Showing 195001 words to 198000 words out of 225640 words
na san halin dan ki ba komai zai gani ya kyale ba sai yai ta nuna rashin kunya a gidan sarauta kuma ba a haka, kara dai sai cikin ya yi kwari”
“Allah Momy ba zan iya ba, abun da kunya sosai”
Daga dayan bangaren Momy ta yi dariya jin abunda Mama Fulani take fada wai da kunya, yau Mama Fulani ce take cewa tana jin kunyar yin wani ba wacce ke bugun gaba tana ganin ita tana da kudi kowa zata iya tinkara ta fada masa magana kai tsaye, kuma jin kunyar ma ta Ataa yarinyar da ta gama wulakantawa tana nuna mata ita din ba kowa ba ce.
“Na fada miki idan kika ce za ki dauki zancen kunya ki saka a ranki za ki yi ta cutar da kanki da d'anki ne kawai, ki kasa sama masa abunda yake so ke ma kuma ki kasawa bawa kanki, ni dai ina farinciki da yadda na ji halin nan ya sauko Wallahi, na dade ina jiran zuwa wannan ranar amman ban samu ba sai yau na dade ina nuna mu ku abunda kuke kuskure ne amman kuka kasa fahimta, sai da Ataa ta zo, lallai Ataa ta zama alheri a familyn mu”
Ajiyar zuciya Mama Fulani ta sauke a hankali sannan ta sake share hawayen da suka zo mata.
“Ina murna da samun cikin nan abunda muka dade muna nema, ashe Allah ya rubuto sai ta bangarenta za a samu, Allah ya inganta ya bata lafiya kula da shi”
“Ameen, yanzu kulawarta a hannunki take tunda kin san a nan za su zauna kusa da ke”
Mama Fulani ta yi shiru tana kallon Muhseen wanda ya shigo hannunsa rike da wasu magani har kala hudu.
“Na gode Sai kin sake ji na”
Mama Fulani ta fada sannan ta katse wayar tana cigaba da kallon Muhseen wanda fuskarsa ke cike da walwala.
“Mama ki sha wannan maganin yanzu”
“Na dazun ma ban sha na fa”
“Miyasa da kin sha ai sai ki sha wannan yanzu kawai, amman ki bar wacan ki sha wannan”
“Duka? Na ji zazzabin ya sauka ma da nai wanka fa”
Kusa da ita ya zauna yana murmushi.
“Mama ki sha kawai likita kika haifa fa, sai dai anjima zai iya dawo miki tunda tunanin yana nan cikin ranki”
“Tunanin me?”
Ta tambaya tana nuna kamar babu abunda ya dame ta.
“Na abunda ya faru mana Mama, kina ta jin kunyar Ataa ko?”
Ta yi shiru bata ce komai ba.
“Wallahi tun daga lokacin da kika fada min labarin nan, sai Ataa da mahaifiyarta suka kara burge ni, yanzu irin yarinyar da ake wulakantawa kamar haka ace ta san tana da family irin wannan amman ta yarda ta zauna a haka ta jure wulakanci da cin mutunci, kin san da wata ce tun daga lokacin da suka fara shiga gararin rayuwa za su fara neman yan'uwnasu ko da yankasu za ayi a ci namam su? Wani abun farinciki faruwar wannan abun ya saka a take jiki ya yi sanyi, kin zubar da makaman yakinki ga shi har kina jin ba dadi a abunda kika aikata, dubi Aliyu dazun davya shigo tare da ita part din Ammy abun har mamaki yake ba ni mai tsanar talaka ya koma son ta ko kunya be ji ba, ke ma kuma kina jin kunyar talaka kamar ba ku ba gaba daya, tun yaushe na ke son rayuwar ku ta canja Mama? Tun yaushe na ke nuna muku cewar talaka ba abun wulakatawa ba ne, amman kuka kasa ganewa ke da d'an lelen danki har kuna ganin kamar ni da Momy ba mu waye ba ne, lallai Ataa yar baiwa ce ita ta canja muku komai cikin kannen lokaci, ni kaina ina cikin farinciki a yanzu domin na samu wace ta fita, kuma raina yake so fiye da ita but the most funniest part Aliyu kishina yake har yanzu, ni kaina dunno why na ji kamar na tsani Ataa, but seriously tana burgeni akan wannan abun daya faru”
Mama Fulani ta mike tsaye ta nufi bandakinta ta dauka fanfon ciki ta kunna ta sha maganin sannan ya fito tana fadin.
