Showing 111001 words to 114000 words out of 225640 words
nufi cikin asibitin, kusan mutane duk wadanda nake cin karo da su babu mai kallo ďaya mazan dai duk wanda ya kalleni sai ya sake kallona wasu har da sakar min murmushi suke. Ni dai in biye da Momy har muka isa cikin dakin da Nana take, Doc Bukar muka samu a ciki da Laraba Doc Bukar na duba Nana wacce ki kwance idonta bude tana kallon mutane, Momy ce ta karasa cikin yayinda ni na tsaya bakin kofa ina kallonta na kasa karasawa tsoro na ke kar na je kusa da ita tace min bata gane ni ba, Doc Bukar na ta sakar min murmushi ni kuma idona na kan Nana har na fara hawaye.
“Karaso mana Ataa”
Cewar Doc Bukar daker na iya daga kafana na fara takawa cikin dakin, karar sautin takalmin kafata ne yasa Nana ta kalli inda na ke wani abun mamaki sai na ga ta sakar min murmushi, dadi na ji da sauri na karasa kusa da ita ina ta kallonta kamar zan cinye ta.
“Nana”
“Na'am Ataa”
Mantawa nai da tiyata ce a jikinta ya rumgume ta ina kukan dadi, bata manta ni ba ko da ta manta komai ni bata manta ni ba, sai da Momy ta dago ni tana dariya ta ce.
“Karki ji mata mana yi a hankali”
Na kalli Doc Bukar ina hawayen farinciki na ce.
“Doc bata manta ni ba”
“Bata manta komai ba sai dai ki yi mata fatan samun lafiya”
“Al-hamdulillah Allah mun gode maka”
Na fada ina daga hannuna sama, dadin da make ji a yanzu ba zan iya misalta shi ba, duk wanda ya kalleni ya san ina cikin farinciki a wannan lokacin, ba ni da wani buri face samun lafiyar Nana da alama muka yanzu ta doro hanyar samun.Kasa cin abinci safen mai saboda murna sai an nemi yunwa na rasa, Ita kuma Momy ta hada mata tea ta bata da kanta a hankali tana sha har ta sha ya isheta.
“Na gode Momy Allah ya saka muku da alheri”
Murmushi tai ta aje kofin tana fadin.
“Ba komai ai yi wa kaine”
Ta dade a asibitin sannan ta fita ita da Laraba wai zata je gida tai wanka ta gyara ta dawo. Aka bar ni asibitin ni da Nana ina kula da ita, cikin muryarta na marasa lafiya take tambayata.
“ataa ina kika samo mutanen nan? Suna da kirki sosai”
“Wannan matar dan ta ne ya taimaka mana, daga gidan da nai aiki a abuja ya biyo ni zuwa nan na fada masa matsalata da kuma dalilin aikin da nake a can gidansu an Abuja shine ya fadawa Mahaifiyarsa sai suka taimaka mana suka kawo ki asibiti ya biya kudin aikinki kuma jinin da aka saka miki jiya ma ance shi ya bada jinin, kuma yanzu haka a gidansu nake zaune su suka ba ni wannan tufafin ma”
“Allah dai yana da kirki sosai Allah ya saka masa da alheri shi da babarsa, bayan Doc Asim mun sake haduwa da wani mutum mai taimako”
Na yi shiru ban ce komai ba, domin Doc Asim ko sunansa ba na son a ambata.
ALIYU POV.
Daga masallacin da yai sallah ya wuce gurin Momy, duka kanensa suna zaune tsakar falon suna cin abinci a plate daya, a tare suke gaishe shi ya amsa musu da dan sakin fuska sai dai ba Sosai ba ya nufi dakin mahaifiyarsa. Zaune ya same ta gaban madubi tana shafa mai a jikinta, juyo tai ta karba masa sallamar da yai tana kallonsa.“Wa'alaikassalam”
“Momy barka da rana”
“Yauwa, ka je asibitin kuwa?”
