Showing 123001 words to 126000 words out of 249515 words
kudin gold din nawa da kika ce za a biya wannan malamin na biyu da shi na fasa, kawai a bani kudin gold dina ko inyi rashin mutunci, dama can ni ba ruwana da harkan Malamai kika wani tashi kika hada ni da Malami" Sai da gaban Haseenah ya fadi tsabar rikicewa da jin abinda Badiyyah ke cewa don murya a sama tayi maganar yanda in dai mutum na balcony ma zai jiyo ta, Haseenah ta dinga kalle kalle da sauri to be sure Maheer baya wajen zuciyarta na wani bugawa, tuni Badiyya tayi wucewarta ta bar ta nan a tsaye, kawai yau ta dawo gida cike da farin ciki don har numberta sai da Dr Musharraf ya amsa bayan ta samesa a office da wani topic a course dinsa amma rashin ganin abinci a gida ne kawai ya ɓata mata mood dinta gaba daya don ita bata wasa da cikinta, bayan tun da take bata taɓa irin wannan farin cikin da tayi yau ba wai a whole Dr Musharraf yayi requesting phone number dinta zai tura mata wani slide ta WhatsApp kawai Haseenah ta wani ɓata mata mood dinta.... Throughout this week was nothing but hell for Mayraah bata yi tunanin zata yi surviving har zuwa ran friday ba, sosai ta rame duk da kokarin da yayyin nata maza suke don a rana sai su zo wajenta sau biyu sau uku amma ta kasa samun sukuni gata nan gata nan dai ne kawai, ga karatu yaki tsaya mata a kai, she try all her best tayi composing kanta idan sun zo, amma suna tafiya zata koma gidan jiya, taji duniyar ya isheta komai yayi mata zafi, she just want to see her self far away, may be in a another world, kullum da wannan feeling din take kwana take tashi a ranta, amma da taji zuciyarta na ingizata ta aiwatar da hakan sai ta tuna final exams dinta.. Yau Sunday tana kwance ita kadai a daki Ummi ta shiga School karatu wayarta ya fara vibrate, ta jawo wayar taga Dr Musharraf ne, tun da ya kirata Tuesday, Wednesday, Thursday bata daga ba bai sake kiranta ba sai yau Saturday, tana ta kallon wayar har ya katse, ya sake kira, dagaws tayi ta sa handsfree tayi shiru, yace "Ki gaya min me na maki kike avoiding calls dina Mayraah? Yayyinki suka hanaki daga kirana ko?" A takaice tace "Saboda me za su hanani daga kiranka?" Yace "Toh gashi nan baki dagawa all this while, we were good, all of a sudden u stopped responding to my calls Mayraah, kin ga dole zan yi tunanin hanaki ɗaga wayata aka yi" Ta ɗan yi shiru, sai kuma tace "It's not so, bani da lafiya ne" Da mamaki yace "Really? but i asked Badiyyah about u yesterday and she said u are fine kince a gida zaki dinga karatun ki" Mayraah dai tayi shiru, yace "Mayraah ki gaya min me yake damunki plss?" Tace "Ai na ji sauki" cike da damuwa yace "Pls ina son ganinki yau, where can i meet you?" Tace "Ai zan shigo school gobe" yace "Da gaske?" Tace "In sha Allah" yace "Amma kina karatun sosai kuwa, next week fa exams din ku" Tace "Ina yi, yanzu ma shi nake yi...." a hankali yace "Ohk in kyaleki ki cigaba kenan?" Tace "Yeah" yace "Toh zan kira ki anjima" katse wayar tayi ta ajiye ta ci gaba da kwanciyarta... Washegari karfe goma da rabi Usman ya ajiyeta a school, a parking space ta ga motar Dr Musharraf, Usman na kallonta bayan ta sauka daga motar yace "In kin gama ki kirani" a hankali tace "Ya Maheer yace zai zo ya daukeni" Shiru Usman yayi, sai kuma yace "Ok" ya ja motarsa ya bar wajen, ta shiga department din nasu, sosai gabanta ya fadi ganin Dr Musharraf na saukowa stairs tare da wani lecturer dinsu, tun da ta kallesa sau daya ta sunkuyar da kanta ta rasa dalilin da zuciyarta ke bugawa da sauri da sauri, shi ma kallonta kawai yake ta cikin glasses din idonsa, ba tare da ta sake kallonsu ba ta gaishesu ta wuce, inda suke sallah a department din ta nufa tana tafiya a hankali, gabanta ya sake faduwa ganin Badiyyah zaune da kawayenta biyu tana basu labari duk sun cika wajen da muryarsu, Badiyyah ta daga kai tana kallon Mayraah da mamaki, ita wllh har ta manta da ita a duniya, mamaki ta dinga yi tana tunanin daga ina kuma take haka, dama