“Yana ta damuna wai na je na yi magana da mahaifiyar Ataa akan tafiyar da za su yi kar su je da ita, ko kuwa ba ni da wannan damar a yanzu”
“Saboda me? Ataa fa dole ta girmamaki indai har tana ganin kimar mijinta, ke fa uwa ce a gurin Aliyu”
“Na sani amman ba yanzu ba”
“Yeah komai da sannu zai wuce kamar ba ayi ba Mama In-Sha-Allah”
Ya fada yana mikewa tsaye.
“Ya maganar kayanka? Idan ka shirya komai sai na yi ma Abbah ku magana”
“Ba yanzu ba Mama sai hankalinki ya kwanta, na fi son ayi komai kina cikin farinciki”
Ta gyada masa kai shi kuma yai murmushi ya fice.
ATAA POV.
Da tunanin abunda Mama Fulani zata fada min na shiga bangarenta, Aliyu ya fada min cewar tana son magana da ni amman akan me? A hankali na tura kofar falon na shiga babu kowa a ciki sai sanyin ac, ni kuma na zauna a saman sofa ban yi kaudi ko tunanin hawa sama inda take ba na zauna zaman jiranta har ta zuwa lokacin da za ta sauko.
Na kusan awa daya a zaune bata fito ba kuma wani be shigo ba, har na mike tsaye da zimmar fita sai na ji motsin saukowata hakan yasa na koma na zauna na daga kaina ina kallon yadda take takowa har ta sauko kasa, wani gefe gafe take da ido kamar ba ta ganni ba ko kuma bata son kallona.
“Mama Fulani Aliyu ya ce kina son magana da ni”
Shiru tai na wani lokaci kamin ta amsa min ba tare da ta kalleni ba.
“A a, wata kila dai be gane ba ne”
“Tau”
Sai da na mike tsaye sannan ta kalli inda na ke sai kuma ta dauke kai, ni kuma nai ficewata ba tare da na sake ce mata komai ba, a harabar gidan na ga karin motoci har biyu ba zan iya shaidar motar waye da waye a wajen ba, amman dai na san bayan motocin da suke fake a cikin gidan sai kuma ta Aliyu da Nasir yanzu kuma wasu ne har biyu irin mayan motocin nan na alfarma. Littafin nan na kudi ne, idan kin ganshi waje na sata ne. Bangaren Ammy na nufa kai tsaye daman na fi zargin bakin ko can suka zo tunda ban ga kowa ya shigo gurin Mama Fulani ba. A lokacin da na shiga falon Ammy sai na tarar babu kowa a ciki, kamar yadda na barta dazun zaune da Mama wato Nana da Aliyu ya lakanta min sunan Mama a saman nata na Nana da na ke kiranta da shi. Zaunawa nai na maida hankalina gurin tv dake kunne. Ba jimawa Ammy ta fito daga bandakin da ke falon tana kallona ta saki murmushi.
“Yanzu nan kuwa Hajiya ta fita”
“Ina suka je?”
“Suna bangaren Abbah, ya zo da wasu baki shine ya kirata”
“Ok”
Na fada ina ta tunanin ko su waye ne. Sai ga Aliyu ya shigo falon rike da line a hannunsa.
“Ina wayarki”
“Gata nan”
Na ciro ta daga koguna na mika masa ni na ma manta da wayar sai yanzu da yai maganar, tun a lokacin da na nunawa Mama ita na biyo ta ajikin gudun kar na manta da ita ban tuna ba sai yanzu.