“No yanzu da na ke son na leka, ban sani ba ko wa a wuce da wani abu shiyasa na biyo”
“Yau Ataa tana cikin farinciki”
Ya kalli Momy da mamakin farincikin nata, Momy bata jira ya tambaye ta ba ta ce.
“Mamanta ta farka kuma bata manta komai ba”
“Wow”
Ya fada yana murmushi.
“Har tea na bata ta sha, yau Ataa har da min godiya”
Ya dada fadada murmushinsa shi kansa ya jidadin jin hakan balle kuma da aka ce masa Ataa tana farinciki, ya gyara zamansa yana kallon Momy ya ce.
“Ban sani ba ko idan na fada miki wani abu za ki yarda”
“Minene?”
“Jiya lokacin da kai abincin dare na samu Ataa bata nan har na kawo Husna na koma bata dawo ba, na tambayi Laraba tace min bata san inda take ba, sai na hankali ya tashi na zata ko Muhseen ya fita da ita ko kuma Doc Bukar domin shi ma kamar yana dan rawar kafa akanta, amman na fara zuwa gidan da na dauko ta na fara dubawa ko taje daukar wani abun kamin na kirasu, sai na same ta tana bachi bakin kofar dakin na kwano, na ji tsoron tashin ta saboda kar ta min masifa so i decided nai gadinta saboda ina jin kamar idan na barta a nan wani zai iya zuwa ya yaga mutuncinta, da daman na mota ya ishe ni sai na fito gurin kwanon na zauna a kasa na jingina....”
Yayi shiru na wani lokaci kaminnya cigaba.“For the first time Momy jiya na zauna akan turda, na ji wani yanayi na dabam da ban taba ji ba, gurin babu ac babu katifa, sai hasken farin wata, garin yayi tsif kamar ba bu mai rayuwa a duniyar nan, Momy abunda na fara tunawa da shi shine kabrina, wata rana zan kwanta kamar haka a cikin kabarina, babu shimfida mai kyau babu gado ko katifa, babu haske sai na aikina, duk wani abun dana tara na dukiya da kawa a nan zan bar shi, zan rayu ni kadai a cikin kabarina”
Ya fada idonsa da kwalla Momy ta yi murmushi cike da kaunar danta.
“Secondly Momy na ji yadda wandada basa da shi suke ji, na taba kasa na zauna a kai i feel it bata da dadi amman a haka wasu suke kwana a samanta a haka wasu suke rayuwa a cikinta, then i realise there are billions of her da abinci kawai suke nema da muhalli, not like thousands of us da idan muka ga dama ba a Nigeria kwana ba a wata kasar ne, i never thought akwai mutumen da zai iya rayuwa a irin wannan yanayin sai yanzu, i never thought there a alot of homeless people da zasu raba a gidan wani kamar haka sai yanzu, Momy na ji wani a cikina some thing differently, wani abun da ban tana tunanin jin sa ba”
Murmushi ne har yanzu a fuskar Momy.
“Shiyasa Musulunci ya koya mana taimakon marasa shi, ko abinci ka taimakawa wani da shi zaka samu lada kuma zai jidadi ya rika ganinka da kima, yatsun hannyen mu Allah yayi su dabam balle kuma.mutane, dole akwai mai arziki akwai mai talauci akwai mai tsakiyar shi ba mai arzikin ba kuma ba mai talaucin ba, sai dai abunda aka fi so, arzikin da tsarki zuciya, a lokacin da nake nuna maka kyamar talaka ba abu ne mai kyau ba, sai kake ganin kamar ban fahimta ba ne, saboda Fulani ta nuna maka wata tarbiyar ta dabam wacce ba ita na so na dora ka akai ba, talakawa mutane da ya kamata ace an rikesu an nuna musu kulawa da kauna ko da ko su din basa son ka, ka yi dan Allah shi zai baka lada, a lokacin da mutum yake cikin yunwa idan ka ka bashi abinci zai dauke babban masoyi, wanda yake kishi kuma ka shayar da shi, zai ga ba shi wani mai sonsa a duniya kamar kai, balle kuma wanda lafiya ta gagareshi ka tsaya nema masa ba zai taba mantawa da kai ba, kuma ragowar rabon yana gurin Ubangijinka, akwa su da yawa marasa mayafi lokacin sanyi marasa abincin lokacin yunwa marasa mafaka lokacin damina, abu kadam su ke son samun su yi farinciki, while kai Allah ya hada maka komai arziki ilmi lafiya hankali da komai, wani yana can shi hankali ma yake nema ya samu be samu ba, shikenan kai dan Allah ya hada maka komai sai ka ce ka fi kowa? Wata kila ma mutanen da kake rainawa sune a gaba ranar alkiyama kai kana baya a kaskance kuma shine babban talauci”
Ya kawar da fuskarsa yana sauke ajiyar zuciya maganganun Momy sun kara taba zuciyarsa ya karanta ya sani amman ya take saninsa saboda yana jin shi din wani ne, yana jin ya fi kowa kuma babu wanda ya isa da shi saboda yana kudi alhalin dukiyarsa ba komai ba ce a gurin Allah.Momy ta share hawayen da suka zubo mata tana dauko zancen Muhseen.
