kone? Gaba daya rikecewa yai ya tashi ta sauri ya fice daga office din ba tare da ya jira likitan ya gama bayanin ba.
Ammy ba ta wani dade asibitin ba bayan likitan ya gama musu bayani suka fito suka samu Aliyu tsaye a waje duk ya bi ya rike kamar ba shi ba, shi kansa ya san Allah kadai ya iya haka, ace koda ta kone, gashi kodar ce daya ta rage mata wacce aka dasa mata sai kuma ace ta kone, kamin ma ya samu wata aiki ne, and ba zai zama ace ko da yaushe sai an dasa nata koda ba idan an samu wata rana ba za a samu ba. Mama Fulani ce ta tsaya da shi tana ta bashi magana tana kokarin kwantar masa da hankali, har wata kanwar mahaifiyar Rahma ta shigo taje ta duba, yasan dokar asibiti ba a kwana da sunan jinya amman a haka ya karya dokar ya zauna a kujerar ya saka matarsa a gaba yana ta kallonta hannunsa cikin nata, ji yake kamar ya cire ta mata ciwon a take ta tashi, jikinsa nata raya masa mutuwa za tai ta bar shi, and all what he was thinking idan ta mutu ba zai iya rayuwa ba, taya ma zai rayu babu Rahma? Haka ya saka ta a gaba yana ta kallo, misalin 12 ya aikawa Nasir da sakon abunda yake faruwa, da Nasir ya kira shi kuma sai ya kasa dauka, sai kallon wayar yake gaba daya ya rike ce ya rasa inda zai saka kansa, gaba ya saka ta yana ta kallo har garin Allah ya waye, bachi be leka idonsa ba ko da wasa. A wani masallaci dake nesa da asibitin yai sallah asuba gaba daya addu'arsa Rahma yai ma, daya fito daga masallacin sai ya zauna cikin motar ya kifa kansa jikin sitarin motar yana ta sauke ajiyar zuciya idonsa na masa mugun nauyi. kiran Nasir ne ya shigo wayarsa amman ya kasa picking har tai ringing ta katse aka sake kira, gaba daya kasala yake ji yana jin shi ma kamar ba shi da lafiyar. Sako ya turawa Nasir na addireshin inda yake, sannan na kwantar da kujerar ya lumshe idonsa, cikin mintunan da ba su fi ashirin ba Nasir ya iso gurin, babban masallaci ne amman hakan bw hana shi gane motar Aliyu ba, domin irin ta bata da yawa a garin Abuja. Yana bude motar Aliyu ya bude idonsa da suka kada sukai ja yana kallonsa.
“Ya jikin nata?”
Aliyu yai shiru be ce komai ba sa yawo yake da idonsa kamar marar gaskiya. Nasir ya dafa shi.
“Aliyu ka kwantar da hankalinka...”
“Wane irin na kwantar da hankalina? Kodar ta fa aka ce ta kone, ko baka gane ba?”
“Na gane, amman me likitocin suka ce?”
Aliyu be ce masa komai ba, ya jinginar da kansa jikin sitarin yana sauke ajiyar zuciya. Can kuma ya dago ya kalli Nasir.
“Saboda kodar nan ta zalinci ce ko? Shiyasa ta kone? Ko kuma saboda Ataa ta ce ba zata taba amfanar Rahma ba? Ta mana Allah ya isa fa”
“Gaskiya ne Aliyu zalinci kawai ba ban da addu'ar da tai muku