“Ina kika saka ta?”
Ya tambaya yana min wani kallo kamar na mamaki ba tare da ya karbi wayar ba, kamar dai ya manta cewar ba daga ni sai shi ne a falon ba Ammy ma tana nan.
“Aliyu dan ta saka waya a jiki sai ya zama laifi?”
Cewar Ammy tana murmushi shi ma murmushin yai sai dai ba sosai ya karbi wayar ya bude yana saka Sim wani dadi ne ya lullube ni ganin layi ne zai saka min hakan na nufi zan iya kira kuma a kirani.
“Ta so muje”
Tashi nai na bi bayansa yana gaba ina biye har muka isa bangaren Abbah, tun kamin mu shiga na fara jiyo muryar wasu na watso turanci kamar turawa sai hayani suke a falon har da muryar mace. Dan tsayawa nai na janyo rigar Aliyu.
“Su wanene?”
Na tambaya kadan kadan kar su ji.
“Idon ki za su cire”
Ya fada min babu alamar wasa a fuskarsa kamar da gaske haka din ne. Sannan ya tura kofar falon ya shiga, ni ma na shiga da dan tsoro. Dukansu suna sanye da suit mata biyu maza hudu mace dayar tana sanye da karamin Hijab a wuyanta, dayar kuma kanta a sake ta saka jam gashi mazan biyu kuma suna rike da abun rubutu.
“Ke ce Ataa?”
Kabilar ta fada da hausa sai na gyada mata kai. Ina ta bin Aliyu duk inda yai har na zauna a inda ya zauna.
“Bude ba ki za ki yi ki mana magana, daga sama aka turo mu nan”
“Ni ce”
“Miye sunanki na gaskiya?”
“Aisha”
“Ya kike da wannan?”
“Mamana ce”
“Ita ta haife ki?”
“Eh”
“Mamanki tana da wani rashin lafiya ne ko wani ciwo?”
“Eh bata da koda daya”
“Garin ya?”
“Wani likita ne ya cire mata”
“Ya akai ya kai cire mata kodar kuma ya akai kika tabbatar cewar bata da koda?”
A take na fara zana musu yadda komai ya faru. Har suka fara tambayana kamaninsa na bayyana musu da kuma inda asibitinsa take. Namijin ya nuna min hoton group din mutane a guri daya ya ce na nuna masa shi sai na nuna fuskarsa.
“Za mu mika wannan statement din aga kungiyar likitoci reahen jiyar sokoto, su fara na su bincike kamin ya iso zuwa nan, and After that za mu dauki ke mu kai ki asibiti a sake miki hoto domin tabbatarwa”
Ta karasa tana kallon Nana. Sai ta gyada mata kai. Sannan ta juya sukai magana da sunan su sai kuma suka mana sallama suka fice tare da Abbah ni sai a lokacin ma na ke lura da Nasir ashe har da shi yana zaune a falo har ma dayan jikan Mai Martaba wanda suka zo da shi. Aliyu da Nasir suka bi bayan Abbah, aka bar mu ni da Mama murmushi na gani a fuskarta na san ba zai wuce na jindadi ba kamar yadda nima na na jidadin ganin cewar za a kwato mata hakkinta, na yi zaton maganar zata fara min sai na ji ta ce.
“Mai Martaba ya ce mu shirya duk abunda ya kamata a yau, gobe da safe za mu wuce Lagos daga can za mu tafi gida”
“Waya fada wa”
“Yusuf ya fada min lokacin da suka shigo, kuma ina fatar kin fadawa mijinki”
“Eh na fada masa amman yanzu zan kara masa maganar”
“Ina jindadi sosai zan ki ga iyalina ni ma kuma zan sadu da su da kuma mahaifiyata bayan tsawon lokaci, na jidadi sosai, na jidadi marar misaltuwa kuma ina cikin jindadin”
Ta fada ya yaren buzanci idon na cika da kwalla.
RAHMA POV.