tana nan ashe, can ta wani kyabe baki ta ci gaba da ba kawayenta labarin da take basu, da har Mayraah zata juya ta bar wajen sai kuma dai kawai ta zauna ɗan nesa da su ta ciro handout dinta tana kallo amma surutunsu duk ya cika mata kunne, Badiyyah tace "In gaya maku har karfe dayan dare we were chatting with him wallahi tallahi" Kawarta Aisha tace "Shi Dr Musharraf din?" Badiyyah ta kyalkyale da dariya tace "Wallahi nake gaya maki, bari ma ku ga" da sauri ta ciro wayarta ta shiga WhatsApp tana nuna masu chat dinta da Dr Musharraf, duk suka zaro ido da mamaki suka ce "Whatttt" Badiyyah dai sai murmushi take ta mayar da wayar jakarta, sai kuma ta fito da wani tsadadden foreign coffee a kwalinsa tace "Toh da yace min yana son coffee shine na dauko masa wannan coffee din a gidan yayana in basa, kun san yanzu gidan Maheer nake for almost a week now, shine ma ke kawo ni school yanzu, dama warce ta shiga tsakaninmu da su yanzu an koreta a gidan, familyn mu ya dawo dai dai yanzu, don haka sai kun ga yanda Maheer ke ji da ni a gidansa wllh tllh, sai ma da na gaya masa zan dauki coffee din kafin in dauka" Aisha ta zaro ido tace "Ke ga Dr Musharraf din na hango ashe ya shigo school din" Badiyya tace "Kai haba" Aisha tace "Wallahi kuwa na ganshi yana tafiya upstairs" Badiyyah ta ciro powder dinta da sauri ta shafa sannan ta fito da wani turare a kwalba ta shafa tace "Bari in kai masa Coffee powder din yanzu kawai" Sai da ta kusa taka Mayraah da gangan sannan ta bar wajen, ita dai Mayraah kanta na kasa tana jin duk hiransu, ta dai kafa ma takardan hannunta ido babu ko kiftawa......
MAYRAAH is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah
Ur evidence via 07087865788
*Wato idan kina neman turaruka masu musulmin kamshi, irin turaren nan da komin bacin rai dole ya narke yabi ruwa🫠 kiji kamar kinyi bargo da gajimare. Toh ki nemi Scentmania_by_sana by sana 07065525409 kawai kice ta baki 'The Empress combo'. Irin turaren dake sa maigida ya nemi shiri cikin gaggawa. In kinason kiyi activating din inner gimbiyarki👸🏽instantly wannan combo din shi ya dace dake.*
[7/5, 9:45 PM] Khaleesat Haiydar💖: Mayraah ta daga kai a hankali tana kallon wata Coursemate dinta da ta dafa shoulder dinta, Farida ta buda ido tace "Duk karatun ne haka Mayraah, have been talking to u since fa" Mayraah ta kirkiri murmushi ta ajiye handout din hannunta tace "Ayya ban sani ba Farida, ya kwana biyu?" Farida tace "Lafiya lau wllh, ya preparation din exams?" Mayraah tace "Alhamdulillah" project supervisor din su daya da Farida wato Dr Musharraf, dama su biyu kadai ne project student dinsa, Farida tace "Supervisor dinmu na kiranki, wani chapter kike yanzu ne? I submitted my chapter 4 just now" Mayraah tace "Ohk, ni ban yi submitting ba" Farida tace "Ohk yace ki je yana jiran ki" Mayraah tace "Toh" Tun barin Badiyyah wajen for almost an hour Mayraah ke zaune ita kadae a gun don kawayen Badiyyan ma tuni suka bar ta a wajen, bayan Mayraah ta maida handout dinta cikin jaka da wayarta da ta saka a Flight mode tun daxu, ta mike ta wuce sama bayan sun yi sallama da Farida don tace gida zata wuce. Office din Dr Musharraf Mayraah ta nufa, tana tsaye bakin kofa tayi knocking gently, sae da yayi mata permission din shiga sannan ta shiga ta kulle office din, shi kadae ne zaune office din amma ba kan office chair dinsa ba yana danne danne a laptop, ya daga kai yana kallonta, ita dai bata bari sun hada ido ba, kwalban coffee dake kan table dinsa kawai take kallo, ta isa har wajen table din ta tsaya kusa da kujeran dake facing din wanda yake zaune without looking at him tace "Good afternoon" Bai amsa ba ya cire glasses din idonsa yace "Na kira wayarki a kashe, so da ban ce a kiraki ba baxa ki shigo ba kenan, i think ko don saboda project dinki ma ai ba sai kin bari na kira ki ba" Shiru tayi taki cewa komai, Musharraf dai kallonta kawai yake, har sannan kuma bata bari sun hada ido da shi ba, bayan few seconds tace "Ana jirana, za