Showing 267001 words to 270000 words out of 479911 words
kaita Asibiti, na bi bayansu a adaidaita sahu, an kaita wani ɗaki an hana kowa shiga, haryanzu dai ina asibitin, likitocin dai ba su ce komai ba, amma dai kamar fa ba ta da rai"
Ashar Viper yayi masa, ya ce "Yaya aka yi ma wuta ta kama a iya ofishin ta kawai? Me hakan yake nufi? Likitoci sun ce ta mutun ne?"
Ɗan mama ya ce "A'a ni nake tunanin hakan, bata motsi ko numfashi a yadda naga an sakata a mota wallahi da ƙyar idan ba mutuwa za ta yi ba"
Liti ya ce "Ɗan mama ko ɗan shegiya, gaba ɗaya yaron nan gaɓo ne, ya za ayi ka gaya masa wannan maganar?"
Walid ya karɓi wayar daga hannun Viper, ya saka a kunnensa ya ce "Ɗan mama kana ji na?"
"Eh oga Walid"
"Duk abun da ka ke ciki, ka din ga sanar da mu"
"To oga walid in sha Allah"
"Jikinta wutar ta taɓa ta ne?"
"A'a, ba ta ƙone ba, hayaƙi ne ya yi mata illa, wutar ma ba ta kama sosai ba"
"To shikenan, muna saurarenka"
Walid ya kalli idon Viper, yadda ya bayyanar da matsanancin tashin hankali.
"Viper, ka kwantar da hankalinka dan Allah komai zai zo da sauƙi, in sha Allah ba zata mutu ba, sai ta cika maka burinka"
Jiki a sanyaye ya ce "Walid yanzu shikenan duk wanda ya raɓe ni, rayuwarsa sai ta shiga hatsari, idan ita ma ta rasa ranta fa, jikina yana bani set up ne abun nan"
Liti ya ce "Kar ka zargi kanka, dama can wannan ba ta ji, kuma haryanzu ai bata fara shari'ar ka ba, balle ace saboda kai ne"
Walid ya ce "Ya isa haka liti, kai abu ba ya wucewa a wurinka"
"Yaushe zai wuce, tun da ta munafurce ni, ta saka aka kamani"
***
Abba kuwa Allah ne ya tsare bai yanke jiki ya faɗi na, bayan sanar masa da cewar, gobara ta kama a ofishin Nabila tana Asibiti.
Haka Nasir ma, cikin gigita da tashin hankali, ya nufi Asibitin da aka ce an kai Nabila.
Likitoci sun hana kowa ya shiga, an cire mata kaya an saka mata wata gown, ana duba jikinta ko da in da ta ƙone, amma babu, sai dai ga zuciyarta na bugawa, amma babu numfashi, idan tayi kamar zata yi numfashi, sai tayi ta tari, hayaƙi na fita ta hancinta da bakinta, sai tayi ɗif.
Gaba ɗaya Abba a rikice ya ƙaraso asibitin, cikin matsanancin tashin hankali Abba ya ƙarasa asibitin, zuwansa babu daɗewa Nasir ma ya ƙaraso, Abba ya nemi a bar shi ya ganta, amma aka ce ba a shiga likitoci na aiki tukuna.
Abba ya ce " 'ya ta ce, ko me za ayi mata ayi a gabana, idan ma ta mutu ne a bari na ganta, ai ni musulmi ne na kuma yadda da ƙaddara mai kyau ko mara kyau" suna ƙoƙarin lallaɓa shi ya haƙura kar ya shiga, ya burkice musu, babu shiri aka bashi damar shiga wurinta.
A kwance ya tarar da ita, ana ta allurai, ya ƙarasa gaban gadon ta ya zuba mata ido, dama ya lafiyar kura balle ta yi hauka, an sha wahalar ciwonta na asma sosai da sosai, sai da ta girma ta ɗan samu sassauci, tayi gado mai wahala, dan mahaifiyarta ce mai ɗauke da ciwon ta gada.
Ya kalleta a kan gado, sai ya ga ta koma masa kamannin mahaifiyarta sosai da sosai, lokacin da take gadon asibiti ta riƙe hannunsa a halin rashin lafiya.
Ya riƙe hannun Nabila, ya ga alamar akwai rai a jikinta, amma a galabaice take, ya daɗe yana yi mata addu'a, sannan ya tashi ya fita waje.