“Dazu Muhseen ya fada min cewar kana takura masa akan Ataa hya fada min sonta yake kuma yana son na shige masa gaba”
Aliyu ya kalleta da sauri mamaki a fuskarsa karara.
“Muhseen din ya fada miki?”
“Eh yace ya fada mata ma”
“Me kika ce masa?”
“Na fada masa ita yanzu ba soyayya ne a gabanta ba, domin mahaifiyarta babu lafiya, wata kila kalaman nawa ba su masa dadi ba, na tafi kai abincin asbibiti tare da ita ko da na dawo na tarar ya tafi, ni kuma ban jidadin hakan ba”
“Miye abun rashin jindadi a ciki Momy? Ai gaskiya kika fada masa mahaifiyar yarinya ba lafiya ban dan rashin tunani ba har ya dube ta ya fada mata yana son ta? Kuma yarinyar nan yanzu abunda take bukata ilmi, bata san komai akan addinta ba, yarinyar da bata iya banbance muharrami da ajnabi, ko mahaifiyarta ta samu lafiya ai ilmi ne first abunda take bukata a yanzu i never thought akwai jahilan mutane irinta Wallahi”
“Akwai sosai ma, bara fa take wai kaga ba lallai ne ace tana zuwa makaranta ba,ni kaina na fada masa hakan ne saboda na san be kamata yai mata maganar a yanzu ba, shi kuma be fahimci ni ba”
“Babu wani rashin fahimta, taya zai ce yana son yarinyar da be san familynta ba? Kuma yar talakawa kamar wannan ai yasan Mama Fulani ba zata taba Amincewa ba”
“Shiyasa yake son ma shige masa gaba, kuma ni mai masa komai ce idan hankali ya kwanta”
“Idan tana son sa ko?”
Ya fada yana mikewa tsaye domin shi sam baya son maganar ma.
“Mi zai sa ba zata so shi ba, miye Muhseen ya rasa?”
“Ina abincin yake?”
“Yana kitchen”
Ficewa yai daga dakin zuwa kitchen din, yana ta tunanin halin Muhseen da son banbancewa idan da haske son Ataa yake ko aa, and if ma son ta yake da gaske ai be dace ya fada mata a irin wannan yanayin.Har ya isa asibitin be daina jin haushin Ataa ba shi ya rasa wace irim yarinya ce da har zata tsaya ta saurareshi, he wonder wace amsa ma ta bashi, yaushe ya fada mata zuwansa a nan ko kuwa tun suna Abuja? Wannan karon ba kamar yadda ya saba shiga dakin ya shiga ba, da sallama ya shiga tsabanin baya da sai dai ya tura kofar ya shiga a haka ba tare da sallama ba. Laraba ta amsa masa Ataa kusa na zauna saman gadon da Nana take tana ta mata fira baki har kunne. Da wani irin far'a marar misaltuwa Ataa ta kalleshi kyau da tai da far'ar data haska fuskarta sai ta tasa gabansa faduwa a karon farko. Ba laifi ya saki fuska sai dai ba sosai ya karasa gurin Nana yana mata ya jiki.
