Showing 303001 words to 306000 words out of 479911 words
har ƙofar ɗakin da Viper ya rubuto mata, wasu masu sanye da kaki, suka tarar a ƙofar ɗakin a tsaye, Nabila suka gaisa, ta ciro id card ta nuna musu.
Suka ce ta shiga, amma ban da sumayya, Nabila ta ce "Ita ma ma'aikaciya ce, yar jarida ce"
Suka ce "A'a kekaɗai aka ce mu bari ki shiga".
Sumayya ta ce "Ba damuwa, zan jira ki a nan"
Nabila ta shiga, ta yi sallama ta tarar da mutum a zaune a kan gado, hannunsa ɗaya an saka masa sarƙa, ƙafarsa kuma ɗaya an yanke ta.
Ta ƙarasa gaban gadon, ta ja kujera ta zauna, ta kalleshi ta ce "Sannu malam"
Ya ce "Yauwwa"
Ta ciro id card ta nuna masa ta ce "Sunana barrister Nabila, na zo ne a kan case ɗinka da Al'amin mai zamani.
Ya ɗago ya kalli Nabila amma bai yi magana ba.
"Ka yi magana, dan ka sauƙaƙa wa shari'a, me ka sani game da kisan da aka yi wa matar mai zamani?"ya yi shiru ya ƙi magana.
Tayi tayi, amma yaƙi cewa komai, ƙarshe haka ta fito bai yi magana ba.
Sumayya suna ta hira da security ɗin wurin, Nabila ta fito, tana ganin Nabila ta tashi ta ce "Kin gama?"
Nabila ta ce "Eh mu tafi"
Suna tafe ta kira Viper a waya, ta ce "Hello V snake"
"Barrister"
"Naje wurin gayen nan, amma yaƙi magana, nayi nayi, yaƙi magana"
Viper ya ce "Rabu da shi, zai yi ta ƙarfin tsiya, ki tafi kawai"
"Ok, na ma taho, amma yakamata yayi magana gaskiya, bari na ƙarasa gida sai anjima" ta kashe wayar.
Sumayya ta ce "Nabila wai wurin wa ki ka zo ne?"
"Zan yi miki bayani, amma ba yanzu ba"
Ta ce "Ok shikenan"
***
"Rahama kina ji na?"
"Ina jinka"
"Zamu sake barin gidan nan" "Zuwa ka mayar da ni gida?"
"Wai na mayar da ke gida ki yi me? Ai kin san iya wuya muna tare, nan zamu bari temporarily, daga can kuma zan kai ki gida, sai kuma makaranta, a abuja zaki koma da karatu ai"
"Yar ƙauye a Abuja, to ai ban iya turanci ba, ni gaskiya na fi son makarantar garinmu"
Abdul ya yi dariya ya ce "Ai Shiyasa zaki je Abujan, zaki iya turanci, kan ki gama ki ƙara gogewa ki zama her excellency rahama"
"Taɓ abun ma ba tsari"
"Kamar ya babu tsari?"
"Wata zaka aura ai, kuma ni a lokacin mutane zasu ji daɗin nuna ni suna aibata ni"
Abdul ya girgiza kai ya ce "Muna tare, babu wanda zai aibata mini ke"
Ramma ta yi murmushi ta ce "Ba zaka iya canza komai ba, ɗabi'ace ta al'ummar hausawa"
Ya ce "Shikenan, mu bar maganar"
Ta ce "Ya dai fi"
Wayarsa ya ɗaga, ya ɗan gyara zamansa ya ce "Na'am Mummy"
"Wato Abdul kafi son ka yi ta sakani a tashin hankali da damuwa ko?"
"Mummy me nayi kuma?"
"Ban sani ba, ka saka babanka yana yi mini kallon ni nake goya maka baya ka ke yi masa rashin ɗa'a, ka fito da yarinyar nan ka huta su huta ka ƙi, rashin mutuncinka har ya kai ka ajiye mace kana lalata da ita, bayan na keta mata haddi,, ga ɗan uwanka can an mayar da shi america, sai abun da Allah ya yi, shiyasa ake ta fafutukar ka zama gwamnan nan ko a samu ya fito, amma ka ƙi, ya ka ke so na yi Abdul, in bar muku duniyar ka huta ko?"
