Showing 93001 words to 96000 words out of 249515 words
wallahi bazan fada ba, kinsan babu boye boye tsakanina da ke to nima wllh sarowa nake wajenta in ɗan yi mix sannan in daura nawa riban in siyar, yanzu in na gaya maki ai gun ta zaki nufa direct gashi nata shine sadidan haka kawai ki saka bawan Allah ya zama makale mata ki ja a koresa aiki, gwara dai ki tsaya iya nawa me mix" Haseenah tace "Kai kawata, wallahi ni ko biyanki kika ce inyi sai in biyaki ki bani numberta, fadi price in tura maki yanzu" Salima ta kwashe da dariya tace "Yanzu duk ba wannan ba, Hajiya cikon kudin Malam fa? Kinsan fa har da nasa aikin, ko kinji ya sake maki wancan maganar me muni?" Haseenah tace "Cewa ma yayi sharrin shaidan ne wllh, kar fa ki ji komai duk zan tura kudin casss, sannan akwai ma wani matsalar yanzu haka Salima, amma kinsan ance the wall have ears, don haka mu yi chatting kawai" Salima tace "Toh shkkn bari in kunna data" Katse wayar Haseenah tayi ta bude WhatsApp dinta. After sleeping all day Mayraah ta bude idonta a hankali ta dalilin hannun da taji a forehead din ta, suna hada ido ta mike zaune da sauri tana murza ido tana kallonsa, yace "How are you feeling?" A hankali tace "Alhamdulillah, ina yini?" Yace "Lafiya lau" Maheer ya karaso wajen nasu yana kallonta yace "Are you okay now?" Ta gyada masa kai, Usman ya juya ya koma kan kujera ya zauna, Maheer yace "Me za ki ci?" Usman yace "I will get her, idan mun fita, it's getting late now" Maheer yace "Ohk, baza ki shiga bandaki ba, za ku fita da Barrister" Mayraah ta kalli Usman, sai kuma ta sauko daga kan gadon ta dau handbag dinta ta nufi bandaki, zata iya daukan pad a gaban Maheer but not Usman tun tasowarta, Maheer dai ya bi ta da kallo ya koma office chair dinsa ya zauna, ko da ta fito daga bandaki Maheer kawai ne a office din, yana kallonta yace "Yana jiranki a mota" Ta marairaice tace "Ina za mu je yaya? Kasan bani da lafiya" Maheer yace "Ai ba dadewa za ku yi ba, zai dawo da ke soon" Ta ɗan yi shiru, sai kuma ta nufi kofa ta fita......
MAYRAAH is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah
Ur evidence 07087865788
[6/26, 7:46 PM] Khaleesat Haiydar💖: Mayraah na isa parking space din asibitin ta nufi motar Usman, ta bude front seat ta shiga ba tare da ta kallesa ba, ya tada motar suka bar asibitin, babu wanda yace koma cikinsu har suka yi nisa, Ita dai sai baza ido take ta ga inda zai kai ta, after many minutes ride ta gane inda suka nufa, nan da nan jikinta yayi sanyi sai take jin abubuwan da suka faru suna dawo mata sabo a zuciyarta, a cikin compound din gidan yayi parking ya juya yana kallonta sannan ya bude motar ya sauka, Mayraah ta kasa fitowa daga motar, gani take kamar za su ga Hajja a gidan, har sai da Usman ya zagayo ya kwankwasa motar yace "Za a sauko da ke ne?" Sunkuyar da kanta tayi ta sauko daga cikin motar ya kulle, sannan ya fara tafiya ta bi bayansa har suka shiga gidan, babu kowa a parlon, ta zauna kan kujera kamar wata bakuwa, Usman na kallonta da mamaki yace "Are you okay? Baxa ki tafi sama ki gaida