“Nana wannan shine Aliyun”
Ataa ta fada mata tana nuna mata domin a yanzu shi Aliyun ne ta gama bata labari da kanansa da kuma mahaifiyarsa.
“Ba mahaifiyarki ba ce kike ce mata Nana?”
“Haka ake kiranta”
“Idan haka ake kiranta ke sai ki kirata haka?”
Tayi shiru tare da yin kasa da kanta.
“Karki sake kiran sunanta ba kyau kiran sunan mahaifiya”
“Ba sunanta na gaskiya bane, sunanta na gaskiya Asma'u”
Wata uwar harara Aliyu ya watsawa Ataa daman wani bakin haushinta yake ji na rashin dalili. Ko minti goma be yi a dakin ba yace zai ta fi sai Nana ta ce.
“Mun gode sosai Ataa ta fada mana yadda kake ta hidima da mu kai da yan'uwanka Allah ya saka da alheri ya kara rufa muku asiri ya tsare ku daga ko wane irin sheri ya kara arziki da wadata”
“Amin”Ya amsa har karkashin zuciyarsa ya jidadin wannan adduar kusan a rayuwarsa sai yace be taba samun wani talaka ya masa irin wannan addu'ar ba, ba ma talaka kadai ba, ko mai arzikin dan'uwansa be taba masa irin wannan addu'ar ba. Bayan ya amsa da Amin din ya juya ya fice daga dakin. Yana fitowa daga ward din ya hadu da doc Bukar sama sama suka gaisa da Doc Bukar din har Bukar yake labarta masa yadda sukai da Ataa ranar, a nan Aliyu ya warware masa zare da bawa akan maganar tun daga farko har karshe.
“Daman ai na san ba zaka aikata ba, ga shi kuma an yi tiyatar cikin nasara gaskiya Doc Muhseen yayi kokari sosai yanzo in time kuma ya maida hankalinsa kam aikin sosai, Allah ya saka hannu a ciki ba a samu wata matsala ba”
Aliyu ya yi shiru be ce komai ba har suka jero suna tafiya gurin motarsa.
“Ni Wallahi yarinyar ta ba ni tausayi sosai irin wannan idan mutum ya same ta ai sai ya rike ta amana”
Ya fada daidai lokacin da Aliyu ya bude motarsa zai shiga ya zauna, kallonsa Aliyu yai sai kuma yai yar dariya mai sauti ya rufe motarsa ba tare da ya ce komai ba, Doc Bukar din ma dariya yake domin shi har ga Allah Ataa ta masa duk da kasancewar matarsa ma fara ce kuma ba shi da niyar kara aure amman ganin Ataa ya ji yana son ta yanayinta da komai nata sun masa.
Sai da Aliyu ya kama hanyar wurno road sako ya shigo wayarsa, yana dubawa ya ga number Rahma.
_Aliyu kana ina_
Be bata amsa ba ta sake aiko masa wani.
_Naga Amina ta saa shegiyar yarinyar a status dinta daman tana gidanka ko?_
_I Love you_
Shine reply dinsa a gareta yana murmushi.
_Kana can gurinta ko Aliyu?_
_I Love You_
Ya sake aika mata da reply.
_Daman na sani ai tana nan cikin ranka amana ta za ka ci ko Aliyu_
_I love you_
Ya sake aika mata as reply.
_I hate you_
Ta rubuto masa a take, wani kasaitaccen murmushi yai ya kara gudun motarsa yana karba kiran Nasir da ke shigowa wayarsa a yanzu.MUHSEEN POV.