Cikin damuwa ya ce "Mummy ki yi haƙuri dan Allah, ki fahimce ni, ya za ayi na so ki mutu, ba haka bane ba. Wallahi Mumm tsoro nake ji na fito da yarinyar nan, ayi mata wani abu na daban, dan Allah ki yi haƙuri, zan zo gida nayi miki bayani, na san zaki fahimce ni in sha Allah. Kuma yaya jafar zai fito in sha Allah, ki yi haƙuri dan Allah"
"Ai shikenan, ka yi abun da ka ke so"
"A'a ba za ayi haka ba, zan zo har gida nayi miki bayani" ta katse wayar, yayi ajiyar zuciya yana lumshe idanunsa ya buɗe yana kallon ramma, da ta yi kamar ba ta jin me yake faɗa a wayar.
"Rahama"
"Na'am"
"An sakoni a gaba a kanki"
"An san ka sace ni kenan?"
Abdul ya ce "Ke fa ba a abun arziki da ke, ke da ban sace kin ba, da yanzu wani zancen ake ba wannan ba"
"Ai ba da kyakywar manufa ka sace ni ba, kashe ni ka ce zaka yi"
"Amma ai ban kashe kin ba ko?" Tayi masa shiru ta cigaba da aikin ta.
****
Nabila ta fito daga banɗaki, kawai ta tarar da Nasir a tsaye a ɗakinta, ta kalleshi ta ce "Lafiya?"
Ya ɗago mata file ɗin Viper da yake hannunsa, ta bar shi a kan gadonta tana aiki, ya faɗo mata ɗaki.
"Menene wannan?" Ta ƙarasa gabansa ta saka hannu zata karɓa, ya janye yana sake tambayarta "Menene wannan Nabila?"
"Babu ruwanka da ko menene, ka bani file ɗina kuma ka daina shigo mini ɗaki ba tare da iznina ba"
Cikin tsawa ya ce "Ki yi mini bayani kin tsaya kina wasu kame-kame da wasu maganganun banza da na wofi"
Cikin dakewa ta ce "DSP aikina nake yi, ka fita daga harkata ka bani file ɗina"
"Nabila, ta tabatta goyon bayan ɗan ta'adda ki ke yi?"
"Ni bayan gaskiya nake bi, kawai, ka bani file ɗina"
"Nabila kina haɗuwa da mutumin nan, kin san in da yake"
"Ni ban san in da yake ba, ka bani file ɗina tun ina ganin mutuncinka"
Shammatarsa tayi, ta kafa masa haƙora a hannunsa, ba shiri ya sakar mata file ɗin, ta kwashe abun ta tayi waje, ya bi ta da kallo, ya kalli hannunsa yadda yake tsatstsafar da jini saboda iya ƙarfinta ta cije shi.
Cikin yarfe hannu, ya bi bayanta, sai dai ko sama ko ƙasa ya nemeta ya rasa a cikin gidan nan.
Zuciyar sa ta daɗe tana mamakin abun da ya gani, amma haryanzu ya kasa gazgata cewar Nabila tana haɗuwa da Viper, ta san in da yake, amma me zai haɗata da ƙasurgumin ɗan ta'adda haka tana ya mace, idan kuwa haka ne, duk hukuncin da doka tayi a kanta shi ba zai ce komai ba, amma ya yanke ya sake tuntuɓar Abba, ya kirata ya ja mata kunne, a lallaɓata a cikin gida idan da abun da ta sani, a sasanta abun, kar asiri ya tonu, dan shi kansa abun kunya ne a gare shi, ace yana can yana haƙilon neman ɗan daba, Nabila na zagewa ta haɗu da shi a ɓoye.
Da daddare Nabila na zaune a falon Abba, ga Nasir a gefe, sai kuma shi kansa Abban, tayi shiru ta sunkuyar da kai fuskarta babu annuri.
"Arfa" Abba ya kira sunanta a kausashe.
"Na'am Abba"
"Gaske ne abun da ɗan uwanki ya gaya mini?"
"Abba ai ban san me ya gaya makan ba"
Abba ya gyara zama ya ce "Gaske ne, kin san in da wanda yake ta haƙilon nema yake? Nabila meye haɗinki da ɗan daba ne? Kina 'ya mace?"