Ammi ba?" Bata ce komai ba ta mike ta wuce sama tana tafiya a hankali, ya bi ta da ido, Mayraah ta kai minti biyu tsaye bakin kofar parlon Ammi ta kasa shiga ciki haka kawai take jin gabanta na faduwa har Usman ya hauro saman, bata bari ya karaso wajenta ba ta bude kofar a hankali ta shiga ciki tare da sallama, Mama Ladi dake zaune da kwanon abinci a gabanta ta tura kwanon ta wagale hannu tace "Lahh jama'a ga Mera, ga Mera" Mayraah suka hada ido da Ammi dake zaune parlon gefen Mama Ladi, Ammi ta kasa daina kallonta ko kiftawa babu, karasawa Mayraah tayi ta duka kusa da ita tana kallonta tace "Ina yini Ammi" Ammi bata bari sun sake hada ido da ita ba, ta jawota jikinta a hankali tace "Lafiya lau Mimi, ya jikin naki?" Mayraah ta sunkuyar da kanta tace "Da sauki" Mama Ladi dake ta washe baki tace "Haba gashi yarinya har tayi kyau tayi kumari ta kara haske da ta bar gidan nan na kwana biyu kawai, amma da duk an bi an sa ta a bakin duniya, baki yayi mata yawa ta ko ina sai hayagaga tsofaffi da yara suke da sunanta gashi ba a san bakin wani ba, wannan yace yeyeyen wancan yace yeyeyen, ba tsoho ba yaro" Ammi dai ta kara jan Mayraah jikinta kamar zata maida ita ciki, ji take kamar an yaye mata duk wani damuwa dake tattare da ita a moment din nan, she just felt a lot of strength da ta rasa na kwana biyu nan, ita kanta Mayraah felt relieved in Ammi's bosom, and for the second time tun faruwan abubuwan nan taji kawai ita bata ma yarda Ammi is not her mother ba, she just can't believe that, don ita dai a duniya bata da uwa sama da Ammi.... Usman na shiga parlon Abba ya zauna ya gaishesa Abba ya amsa yana kallonsa yace "Ya jikin nata?" Usman yace "Da sauki, tana wajen Ammi" Abba ya ɗan yi shiru, sai kuma ya nisa yace "Usman ta yaya kake ganin zan fara yi ma Mayraah magana ga me da asalinta ta yanda hankalinta bazai tashi ba? I really don't want to hurt my daughter, though she is already hurt, what if she is healing in sake dawo mata da zancen? yanzu kamata yayi ace kwantar mata da hankali za ayi giving her hope ba kara daga mata hankali da wannan issue din ba Usman, ko na ce zan mata magana ban san ta inda zan fara ba" Usman ya daga kai ya kalli Abba yace "Abba babu amfanin boye mata komai ga me da asalinta a yanzu dai don abinda zai faru ya riga ya faru, abinda ya sa she is this hurt is because ba a bakinku ta fara jin ku ba iyayenta bane, don haka bai kamata ayi shiru a ki ce mata komai ba har yanzu, dalilin abun nan fa yasa aka fasa aurenta Abba, as if that is not enough Hajja ta billo da nata matsalar which is uncalled for, to ta yaya za ayi mata shiru and we keep on acting like everything is okay whereas ba haka bane, shirun nan zai fi mata ciwo a kan telling her who she is a yanzu dai, you need to talk to her Abba, nasan ita Ammi bazata iya ba" Abba ya nisa yace "I will, amma i don't think zan bazan bude mata komai kamar yanda na bude maka" Usman yace "Abba just tell her everything once and for all, idan ma baka gaya mata ba zata ji a wani waje wataran tunda kaga yanzun ma a wani wajen ta