mu tafi gida" Ganin bai bata amsa ba ta juya zata bar office din ya riko hijab dinta, bata san sanda ta warce ba ta juyo tana kallonsa da kyau tace "Kar ka sake pls" Ya mike yana kallonta yace "Are you okay?" Ta gyada masa kai furiously tace "I am very much okay, kawai nayi regretting relationship dina da kai ne tun daga farkonsa har yau, i just realized u are the reason i am going through all this, nayi da na sanin haduwata da kai...." Dr Musharraf ya koma ya zauna yana kallonta yace "Really?" Mayraah was trying so hard to control her self kar ta fashe da kukan dake cin ta tace "I regret everything...." A hankali Musharraf yace "I should be the one regretting Mayraah, ni aka yi ma damage so i should regret not you" Kallonsa kawai take zuciyarta na bugawa, can ta juya ta nufi kofa shi dai bai ce mata komai ba, har ta rike handle din kofar ta juya tana kallonsa with regret tace "I regret trusting you, i hate my self for believing in you har na kusa saɓa ma Allah, i will never forgive u for this...." Musharraf yayi kasa da murya yace "I don't understand, ni na sa kiyi saɓon Allah? How?" Hawaye cike idonta tace "Ae zuwa gidanka ma da abinda ka so yi min saɓon Allah ne" Yace "Na taɓa cewa ki zo gidana? Of course no, kawai ke kika ga ya kamata ki zo but ni ban taɓa ce maki ki zo ki sameni a gida ba...." Kallonsa kawai Mayraah take babu ko kiftawa, lokaci daya ta juya ta fice daga office din ta share hawayen idonta bayan haka kuma bata sake jin hawayen ya taho mata ba, ko minti daya bata kara a makarantar ba ta wuce hostel din da take, tana isa hostel din first abinda ta fara yi shine goge duk numbers din Dr Musharraf a wayarta bayan tayi blocking dinsa, ta shiga WhatsApp ma tayi blocking dinsa ta nan, kwanciya tayi gefen gado taji hawaye me zafi na sauka idonta kamar an bude pampo, kalmominsa na karshe ne kawai suka dinga kai komo a brain dinta, tayi da ta sanin zuwa ta samesa a gidansa, tayi mugun da na sani, she wish she neva did that, ta fashe da kuka sosai, tayi me isarta sannan ta mike ta dau wayarta ta shiga timetable din exams dinsu tana dubawa, don tun fitowar timetable din sau daya kadai ta duba, after checking the timetable ta fiddo complete handouts dinta ta jera su according to the timetable sannan ta shiga bandaki ta dauro alwala ta fito don an kira azahar. Karfe hudu da rabi Mayraah ta fito waje ta dalilin kiranta da Usman yayi, yana tsaye jikin motar ta karasa ta tsaya gefensa ta gaishesa, ya amsa yana kallonta yace "Ya kike?" Tace "Alhamdulillah" Yace "Kina karatun sosai?" Ta daga kai ta kallesa tace "Ina yi" Ya ɗan yi shiru, sai kuma yace "Zan yi tafiya gobe zan je wani aiki, so i don't know how long zan tsaya a can kafin in dawo...." Mayraah tace "Toh Allah ya tsare, i will be fine in sha Allah" Yace "Sure?" Ta ɗan yi murmushi tace "In sha Allah" Usman bai wuce 30 minutes ba ya wuce, Mayraah ta koma cikin hostel, har ranta dama taji bata ma son kowa ya dinga zuwa wajenta daga yanzu she just want to be left alone, and she is happy Usman is traveling tunda shi bazata iya gaya masa she wants to be left alone ba, Maheer kuma dama zata iya masa magana without any fear zata ce masa tana son ta dinga karatun ta without distraction..... Daren ranan Maheer ya zo, Mayraah ta gaya masa abinda ke ranta, bai iya ya ce mata komai ba at first, ita dai tana ta jiran abinda zai ce, bayan wani lokaci yace "Haka kike so Mimi?" Ta gyada masa kai tace "Yea, i want to concentrate fully, za mu dinga shiga school tare da Ummi from morning till evening don inyi karatu sosai" Maheer ya sauke ajiyar zuciya, yau kam yaji da confidence dinta take magana kamar ta samu motivation from somewhere, a hankali yace "Shikenan, if that is what u want Mimi...." Bata ce masa komai ba and she was expecting taga ya tashi ya tafi, can ya juya ya kalleta yace "Amma ai zan iya dinga zuwa sau daya in ganki?" Ta girgiza kai tace "Aa yaya, i said i can take care of my self, even Ummi that is in level 2 babu