Barrister Kabir kuwa tuni suka yi reporting wurin Jami'an tsaro, aka zo aka fara bincike a kan musababbin tashin wutar, abun bai tsaya iya nan ba, sai da aka tattare masu gadin wurin, aka tafi da su wurin 'yan sanda domin fuskantar tuhuma.
Sumayya ma tun kan ta ƙaraso asibitin take uban kuka, saboda yadda aka gaya mata faruwar abun, ta riga ta fitar da rai Nabila tana raye.
Sai da Nabila ta shafe awa biyu, likitoci na procedure daban-daban a kanta, aka samu numfashinta ya dawo, sai dai a wahale take yin sa, aka fito da ita daga emergency, aka mayar da ita wani ɗakin.
****
Bunkure ta daki tebur ta ce "Tana raye kenan?"
Mutumin gabanta ya ce "Eh ranki ya daɗe, an samu nasarar fitar da ita daga wurin, amma na samu tabbacin tana raye, bata mutu ba sai dai tana cikin mawuyacin hali"
"Babu ruwana da mawuyacin hali, wannan wane irin aiki ne? Yaya za ayi ni ga yadda muka yi da ku, amma abun da ku ka yi daban?"
"Ba daga mu bane ba ranki ya daɗe, wallahi aiki an yi shi yadda yakamata, agajin gaggawa aka kai mata shiyasa"
Ta numfasa ta ce "Shikenan, zaka iya tafiya, a asibitin zan saka a ƙarasata".
***
Hankalin Viper bai dawo jikinsa ba, sai da ɗan mama ya dawo, ya tabattar masa da a kan idonsa aka fito da ita, tana raye, kuma ba ta ƙone ba, ko ƙwarzane babu a jikinta.
Nannauyar ajiyar zuciya Viper ya sauke, yana fatan Allah ya sa hakan, ya kuma bata lafiya.
Hatta 'yan gidan su Nabila, sai da suka tausayawa halin da take ciki, duk da ba shiri suke yi da ita ba, baba magajiya kuwa kuka ta ɗora hannu a ka ta din ga yi, ba ta san iya tashin hankalin da zata shiga ba, idan aka ce ba Nabila.
Sumayya na gefen Nabilan, ta riƙe hannunta tana ta matsar hawaye, tari ne ya kuma turnuƙe ta, kawai ta yinƙura zata tashi zaune, duk suka nufo kanta, Sumayya ta riƙeta tana kiran sunanta.
"Viper wuta, wani ya kulle ni ta waje, ku taimaka mini, Viper wuta" gaba ɗaya sai suka yi sak, suka zuba mata ido.
Abba ya ce "Waye kuma Viper?"
Cikin matsananciyar tuhuma Nasir yake bin ta da kallo, da yake ta surutai cikin fita hayyaci.
Barrister Habib ma sak yayi, Sumayya ta ce "Abba sunan wani ɗan daba ne, da take bincike a kan sa, maybe tana ƙadamin aiki a kansa ne abun ya faru"
Abba ya ce "Na rasa irin Arfa, wataƙila ma a dalilin wannan kwashe-kwashen nata, aka yi yinƙurin cutar da ita.
Barrister Habib ya ce "Bana tunanin haka sir, maybe ƙaddara ce kawai, ai tana yawan zancen ɗan daban nan ne, ta ce Yayanta shi ne incharge na nemansa tana fatan ta taimaka masa"
Nasir duk da ido yake bin su da kallo, yanayin yadda take surutan, kamar akwai sabo da kuma shaƙuwa a tsakanin su.
A hankali sumayya ta ce "Masoyiyya"
"Na'am sumy"
"Na'am"
"Wuta aka saka mini a office ɗina, da ta tashi, na tafi da gudu na buɗe ƙofa na ji an rufe ni ta waje"
Abba ya ce "A'a Arfa, Allah ne dai ya ƙaddara tashin wutar, kar ki zargi kowa"
Nabila ta ce "Abba, ni fa na buɗe office ɗin da kaina, na bar key a jiki ta waje na shiga, da wutar ta tashi na je na buɗe, na ji an murɗa key ɗin sau biyu"
Abba ya ce "Ki na cikin hayyacinki, kin farka gaba ɗaya?" Ta jinjina masa kai.
Ya ce "Alhamdilillah" nan aka din ga jera mata sannu, duk da tana ta haki a hakan ma.
***
Ramma ce a tsaye, ta shirya cikin doguwar rigar abaya, ta ɗora mayafin a kanta, Abdul ya bata facemask ya ce "Saka wannan" ta karɓa ta saka, ya ce "Wow, kin yi kyau sosai beb" ta yi murmushi tare da gyara mayafinta.