fara ji" Abba ya sauke ajiyar zuciya yace "To bari mu dawo masallaci, it's almost Magrib now" Mayraah na zaune gefen Ammi dake kan darduma ta idar da sallahn magrib, tuwon da Ammi ta sa Sabira ta kawo mata take ci a hankali, Mama Ladi ta rufe akwalan akwatinta tace "Kala uku ma sun isheni zaman duniya ba na kiyama ba a gidan, banda ma dai Badiyya ta kwace Rigar Maman da ta ban ai ba sai na debi kaya har kala uku ba" Ammi dai bata ma san abinda Mama Ladi ke cewa ba don duk hankalinta na kan Mayraah dake cin tuwo a hankali, sosai taga ta rame kamar ba Mayraan ta ba, kuma kana kallon fuskarta zaka san akwai damuwa still a tattare da ita, Mama Ladi na kallon Mayraah tace "Wannan dai dakin da na zabar maki aka baki a gidan?" Mayraah ta daga kai ta kalleta sannan ta gyada mata kai, Mama Ladi tace "Ahau ai dama nace naki ne dakin, kuma girmansu daya da dakin Sasinar, kinga su suna daga can gefe ke kuma ga ki a naki gefen babu ruwanki da harkar matar don naga er iska ce ta bugawa a jarida" Ammi ta juya ta kalli Mama Ladi , Mama Ladi na zare mata ido tace "Kwarai kuwa er iska ce, ai ta min iskancin ne, naga kina wani kallona" Ammi dai ba abinda tace mata, Bude kofar parlon aka yi duk suka juya, Usman ya shigo da sallama yana kallon Mayraah yace "Ina jiranki a corridor" Mayraah ta kalli Ammi, Cikin sanyin murya Ammi tace "Why not leave it till around 10" Usman yace "Abba wants to speak to her" Ammi tace "Ohk, bari ta gama cin abincin" Juyawa yayi ya fita daga parlon, Mama Ladi tace "Ji jaraba kamar Allah Allah ma yake ya fita da ita daga gidan, anya da gaskiya cikin lamarin 'ya yan nan naki kuwa?" Ammi dai bata ce komai ba, Mayraah ta rufe abincin gabanta duk da ta dan ci ba laifi, Ammi tace "Baki cinye ba ai" Ta girgiza kai tace "Na koshi" Mama Ladi ta mike tana kokarin kinkiman akwatinta tace "Maza wanko hannu mu tafi" Ammi ta juya ta kalli Mama Ladi da mamaki, can dai tace "Abba ne fa ke kiranta Mama Ladi" Mama Ladi tace "Aihoo, to je ki dawo, ina nan ina jira" Mayraah ta wanke hannu ta fita, tsaye ta tadda Usman a corridor, ya maida wayarsa da yake dannawa cikin aljihu ya nufi parlon Abba ta bi bayansa, tun da ta shigo Abba ke kallonta, ta zauna kasan carpet cikin sanyin murya tace "Abba ina yini" Abba ya sauke boyayyen ajiyar zuciya yace "Lafiya lau daughter" juyawa Usman yayi ya bar masu parlon. Usman na dawowa parlon Ammi tayi masa turanci tace ya jirata waje zata masa magana, Mama Ladi dai tayi kishingide a parlon tana jiran dawowan Mayraah daga wajen Abba, Bayan yan mintuna Ammi ta mike tana kallon Mama Ladi tace "Bari in hada ma Alhaji abincinsa a kitchen" Mama Ladi tace "Toh ba laifi, maza je ki" Daga haka Ammi ta fita daga parlonta, can bakin stairs ta tadda Usman a tsaye yana jiranta, Ammi ta karasa kusa da shi da damuwa tace "Usman kana gani fa Mama Ladi ta hada akwati wai zata bi Mayraah gidan Maheer, abinda ya kamata fa shi ake yi, me zata je tayi gidan yarinya da aka kai ko kwana biyar ba ayi ba yau fisabilillah? Ita kanta Mayraah in sha Allahu kafin nan da sati biyu komai