Ta girgiza kai ta ce "Abba ya za ayi na haɗu da wanda yan sanda ma suka kasa kamawa, file ɗin shari'arsa kawai ya gani a ɗakina, kuma ba nawa bane ba, na barrister Habib ne, nima karɓa nayi na duba, ina dudduba yadda aka gudanar da shari'ar sa a wancan lokacin ne, an ce yayi shekara biyar a prison ba ayi masa shari'a, kwatsam kuma aka ce an sake shi, aka dawo ana nemansa sai nake jin kamar akwai wani ɓoyayyen lamari, shi ne nake ta bibiya, ka san muna program da sumayya, so ina binciken cases makamantan nasa shi ne kawai, amma sai zargina yake yi, ni ban san meyasa ba"
Abba ya yi ajiyar zuciya ya ce "To kai ka ji abun da ta ce, me zaka ce?"
Sam Nasir bai ji ya yarda da abun da Nabilan ta faɗa ba, amma ya ce "Shikenan Abba, tun da haka ta ce"
"Dan Allah ku daina wannan rigingimun, da ba haka kuke ba, naga tare kuke sharing working experience ɗinku, amma yanzu kuna nema ku lalata tsakaninku, ni ban ji dama arfa zata iya bin wani ɗan daba ba, tana ƙyamar irin wannan laifukan, dan haka dan Allah duk ku yi haƙuri Allah ya yi muku jagora, ya rufa muku asiri"
Nabila ce ta fara miƙewa ta amsa da Amin, ta fice tana hararar Nasir, shi kuma ya bi bayanta da kallo, sam bai yarda da ita ba.
Washegari aka dawo da motar Nabila, an gyarota fes har fenti an canza mata, ta ji daɗin dawowar motar nan, dama yawan zirga-zirgar nan ya isheta.
Ɓangaren sumayya ma, nata program ɗin da take gabatarwa a kan shirin siyasa, na an yi walƙiyya, yana ta jan dubban masu sauraro, sakamakon yadda take baje wa mutane komai, game da irin kuɗaɗen da gwamantin tarayya take bayarwa domin ayyukan raya ƙasa, ta kan ɗauki ƙananan hukumomin shiyya ɗaya, ta kawo kuɗin da suka samu na wata, na tarayya, na jiha da na ƙanan hukumomin, da iya ayyukan da aka yi musu.
Sai dai tun da ta zo kan na Indabo, a ƙalla tafi sati uku, program ɗin a kansa yake, dan sai da ta faro tun daga farkon tenure sa, yadda take hawa da sauka a kansa, zai tabattar maka akwai wata a ƙasa tsakaninta da shi. Yan siyasa da dama, sun kawo wa program ɗin hari, da neman a dakatar da shi, amma hukumar gudanarwa ta tashar suka tabattar da cewa an riga an biya su ɗaukar nauyin program ɗin, dan haka ba zasu dakatar ba, wanda bai gamsu ba, ko ya ji an yi masa sharri ko cin zarafin sa, to ya kai kotu.
Da safe Nabila ta fito da motarta, sai ƙyalli take yi, ta batta a kunne, ta shiga gida ta haɗo kayan breakfast ɗin ta, ta koma cikin mota, Viper ya kirata a waya.
Ta ɗaga ta ce "Hello V snake"
Cikin dakakkiyar muryarsa ya ce "Kin fita aiki ne?"
"Ina ƙofar gida ne, yanzu zan tafi ka tayani da addu'a, yau zan kai kokenmi kotu"
Ya ɗan ja numfashi ya ce "Ki bi ta farkon layinku, wurin incomplete building ɗin nan, ina nan ina jiran ki"
"Ok sir, gani nan"
Ta ja motar ta ƙarasa in da ya ce mata, a wurin ta tarar da shi, ya tako a hankali, cikin nutsuwa. Ta zura masa ido tana murmushi ba tare da ta san tana yi ba.
Ya shigo ya rufe ƙofar, ta kalleshi ta ce "Good morning"
"Morning" ya amsa ba tare da ya kalleta ba, ya ajiye mata baƙar leda.
Ta ɗauka ta ciro abun ciki, baƙar riga ce, da sunansa a jiki Viper, da hoton maciji.
"Wow masha Allah, har an yi mini? Na gode sosai, wai waye yake yi maka rigunan nan?" Yayi shiru bai amsa mata ba.
Sai kuma ta ce "Sanyin Ac yayi maka normal ko na rage?" Kawai ya jingina da seat ɗin motar ya zuba mata ido.