A ka'ida sai gobe zai koma Abuja kamar yadda ya siya ticket amman ya kasa hakurin zama gidan na minti talati ma balle har ya sake kwana, a yanzu ya fahimta ba Aliyu ne kawai baya son alakarsa da Ataa ba har da Momy domin a yanayinta da ya gani da kuma irin amsar da ya ji a gurinta yasa shi fahimtar hakan, wata kila ita ma bata son ya so Ataa saboda dan ta yana sonta, wanda yake ganin hakan kamar nuna masa banbanci ne tsabanin Aliyu da Mama Fulani take nuna masa kauna fiye da Muhseen din da ta haifa. Shi har yanzu be ga laifinsa dan ya nuna son Ataa saboda tana da kyau ba, ya sani musulunci ma be hana a so mace dan kyauta ba, idan kuma har Aliyu zai nuna kebewarsa da ita matsala shi ma din be dace ya kebe da ita ba, domin shi din ma ba ma a sumi ba ne. Har ya isa Kaduna Momy bata daina kiran wayarsa ba shi kuma be daga ba, be ko tsaya kwana a kaduna ba haka ya bi hanyar Abuja, wani bangare na zuciyarsa yana ba shi hakuri akan ya kyale Ataa ya cire a zuciyarsa yayinda dayan kuma ke zuga shi akan idan har ya barta ya nuna Aliyu ya ci galaba akansa kenan kuma be kamata ya kyale Momy da Aliyu yayi musu hallacci ba idan su din ba su masa ba.
Ya shiga Abuja late domin uku na dare ta yi, ya dade yana danna horn kamin a bude masa gate din. To his surprise da ya shiga ciki sai ya samu Mama Fulani da Abbah da su Maryam da Rukaiya duka farke har Baby ma sai fira suke ana cikin nishadi. Ba karamin tsoro da mamaki suka ji ba ganinsa, domin ba saka ran dawowarsa yau ba ko dai zai dawo ba cikin dare kamar yanzu ba.“Lafiya ba ku yi bachi ba?”
“Muna celebration ne mutumen nan na Nijar da na ke fada maka ya siye kamfanin har an biya kudi kuma ya danka ragawar kamfanin a gurin Abbah ku, har da wasu gyare gyare ma zai yi”
Mama Fulani ta fada baki har kunne.
“Mashallah abu yayi kyau Abbah congratulations”
Ya mikawa Abbah hannu sukai shaking.
“Congratulations to us, Muhseen ya za ka biyo hanya a dare nan? Lafiya dai?”
“Ba lafiya ba Abbah amman da safe za mu yi magana”
A take murmushi da murnar da ke fuskarsu suka gushe. Bama kamar Mama Fulani da bata son damuwar yaranta.
“Ka fada mana ko minene a yanzu ba sai da safe ba, ba za mu iya jira ba”
“Ki bar shi idan ya huta da safe sai mu ji ko mienene tashi kaje dakinka”
“Na gode Abbah”
Ya fada yana mikewa tsaye ya fice daga falon cikin yanayin damuwa.
“Ko fada sukai da Aliyu? Ko kuma matar da kaje yi ma aikin ce ta mutu ko wani abun ya faru ba”
Maryam da Rukaiya sun fada.
“Ko ma minene za mu ji da safe, ku tashi muje ku kwanta”
Abbah ya fada yana mikewa tsaye ya fice daga falon zuwa part din Ammy. Lokacin daya shiga part dinsa wanka fara yi yai sallah isha'i da samu yi ba sannan ya saka kayan bachi ya hau saman gadon ya kwanata. Kasa bachi ya yi sai juyi yake akan gadon, duk wani so da yace yana ma Ataa a da sai a yanzu ya gane wasa ne, domin a yanzu ne yake jin matsifar son ta cikin ransa da kuma tsanar Aliyu, tabbas ba zai iya yafewa ta ba, domin a yanzu na gane duk na da ma wasa ne yanzu nen yake sonta da gaske. Kamar kar Aliyu ya fadi cewar yes son ta yake sai ya ji ya kara tsanar Aliyun son ta kuma na karuwa a ransa.
*Khadeeja Candy*
*ZAKI
By Khadeeja Candy
35...
Ya farka da wuri saboda be samu kwanan ba har garin Allah ya waye, bachi barawo ne amman ya san wanda yake sata, akwai gajiya sosai