zai daidaita ta dawo gida, wllh ba da son raina take gidan Maheer ba i just don't have choice for now, ji nake kamar wani part of me ne baya tare da ni yanzu haka, kuma abinda yasa ma na hakura da zamanta gidan Maheer din nasan bazai bar ta cikin damuwa ba, to ga wannan tsohuwa wai ita lallai lallai sai ta bi Mayraah, ita Haseenar adalci aka mata? Wannan ai ba ma abinda hankali zai dauka bane, At the first place ma bai yi ace daga tarewarta an kai mata yarinya ba in dai adalci za a bi" Duk da Usman ya hango Mama Ladi da ta makale jikin bangon kusa da karfen stairs din bai ce komai ba har Ammi ta kai aya, Usman ya gyara tsayuwarsa yace "Toh yanzu ya kike son ayi Ammi?" Ammi tace "Kawai kace mata baza ka tafi da ita ba, iyaka tayi fadanta ta gaji ta kwanta, ko kuma kace mata Maheer din da kansa zai zo ya dau Mayraah, kaga sanda za ku fita ma bata sani ba" Murmushi kawai Usman yake yana shafa beard dinsa, Mama Ladi tayi wani tsalle ta fito sarari tayi mitsi mitsi da ido tace "Ashe dai ba Mariya kadai ta iya munafurci ba" Usman ya juya yana dariya ya sauka downstairs ya bar su wajen, Ammi tayi tsuru tsuru a tsaye, Mama Ladi tace "Amma wallahi kin ban mamaki, kuma naga dai ba gidan uwarki Hajja nace zan je ba gidan Mashir zan je balle ki min iyaka, kuma gidan Mashir kamar na je wallahi ban ga wanda ya isa ya ki kai ni ba ko a kafa zan nemo gidan, haka kawai bazan zuba ido wannan guzumar da ya ajiye a gida ta cuci Mera ba duk Allah ya kama mu tunda dai zuwa yanzu babu wanda bai san Mera marainiya ce da aka tsinta a bakin masallaci cikin kwali ba, sannan kiyi ta makala ma matar nan yarinya, wai an gaya maki matar Mashir yarinya ce? Ta fa girmesa don ma ki ji in gaya maki, ni tun a ranan da aka kawota daki ta gaishemu na dauka Bazawara ce kawai dai na ja bakina ne nayi shiru kada ace na cika surutu" a hankali Ammi tace "Kiyi hakuri ni ba haka nake nufi ba Mama Ladi" Mama Ladi tace "Kya dai ci kanki, gidan Mashir kamar naje wllh" Daga haka ta juya ta bar ta tsaye a wajen. Abba na kallon Mayraah dake ta hawaye ya dafa kanta yace "In sha Allah next week Maheer zai maido ki gida, Allah maki albarka" ta kasa cewa komai ta gyada masa kai hawaye na sauka idonta.... Parlor Mama Ladi ta dawo ta zauna da akwatinta a gaba tana jiran fitowar Mayraah don tun da Usman ya fita Masallaci sallan Isha bai shigo ba, Mayraah ta sauko downstairs Mama Ladi ta mike tace "Dau akwatin mu tafi, yana can waje yana jiranmu har ya fita da mota" cikin sanyin murya Mayraah tace "Kitchen zan shiga" Mama Ladi tace "Wai ya ku ke abu kamar ba kwa kallon agogo, karfe takwas da rabi fa yanzu" Mayraah tace "Shayi zan dafa" Mama Ladi ta koma ta zauna tace "Da can da suka biye Hajja uban wa ke dafa mata shayin in ba gulma ba" Ita dai Mayraah ta shiga kitchen din ta kulle kofa, a hankali ta bude kofar baya kamar yanda Usman yayi instructing dinta ta fita sannan ta rufe, ta zagayo zuwa gaban compound ta nufi gate ta fita da sauri, yana cikin mota yana jiranta, ta bude front seat ta shiga sannan ya ja motar suka bar layin.....