Ya riƙe hannunta, har cikin motarsa, da hannu ɗaya yake tuƙi, hannunsa ɗaya kuma ya riƙe nata, loka-lokaci sai ya sumbaci hannunta, yana jin wani irin so da shauƙinta yana ratsa ilahirin jikinsa.
"Ni ka daina shafa mini yawu a hannu"
"Haba Rahama, yawun ƙauna ne fa" yayi maganar yana satar kallonta.
Ta jingina da seat ɗin motar, ta numfasa ta ce "Yaushe ne bikinka, ko an yi ne?"
Ya ce "A'a, ya za ai, ayi ba ki sani ba? Wai bata ƙarasa karatu ba, da an so ayi ne idan ta dawo shikenan ta tare, babanta ya ce a bari ta gama, saura 2months"
Ramma ta ce "Allah sarki, ni nawa karatun ko oho, na zama karuwa"
"Haba rahama, dan Allah ki daina wannan maganar, ina da kyakykyawan tanadi a kan rayuwar ki da iliminki, na san na cutar da ke, amma zan gyara laifina in sha Allah" tayi masa shiru tana kallon titi.
Dare ne sosai, duk sahu ya ɗauke.
Ya zuba mata ido, a lokacin da take shan ice cream ɗin gabanta, ya tuna yadda yake ta fama da mahaifinsa, ya tsunduma tunanin ya zai yi ya sanar da shi batun ramma? Dan sai dai ayi wadda za ayi a kan ramma, amma bai ji duk iya bala'in da za ayi zai rabu da ita ba, ta kalleshi ta ce "Ka sha mana" yayi murmushi ya jinjina mata kai, mama ya cigaba da jujjuya cokalin.
Hakan ya sanya ta fuskanci a cikin damuwa yake, ta ɗebo icecream ɗin ta kai bakinsa, ya ɗaga ido ya kalleta, ya buɗe bakinsa ya karɓa.
Ya ce "Kin yafe mini dukan da nayi miki, kin daina fushi da ni?" Ta jinjina masa kai alamar eh.
"To ɗaya laifin fa?"
"Ban yafe wannan ba" ta bashi amsa kai tsaye.
"Tun da ki ka yafe wannan, wancan ma zaki yafe mini in sha Allah" ta yi shiru tana kallonsa.
Sai da ta gama ciye-ciyenta son ranta, sannan ya ce ta raka shi asibitin abokinsa, zai duba wasu marasa lafiya.
A zuciyarsa yake zargin kamar wani cikin ne da ramma, amma bai tabattar ba, kuma bai ambata ba, balle ta tashi hankalinta, muddin kuma ya ce zai gwada za ta gane, kuma ta daina yarda da shi, dan ce mata yai, yayi mata allurar planing, ba zata sake ɗaukar ciki ba sai allurar ta sake ta.
Waɗanda ya yi wa tiyata a asibitin ya duba, sun fito take tambayarsa "Nan ne asibitinka?"
Ya ce "A'a, Asibitina na can wajen gari, na kan je wasu asibitocin da aka buƙace ni, na gabatar da aiki, zan kai ki namun ma ki gani"
Ramma ta ce "Naka dai"
"A'a namu dai, idan komai ya daidaita, ai bikinmu za ayi, na nuna wa duniya ke, komai ya wuce"
Ta ce "Taɓ kwaɗo"
Babu tsammani yayi karo da wata matashiyar budurwa, hannunta riƙe da ledar Pharmacy.
"Ke ba kya gani ne?"
"Ban gane bana gani ba, kawai ka zo ka tsaya a hanya, kana rangwaɗa, da alama kai jin daɗi ne ya kawo ka asibitin ba mara lafiya ne da kai ba" Ramma ji tayi kamar ta san muryar.
A fusace ya yinƙura zai yi masifa, ramma ta ce "Dan Allah ki yi haƙuri, mun tsare hanya kam, Allah ya ƙara afuwa ga mara lafiyan"
Sumayya ta amsa da "Amin" ta harare shi ta wuce.
"Dan Allah ka din ga rage faɗa, har marasa lafiyar ma, faɗa ka ke yi musu, haba kai kuwa" ƙwafa yayi suka tafi.
***
Sosai Viper yake son kiran wayar Nabila, amma babu hali, dan ɗan mama ya tabattar masa da ya ga an fito da wayarta, da jakarta da system ɗin ta, wani mutum ya karɓa, amma alamu sun nuna a wurin yake aiki shi ma.