Sai ta ɗan rikice ta ce "Menene? Ko wani abun ne?" Still bai yi magana ba.
Ji tayi tsigar jikinta na tashi, ta ce "Dan Allah ka gaya mini menene?"
"Ina jin ƙwarin gwiwa a kan shari'ar nan, wanda ke ki ka bani shi, and at the same time scared, idan rayuwarki ta salwanta saboda ni, ba zan yafe wa kaina ba, dan rayuwar ki kika saka a haɗari saboda ni, na zo ne in ce miki good luck"
Duk da ta takura da kallon da yake yi mata, tamkar ta nutse, ga wata fargaba da bata san ta mecece ba, amma ta dake ta ce "Allah yana tare da mu, in sha Allah zamu yi nasara"
"Allah ya sa, ko mun yi nasara ko bamu yi ba, ina da kyakykyawan tukuici gareki"
"Ni zuciyarka kawai nake so, shi ne tukuicin da nake so" haɗe rai yayi ya ce "You are not serious, ba zaki daina wannan shirmen ba ko? Wahala zaki yi ta sha kuwa, ba na kallon kowace mace mace idan ba jauhar ba, ki je ki samu wani ku daidaita" yayi maganar ba tare da ya kalleta ba, yana ƙoƙarin buɗe ƙofa ya fita, jikinta har yayi sanyi, idonta ya cika da hawaye" yayi saurin ficewa, ba tare da ya sake kallonta ba. A guje ta fizgi motar, ta bar wurin, wanda hakan sai da ya bashi dariya, dan ya san fushi ta yi.
Nabila tana tafe hawaye na zuba daga idanunta, duk ta ɓata kwalliyar ta, sai taga kamar zata yi nasara, kawai sai ya buntsure, gashi ita kullum ƙara son sa take yi so mai zafin gaske.
Da haka ta ƙarasa court, ta tsaya ta ƙara gyara fuskarta, sannan ta fita ta shiga cikin court ɗin.
Nabila ta nemi kotu, ta hana hukumar 'yan sanda kama Muhammad Al'amin Ibrahim, da aka fi sani da Viper, har sai an yi cikakken bincike a kan kisan kan da aka yi wa matarsa shekaru biyar da suka gabata, hakazalika yana neman hakkinsa, na tsare shi shekaru biyar ba tare da yi masa shari'a ba, a kan laifin da ba shi ya aikata ba. Ta gabatarwa kotu kwafin shari'ar da aka yi masa a baya.
Duk da ba ma a fara shari'ar ba, amma haka nan ta din ga jin tamkar ta kama hanyar sauke gingimemen nauyin da yake kanta.
Abun da Nabila bata sani ba shi ne, tuni aka kira Nasir, aka sanar masa da an ganta da wani, a wurin sabbin gine-gine da ake yi a unguwar, kamar yadda ya saka CID ta ko ina a kanta.
Ya shiga kitchen ɗaukar lemo a fridge ya tarar da wayar Nabila a kitchen tana ringing, ita kuma bata kitchen ɗin, ya ƙarasa in da wayar take, kiran ya yanke. Ya kalli wallpaper ɗin ta Hoton sunan Viper ne, da maciji a kan wallpaper da wani heart.
Ya saka hannu ya ɗauki wayar, wani kiran ya kuma shigowa.
Kawai ya ɗaga kiran ya saka a kunnensa ya ce "Waye?"
"Viper ne, mai zamani
Ayshercool
08081012143
73
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Ina ma'abota bibiyar litattafan bright pens, ƙarƙashin mikiya writers association, marubutan da suka kawo muku CUTARWA, MUNAFUKIN MIJI, YI WA KAI, A first batch ga second batch, ƘARFE A WUTA, MUTALLAB ya fara zuwar muku da na sa saloz sai kuma ZAYTOON DA HADARIN GABAS NA NAN TAFE SUMA A CIKIN WANNAN WATAN, KAR KU BARI A BAKU LABARI.
Cak Nasir ya ƙame, a daidai lokacin da Nabila ta dawo kitchen ɗin.
"Wa ka ce?"
"Sarai ka ji abun da na ce, kar na sake kiran waya, ka ɗaga mini, ka bawa mai wayar, zan yi magana da lawyer ta"
Hakan yayi daidai da shigowar Nabila da take tsaye a bayansa, ya waiwayo ya kalleta, ya miƙa mata wayar yana tsareta da idanunsa da ya zazzaro su, tamkar zasu faɗo ƙasa.