Mayraah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah
Ur evidence via 07087865788
[6/27, 8:07 PM] Khaleesat Haiydar💖: Usman yayi parking dai dai kofar gidan Maheer, sannan ya kalleta yace "Sae da safe" Tace "Yaya za ka kawo min jakar gobe?" Yace "Kiyi me da shi?" Tace "My handout is inside" Bai kuma cewa komai ba, ganin haka ta bude motar tace "Sae da safe" Yace "Allah ya tashe mu lafiya" Sauka tayi ta kulle masa motar sannan ta nufi gate, yana tsaye har ya ga shiganta compound din gidan kafin yayi reverse, Mayraah na tsaye bakin kofa tayi knocking a hankali ta koma gefe ta tsaya, jin shiru yasa ta sake kwankwasawa, bude kofar aka yi suka yi ido hudu da Haseenah, Haseenah tayi mata wani matsiyacin kallo tare da jan dogon tsaki ta mayar da kofar ta kulle da karfi sannan ta saka makulli, Mayraah bata san sanda ta taɓe baki ba, tayi unlocking wayarta dake hannunta tayi dialing number Maheer, yana fara ring ya daga yace "Kun dawo ne?" Tace "Ehh" yace "Ohk let me open the door for you" Daga haka ya katse wayar, sai ga shi ya fito parlor daga Bedroom, Haseenah dake zaune kan kujera ta bi sa da kallo har ya nufi kofar parlon, budewa yayi yana kallon Mayraah, sai da ta shigo parlon yace "Usman din ya tafi?" Ta gyada masa kai, yace "Ohk zan baki spare key ki rike a wajenki" Haseenah dae sai girgiza kafa take tana kallon TV fuskarta babu yabo babu fallasa, Mayraah ta nufi dakinta ya bi ta da kallo yace "Ina jakar?" Tace "Ya Usman zai kawo min gobe" Yace "Ohk" Daga haka ta wuce dakinta ta kulle, Maheer ya ɗan kalli Haseenah ya zauna gefenta yace "Where is the black tea i asked you to make for me?" Bata ce masa komai ba, yace "Baby i am talking to you" bayan some seconds ta mike ta nufi kitchen ya bi ta da kallo, sae da ya ga ta shiga kitchen din sannan ya tashi ya tafi dakin Mayraah, tsaye ya ganta tana linke Hijab dinta, ya kulle kofar yayi kasa da murya yace "But why didn't u greet her Mimi?" A takaice tace "She shut the door in my face" Yayi shiru, ta gama linke Hijab dinta zata ciro kayan da zata canza taji yace "Amma da kinyi hakuri kin gaisheta..." Juyawa tayi tana kallonsa, ya ɗan shafa kansa yace "Kinga ai Aunt dinki ce Mimi and she deserves some respect" Mayraah tace "Is that why she should close the door on me? Did she think i want to be here too??" Nan da nan hawaye ya cika idonta, dai dai nan aka bude kofar dakin Maheer ya juya da sauri, Mayraah ta ajiye kayan baccin da ta ciro ta dau pad da inner wear dinta tayi shigewarta bandaki ta bar su wajen, Maheer na kallon Haseenah dake masa wani irin kallo yace "Har kin dafa shayin?" Ta watsa masa kallo daga sama har kasa ta bar bakin kofar, ya bi ta har zuwa Bedroom dinsu. Ko da Mayraah ta fito makulli ta sa ma dakin ta sa kayan baccinta ta kwanta, ko kadan bata bari abinda Haseenah tayi ya tsaya mata a rai ba cause that's not her concern for now, damuwarta yanzu dalilin da yasa Musharraf ya ki kiranta throughout today, dialing numbersa tayi, after ringing for a while ya daga, kamar yana ganinta ta hade rai tayi shiru, daga daya bangaren yace "Ya jikin ki?" Kamar zata yi kuka tace "Sae da na kira ne zaka tambaye ni?" Yayi shiru, kafin yace "I called, not reachable" tace "You didn't" yace "Yanzu dae ba an kula da ke kin samu lafiya ba?" Tace "Toh shikenan, sae da safe" Yace "Wait..." Bata katse wayar