A hankali numfashinta yake shiga jikinta, idonta kulle hancinta kuma manne da oxygen, ga wani katon tukuyar shakar numfashi da ke aje gefenta tare da wata nu'urar da ke taimaka mata tai numfashin, idonta a rufe suke amman hawaye masu zafi ne suke gangarowa daga cikin idonta da ke rufe zuwa gefen ko wane kuncin fuskarta.
Mommynta tana zaune gefenta idonta ya sumbura sosai saboda kuka gaba daya ta fita daga hayyacinta kamar ita ce marar lafiyar ba Rahma ba. Samun koda yanzu abu ne mai wahala, domin sun saka nema har yanzu ba a dace ba, balle kuma yanzu da likitocin suka tabbatar musu da samun ta a dole matukar suna son yar su a raye cikin koshin lafiya.
Ba zata iya kallon yarta ta mutu ba, bayan tsawon lokacin data dauka tana jinya kuma tana son Rahma a cikin yayanta fiye da kowa, matukar aka kwana biyu ba a samu ba zata yarda a cire nata daya a dasawa Rahma ko da ko ita zata rasa ranta ne ko kuma lafiyarta, ba zata iya kallon Rahma ta bar duniya ba saboda rashin abunda zata iya samar mata ba, tunaninta da bakincikin mutuwar Rahma idan har ta Allah ta kasance ta san ita ma ba zai barta ta rayu ba. Da wannan kara kawai ta bata kodarta daya idan har zai yi, ita kanta ta san abubuwa sun yi ma Rahma yawa a yanzu, samun cikin Ataa, barinta da Aliyu yai ya auri wata, ga Kuma bullowar wannan lamarin na kakanta Ataa wanda ya zama karkashin inuwarsa dukansu suke rayuwa, ta alfahari da bugun gaba ta kare.
*Ina mata son rage kiba? Ina mazan da kiba ta hana su sukuni? Ina masu jikin yai kyau kamar na yarinya? Ina masu fama da kujera ko wani ta bo a fuska? Ina masu fama da hawan jini? Masu diabetic? Ag cera an gwada yayi an tantance ingancin babu shakku ko kadan. AG cera ya zo domin ya temaki garkuwan jiki da kuma lafiyar jiki. Sinadari ne wanda ze magance matsaloli da dama wadanda suke hana garkuwan jiki aiki yadda ya kamata ko kuma yake rusa garkuwan jikin ita kanta.*
*Cututtukan zamani daban daban sun sa mutane gaba kuma magance su yana da wahala; irin ciwon Sugar, hawan jini, ciwon sanyin kashi, ciwon gabobi da sauran su. Haka ma cutukka irin wadanda suka shafi fatar jikin wadanda sun hada da kyasfi, pimples, takurewar fata, rakainuwar fata da kuma haske da kyallin fata duka ana shan AG cera kuma yana temakawa wajen magance illolin nan. Mutane masu fama da rashin karfin jiki wajen kwanciya da iyali da kuma mata masu fama da yawan ciwon mara lokacin al'ada ta karshen wata suma baa bar su a baya ba. A takaice dai AG Cera yana temakawa wajen magance cuttukka daban daban wadan ke damun mutum. Domin karin bayani ku tuntuni mu a wannan number +60167474649 ko kuma ku ziyarci shafin mu http://agnutritioninternational.com.*
*******
55
Ba mu koma gida ba sai dare, Nana ta yi ta nanata min lokacin da za mu tafi kamar yadda Mai Martaba ya fada mata, a hanya Aliyu ya tsaya ya siya mana ayaba kankana sannan muka isa gida. Sai ya ya faka motarsa sannan na saki hannunsa na bude motar kamin na fito har ya zagoyo gefen da na ke ya karasa bude min ganbun motar. A hankali na sauko ina takawa yana rike da hannuna dayan hannunsa kuma rike da ledar da muka siyo ayaba.
“Mama ta ce nai tuna maka zancen tafiyar mu fa”
Be ce min komai ba, har muka shiga falon sai ya zauna saman kujera ya janyo hannun na zauna saman jikinsa ya rumgume.