Ta saka hannu ta karɓi wayar, tayi ƙasa da murya, ta ce "V ka kashe ni"
"Shhh ki tsaya ki saurare ni"
Ta ce "Tom"
"Yaya zaki yi da batun shaidun nan? kin ce gayen nan yaƙi magana, ina so zan je in da yake da kaina"
"To ai ka ga ni ban san me ma zan ce ba, ban san wace hukumar ta ce ta kama shi ba, dole yan sanda zamu shigarwa koken su kama shi".
"Na fahimta, na san abun da zan yi, dama na zata zai yi magana ne, ki samu wani abun as shaida, amma na san abun da zan yi masa, zai yi magana ta ƙarfin tsiya. And am sorry for what i did, na san zan saka ki a matsala, amma hakan ka iya zama maganin wasu matsalolin naki, dole za a zo wurin nan, cigaba da ɓoye-ɓoye ba zai haifar da ɗa mai ido ba, no matter what it takes, duk tsanani da ƙalubalen da zaki fuskanta ki jure, da Allah na dogara, amma kekaɗai ce ƙwarin gwiwa ta, Please don't give up"
"Kar ka damu, in sha Allah I won't, i promise you that"
"Thank you" ya katse wayar, hankali kwance ta kammala wayar, Nasir ya zuba mata ido, yana jiran ta gama, ya ji wace ƙaryar za ta yi masa, kawai ya ga ta basar, ta cigaba da abun da yake gabanta.
Da ƙarfin tsiya, ya janyo kafaɗarta ya tsayar da ita tana fuskantar sa, ya ɗaga hannu zai kwaɗa mata mari ya ji muryar Baba magajiya "A'aaa lalalalaaaaa me zan gani haka, a kul ɗin ka, kar ka kuskura fara me yayi zafi zaka dakar mini 'ya Nasir" tayi maganar tana nuna shi da yatsa, Nabila kuwa da gudu ta gudu ta ɓuya a bayanta, tana ƙifta idanuwa.
"Ammm baba magajiya, ki fita daga cikin maganar nan"
"Ban gane in fita daga maganar nan ba, zaka kassara mini ƴa ka ɗaga hannu zaka daketa, ƙarfin ka da nata ɗaya ne?" Ai tana rufe baki, ya ture baba magajiya ya danƙo Nabila ya fara janta.
Tirjewa ta din ga yi, tana zunduma ihu, tana a taimaketa zai kasheta.
Baba magajiya ta sake biyo su, tana yi masa masifar ya saki Nabila. Sai da ya kaita tsakiyar falo, sannan ya kalleta cikin ƙunar rai ya ce "Nabila umarni nake baki, a yanzu yanzu cikin gaggawa ki sanar mini ina wannan ɗan iskan ɗan daban yake, kafin na tafi da ke na kulle ki, Nabila wace irin mahaukaciya ce, kina iƙirarin ke mai gaskiya ce, amma kina take doka kina ɓoye mai laifi?".
"Ni ban taka kowace irin doka ba, bisa doron doka nake gudanar da aikina"
"Shut up, ki gaya mini in da yake, kafin na saka ankwa ke na tafi da ke, na je na kulle ki"
Nabila ta ce "Ka kulleni a nayi maka laifin me?"
"Tambayata ki ke sake yi saboda kin raina mini hankali, ko bayan wannan hujjar wata ki ke nema? Am disappointed on you, kin bani kunya Nabila, ban taɓa tunanin duk wannan haƙilon da ki ke yi, zaki iya cin amanar ƙasa ba, kuma ki ci amanata ba"
"Ban ci amanar kowa ba, ni ba maciyiya amana ba ce ba"
"Ba zaki yi mini shiru ba, sai na tattakaki tukuna? Ki na ɗiya mace daga gidan daraja da mutunci, amma ki zubar wa da kanki kima, dan ba zan ce mu ki ka zubar wa ba, ki gaya mini ina ce maɓoyarsa, kafin ke nayi arresting ɗinki"
"Kayi arresting ɗina like how, DSP lawyer ce fa ni, lawyer ma mai zaman kanta, ina da ikon kare duk wanda ya zo gabana ya nemi hakan, duk girman laifin da ya aikata kuwa, balle wannan da makauniyar shari'a kawai ake yi. Ba ka da ikon kama