wanda yake zuwa nan dubata kullum, and i am not a kid" Maheer dai kallonta kawai yake, can ya ɗan yi murmushi yace "To shikenan, nasan zaki kula da kanki Mimi, today is Monday, in sha Allah Wednesday zan zo in ganki, hakan yayi ko?" Ta ɗan hade rai tace "Aa yaya, i said i can take care of my self, I am not a kid" Bai kuma ce mata komai ba, ita ma haka, a ranta kuwa ta kagu ya tashi ya tafi ta wuce ciki abunta, she just hate the sight of everyone har cikin ranta, bayan few minutes yace "Shikenan zan tafi, i will be calling u Mimi" Tace "Thank you" Daga haka ta mike ta shige cikin hostel din ya bi ta da kallo.... Har ya koma gida jikinsa a sanyaye yake, kullum addu'ansa Allah ya kawo karshen wannan abun ko zai samu rest of mind, a kofar gida yayi parking don yana son zai je wajen Ammi bayan magrib, yana shiga cikin gidan ya zauna parlor, kamshin girki ne ya cika gidan alamar ana girki a kitchen, can dai ya mike ya nufi corridor, dai dai nan Badiyyah ta fito daga dakin Haseenah kusan a guje rike da turmin atamfa uku ta cusa a cikin leda, sosai ta tsorata ganinsa ta koma gefe tana gwale ido sai rufe bakin ledan take kar ya ga meye a ciki, da kamar bazai ce mata komai ba sai kuma yace "Kin dawo" Tana kame kame tace "Eh, dama, eh dama yanzun nan nima na dawo, ajiya na bata shine na dauko yanzu" Yace "Ohk" Daga haka ya bude dakinsa da yake kullewa da makulli ya shiga ya rufe, Badiyyah tayi saurin shigewa dakin da take ta bude jakarta ta saka turamen atamfar ta kulle jakar, ta zauna gefen gado tana sauke ajiyar zuciya. Haseenah ta gama tuwo da miyar vegetable da take ta juye komai a cooler ta fito daga kitchen din, zaune taga Badiyyah a parlor, ko sanin Badiyyar ta dawo bata yi ba don tun karfe uku take kitchen kamar me girka abincin mutane goma, sai yanzu biyar da rabi ta fito, Haseenah ta dake tace "Aa kin dawo ashe" Tun da Badiyyah tayi mata maganar kudin gold few days back ta ɗan fara sake mata sama sama tana kauda kai a abubuwa da yawa sai dai ita kadai tasan plan din da suka yi ma Badiyyah ita da Cousin sister dinta Ramlah, Badiyyah na tauna chewing gum tace "Yanzun nan na shigo ae ko daki ban karasa ba" Haseenah tace "Ko zaki dafa Indomie don tuwo ne malmala biyu ya sa in masa, nasan ke baki cin tuwo" Badiyyah ta hade rai tace "Ni nasan yanda ake wani dafa Indomie, kuma yaushe nace maki bana cin tuwo" Haseenah tayi wucewarta ta bar ta a wajen, bata so Badiyya ta dawo gidan bata gama girki ba, so tayi ace kafin ta dawo ta gama tayi maza ta shige daki da shi ai dai bazata ce tayi girki ta hanata ba, duk saurin da take wai ashe har Badiyyar ta dawo.... Haseenah tayi wanka sharp sharp ta fito daga dakinta wajen karfe shidda, har sannan bata san Maheer ya dawo gidan ba tunda bai shigo da mota ba, Badiyyah ta gani tsaye corridor tana kwankwasa kofar dakin Maheer, Haseenah ta koma gefe tana kallon ikon Allah thinking yaushe Maheer ya dawo, Maheer ya bude kofar yana kallon Badiyyah, Badiyyah ta wani narke murya tace "Yaya don Allah subscription zaka min, nawa ya kare kuma abu ake koya min a WhatsApp for my exams" Haseenah da zuciyarta ya hau tafarfasa ta dinga kallonsu da mamaki, wai dama Maheer ya dawo gidan nan, to ko dai tare ma suka dawo tana can kitchen bata sani ba, Maheer na kallon Badiyyah yace "Ohk, kamar na nawa kike so?" Ta washe baki ta jingina da bango tana wasa da hannun rigarta tace "Yaya ko na dubu goma ne kawai kayi min nagode" Maheer yace "Ohk, naga kin kara haske wani mai kike shafawa ne haka?" Haseenah taji brain dinta ya tsaya cak for some minutes, Badiyyah tayi wani er siririyar dariya tace "Wallahi dama yaya cream din ma ya kare da soap, haka ma turarena sun kare" Yace "Sai a siya maki ai, zan je gidan Hajja yanzu ki shirya sai mu fita tare daga nan sai mu je supermarket din..." Badiyyah na wani blushing tace "To yaya bari in shirya, nagodeee yayana" Daga haka ta shige dakinta da sauri, Maheer ya kulle kofar dakinsa duk suka bar Haseenah wajen a tsaye kamar