“Na sani ai, tare za mu tafi”
“Da gaske?”
Na fada cike da jindadi ina wara ido sai ya gyada min kai, rumgume shi nai na lafe a jikinsa kamar wata kyanwa yana shafa bayana a hankali. Mun dade a haka kamin mu koma daki, duk wani abu daya san zamu bukace shi a cikin daren ya hada mana shi, jaka daya ya hada mana kayanmu kamar yadda yai mana a wacan karon da za mu tafi Las Vegas, misalin tara da rabi Nasir ya kawo masa maganin da aka rubutu asibiti, sun dade suna magana waje kamin su yi sallama ya dawo ciki.
A gado daya muka kwana kamar yadda muka saba ina cikin kirjinsa har sai da yunwar da dare ta fara damuna na fito kitchen na dora indomie a cikin daren nan domin duk wani abu da ke nan bana sha'awar cinsa ba, ciki kuwa har da kayan marmarin dana ci jiya. Ina cikin zuba magi Aliyu ya shigo kitchen din, hannayensa ya dora a kafata taya ta tayani duba indomie a haka har ta dafu muka ci tare sai ya fini cin ma.
“Ashe kai ma kana jin yunwar”
“Ba dole na ji yunwa ba”
“Ba ka ci abinci ba a gidan Mama Fulani?”
“Na ci”
Bayan mun gama ya kai plate din a kitchen, ni kuma na nufo dakin domin a falo muka ci abincin indomie. Bathroom na shiga na yi fitsari ko da na fito yana rike da wayarsa da alama kira yake ko kuma karanta sako domin screen din wayar kawai yake kallo na tsawon lokaci sannan ya aje wayar ya zo bayana ya kwanta.
Washe gari da wuri na tashi fiye da ko yaushe saboda marmarin tafiyar da za mu yi, Aliyu ne ya hada mana abun karyawa muka karya tare a dinning sannan na shiga bathroom din dakina nai wanka, na saka farin material marar nauyi kamar yadda ya umarce ni, na saka sarka da abun hannu na manta rabon da nai kwallaiya da sarka tun ina karama a lokacin da Mahaifina yake raya ya siya min wata sarka a lokacin karamar sallah, sai kuma lokacin bikina da aka min kwaliya aka saka min sarka, sai kuma yau wani kwarji da kyau sarkar ta kara min kasancewar mai tsada har wani haske ba, kumatuna ya dan kumboro kamar ba nawa ba, mayan idanuwa sun kara fitowa sakamakon cikar da naman idona nai fari na karu sosai har wani shining na ke, ban tana lura da haka ba sai yau da nake kallon kaina a madubi. Murmushi mai wanda ya kara min kyau madaidaicin bakina ya kwanta dan jan bakina da na shafa ya kara fitowa, hannuna na kai na janyo gashina da nai parking a baya zuwa saman wuyana, sannan na dauki wayata ina daukar kaina hoto. Ta cikim madubi na hango Aliyu wanda ya saka wani boyal sky blue kamar na nawa sai dai nawa yadi ne kalar ce kawai daya. Zuwa yai gabana ya tsuna tana ta kallon fuskata ni ko ina aika masa da murmushi mai kyau da saukar da natsuwa.
“Kalle ki Babyna kamar ba ke ba”
Wannan karon dariya nai ya lumshe idona na bude, ni kaina ina jin cewar kamar ba ni ba ce, ta wani bangaren duk wani abu da ke ta yar min da hankali a yanzu babu shi, na samu rayuwar da ban taba mafarkin samu ba, kuma a cikin sauki ciki kuwa har da saduwar da Mama za tai yau da iyala wanda shi yafi komai faranta min rai a yanzu, da kuma muhunta Asim da za ayi, ga kuma auren Aliyu wanda na san shi ma babban nasara ce a rayuwata domin har ga Allah ina jindadin yadda yake kula da ni yana nuna min kauna, babban abun