Viper bai san waye ya karɓi wayar da system ɗin ba, akwai ayyukansa a cikin system ɗin ta, da suke buƙatar sirri sosai da sosai.
Nasir ya karɓi system ɗin Nabila da wayoyinta a hannun barrister Habib, sai dai ya kasa buɗewa, dan bai san menene password ɗin ta ba, har su walida ya tambaya ko sun sani, suka ce ba su sani ba.
Ƙaramar wayarta kawai ya iya buɗewa, sunan confidential ya fara nema, yayi sa'a ya samo lambar, sai dai ya duba lambar da aka yi saving a kan sunan, ya tarar da suna babu lamba, ya duba ya duba, amma ya rasa samun lambar, ya din ga kwafar lambobin wayar, yana dubawa a Truecaller ɗin sa, amma babu wani suspicious abu da ya samu.
Yanzu tantamar da yake yi a kan Nabila, ya wuce zargi, akwai abun da take aikatawa na rashin gaskiya, ya ƙallafa ransa sai ya gano, waye wannan mutumin da ya gansu tare sau biyu.
A kunne ya bar wayoyin, sai dai yadda aka din ga kira babu ƙaƙƙautawa, tun yana ɗagawa yana saka ran, zai samu wani abu na information, harya haƙura ya daina ɗagawa.
Nabila ta farga da rashin wayoyinta, ta tambayi a bata wayoyinta, aka ce mata suna wurin Nasir, ta jira ya zo Asibitin ta ce ya kawo mata wayoyinta ya ce ba zai bayar ba.
Cikin mamaki ta ce "Amma meysa na san za a neme ni a wayar?"
Ya ce "Kina fama da kanki, uban me zaki yi da wata waya?"
Sumayya ta ce "Ke ma dai arfa, uban meye a wayar ne, ki hutawa kanki ki gama farfaɗowa" kallon Nasir take yi, tana nazarin irin kallon da yake yi mata, ta fara fatan Allah ya sa ba wani abun ya gano a wayar ba.
Abba ne ya shigo, suka gaggaisa, ya din ga tsokanar Sumayya tare da Nabila, ko wurin aiki Sumayya ba ta zuwa, tana liƙe a asibiti da Arfa, Sai da Nabila ta magantu a kan wurin aikin sumayya amma ta basar da ita.
Ƙwanƙwasa ƙofar ɗakin aka yi, sannan aka buɗe.
Jmau'an tsaro ne da bindigogi suka fara shigowa, gaba ɗaya suka yi ƙuri da ido, suna kallonsu.
Alhaji wada m karofi ne ya shigo, suka gaisa da Abba, Nasir ma ya gaishe shi.
Nabila ta ce masa "Lafiya, wannan kama ni za su yi?"
Yayi murmushi ya ce "Saboda ke ce Sarkin laifi ba, yaya jiki ashe haka wannan iftila'in ya faru?"
"To ai na ganka da yan sanda me na yi?"
Yayi mata shiru, suka ƙarasa gaisawa da Abba suka gaisa, Sumayya ta ce "Ina kwana?"
"Lafiya ƙalau T ladan, ya gidan radio?"
"Yana nan sir"
Nabila ta ce "Dama kin san shi?"
Sumayya ta girgiza kai.
Ya ce "Eh ba lallai ta sanni, amma ita muryarta sananniya ce ai, kuma kina bani labarinta ai, ko ba sumayya T ladan ba ce?"
Sumayya ta jinjina kai tana murmushi.
Nan yake gaya wa Abba, ai a law firm ɗin Barrister Kabir yake ganin Nabila suke gaisawa, shi yake sanar masa tsautsayin da ya faru.
Nasir dai ya din ga mamakin yadda karakainar Nabila, ta kai ga ta ga sanin manyan mutane har haka, bayan ya gama duba ta, yayi musu sallama ya tafi, Nasir ma da Abba tafiyar suka yi, aka bar sauda da Sumayya, suna tafiya Saudan ma ta shura takalmanta ta fice, dama ba son zaman take yi ba.
Sumayya ta kalli Nabila ta ce "Nabila na ajiye aikina fa"
Nabila ta waro ido ta ce "What? Saboda me?"
Sumayya ta numfasa ta ce "Hakan shi ne yafi dacewa ne"
"Sumayya wannan ai wauta ce, meyasa zaki ajiye aikin?"
"Na gaji da barazanar da ake yi mini, da tashin hankalin da ake yi mini, Allah ya taimake ni an shiga tsakanina da indabo, ya rabu da ni, amma support ɗin da muke baki, da ni da yaya murtala baki ga rashin mutuncin da ake yi mana ba, ga hantara da tsangwama. Da barazanar kora babu yau babu gobe, na ajiye musu bakin da Allah ya tsaga ba ya hana shi abun da zai ci"
Cikin matsanancin damuwa Nabila ta ce "Sumayya baki kyauta mini ba, da ki ka ɓoye mini wannan babban al'amari haka, ki rasa aikinki a dalilina, haba sumayya".
Sumayya ta yi dariya ta ce "Kar ki damu, umma ma ta sani, kuma ta bani ƙwarin gwiwa yaya murtala yana yi mana processing ɗin wani sabon gidan radio, za su bani aiki da ni da shi, shi ma baro can zai yi, su ci kansu"
Cikin damuwa ta ce "Sumayya duk da haka ban ji daɗi ba, idan kuma ba a samu aikin ba fa?"
"Zafa a samu in sha Allah, na bawa yaya murtala cv na, ya ce mini sun yi murna sosai da jin zan koma wurinsu, sabon gidan radio ne, za a buɗe dama lawisa a ƙule take da ni, ta ƙara takura mini, saboda mutane suna yi na, sai su kwaɗa gidan radion su cinye"
Nabila ta numfasa ta ce "Sai mu duƙufa addu'a masoyiyya, Allah ya sa ki samu ya tabattar da dukkanin alkhairansa"
"Amin, amma Nabila wannan wutar kuwa ba set up bane ba, ana sane aka sakata ba?"
Nabila ta ce "Set up ne mana, sai da na shiga na zauna sannan ta kama, na taho na fita kuma, aka sakawa ƙofar key"
"Wa ki ke zargi?"
Ta girgiza kai ta ce "Bana zargin kowa, abun da nake yi ne dai ba zan bari ba"
"Nabila"
"Na'am sumayya T ladan"
"Haryanzu kina zuwa in da Viper yake kuna haɗuwa?"
Nabila ta kalleta ta ce "Wace irin tambaya ce wannan?"
"Amsa zaki bani, ba ki tambaye ni ba"
"Ban ga gurbin yin tambayar a nan ba, ko dai haryanzu yaudarata ki ke yi, aiki ki ke yi wa Indabo a kaina?"
"Ko kaɗan, indabo ma Allah ya yi mini maganinsa, ya rabani da shi, amma alamu sun nuna kina haɗuwa da Viper, da sunansa ki ka farfaɗo a bakinki"
"Tuhumata ki ke ko zargi?"
"Babu ɗaya"
"To idan har ba aiki ki ke yi wa wani a kaina haryanzu ba, to ki bar maganar nan"
Sumayya ta ce "Shikenan, an bar ta"
Likita ne ya shigo, ya kalli Nabila ya ce "Barrister jiki yayi kyau, jiya doctor yasar ya shigo, ai da na sani nayi masa magana ya duba jikin naki, idan da wani abu da zai ƙara miki"
"Doctor ni dai dan Allah ka sallame ni, na gaji wallahi"
"Ki yi haƙuri, zai sake shigowa yanzu, mun yi waya da shi, zai ga masu hawan jini kan ya wuce, kin san shi abun ne ya haɗar masa, ga siyasa ga kuma aikin likita"
"Ashe kuwa zaka neme ni ka rasa a asibitin nan, tafiya ta zan yi na gaji"
"No ba za ayi hakan ba, bari na rubuta miki sallama, Alhamdilillah ai jiki yayi kyau sosai".
Sumayya ta ce "Mun gode sosai doctor"
Tashin hankalin da Indabo yake ciki a yan kwanakin nan, duk sai tsufansa ya fito, ko bacci baya iya yi sai ya sha ƙwayoyi, saboda damuwa da tashin hankali.
Cikin dare ya ga kiran Wada karofi, ransa ya ɓaci kamar kar ya ɗaga, sai kuma ya ɗaga ya ce "Karofi wani irin wulaƙanci ne ya sanya kake kirana ƙarfe ɗaya na dare?"
"Kashedi, da kuma gargaɗi, Nabila ta tsallake wannan tarkon da kuka yi mata, kamar yadda na taka maka burki a kan ƙawarta, ina mai ja maka kunne a kanta, wallahi wani abu ya samu yarinyar nan, zan yi abun da baka so"
"Wacece