Showing 327001 words to 330000 words out of 391264 words

Chapter 110 - Cigaban Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel

11 Feb 2025

2645

Imam, Ya girgiza da jin basu dawo Danish ba, wlh yaji zafi acikin zuciyar shi..

Girgiza kai yai idanunsa cike tab da ?walla.

Ya dan jima batare daya furta kalma ba, Can ya numfasa cikin karyayyar murya yai masu nasiha akan suyi hakuri da rashin da sukayi Su mika lamuransu gurin kada su sare, Danish kuma zasu tayashi da addu'a in ya mutu Allah yajikan shi In kuma yana araye Allah ya bayyanar da shi.

Sannan Ya bukaci yana son yaje ya duba su Salsabeel chief yace idan suka tashi zuwa zai kirashi sai suje atare su duba jikin su saboda asibitin ba a kusa yake ba.

Shiru sukayi falon yai tsit kowa da abunda yake sakawa acikin zuciyar shi.

"Ina auntynku? Ko itama tana a dayan bangaren ne"? Kaitsaye maganar shi ta dira a kunnan Ummi tayi mamakin Jin sheikh Imam ya tambayeta.

"Tana anan tare da mu" Batool ce ta bashi amsa..

Batay niyar fitowa ba amma saboda maganar sheikh Imam yasa ta fito jikinta sanye da dogon hijabin data dauko a cikin closet din su Unaisah.

Har kasa ta zukunna ta gaishe da shi fuskarsa da fara'a ya amsa mata, ta danyi mamaki mutumin da ko kallonta baisonyi amma yau haryake tambayar tana ina.

"Hateem Yasan da maganar"! Girgiza kai chief yai"ban sanar da shi ba ko da zaiji ba yanzu ba,"

Sheikh yace"Allahu akhbar, Allah baya barin wani don wani yaji dadi, Hateem yaso yaron nan kamar dan cikinsa, nasan in yaji hankalinsa ba karamin tashi zaiyi ba"

ya fada fuskarsa da damuwa jikinshi duk yai sanyi, Zuciyarsa ta karaya, saboda shi kan shi yaso yaron kuma bakomai yafi daga masa hankali ba face kin kar6ar shahadar da baiyi ba.


"Sheikh ga Unaisah nan, Har yau bata daina sanya damuwa aranta ba, dakyar muke samu tayi bacci, dan Allah ay mata nasiha.." Taj ne yai maganar.


Ya tambayi meye silar ciwonta, Taj ya fada masa komai.

Tsananin tausayin su ne Ya kama shi, Cikin sanyin murya ya farayi masu Nasiha har na tsawon mintuna talatin kafin Ya gama gaba daya jikinsu yayi sanyi lakwas, Imani ya kara shigarsu sosai.


Har wurare karfe 9 Shiekh Imam yana agidan daga bisani yai masu sallama Chief Ya rakasa Har cikin motarsa sai da yaga tafiyarsa kafin ya juyo.

Time daya shigo falon ya tsinkayi muryar Ummi tana fada ma Taj Unaisah taki cin abinci.

Da damuwa akan fuskarsa yace"Why Unaisah? Baki so ki samu lafiya ne? Ai ta fama dake akan kici abinci"


Muryarta kasa kasa ta furta"Zuciyata ke tashi,duka abincin da naci da safe dana rana saida na amayar da su a toilet, ban fadi maku bane saboda bana son in tada maku hankali, abincin ma bana jin dadin shi ..."


Kafin wani ya furta kalma muryar Chief ta katse su.

"Gobe idan dr yazo duba ki ki fada masa aman da kike yi, amma bazan bari ki kwana da yunwa ba, Fada min me kike son Ci"

ya fada tare da dafe Sofa da hannayensa Yayin da idanunsa ke akan fuskarta.

Saboda nauyin shi da take jine yasa ta ce"zan daure naci wanda aka kawo min"

"Ina abincin nata yake" Batool tace"yana a daki"


"Je ki Wauko min" mikewa ta yi da sauri ta nufi dakinsu.

Jim kaWan sai gata ta dawo hannayen ta ruke da tray ta ajiye shi kan rug.


Zagayowa yayi tare da samun wuri Ya zauna a gaban tray din, mamakin chief ya rukesu Musamman daya Kira Unaisa Ya nuna mata gaban tray din Yace tazo taci abinci"

Ta dan zaro idanu tare da kallon Taj fuskarsa Wauke da murmushi yai mata alamar taje mikewa tay jiki ba kwari ta zauna tana fuskantarsa, yayin da tray din ya raba tsakanin su.

Coconut water ya dauka da sauri ta mika yatsun hannunta dake kerma da niyar ta kar6i Glass din
Batai aune ba taji ya kanga mata strawa din a baki, wata irin kunyace ta kamata, adan rude ta saci kallon su ummi da Taj fuskokinsu dauke da murmushi..


Ganin ta ki motsa lips dinta yasa shi furta"ki sha" yawu ta hadiya ?utt kafin a hankali ta fara zukar shi, abunda tagaza sha dazu sai gashi ta kwankwade shi duka batare da ta ankara ba har saida ya janye straw din daga bakinta.


Spoon ya dauka Murya na rawa ta furta"zan iya ci da kaina" ta fada tana kyafkyafta gray eyes din ta
Hakan ba karamin Jan hankalin shi yai ba.

"Ki bari ya baki mana Unaisah, Baki ga yadda hannunki ke kerma ba taya zaki iya ruke spoon" Ummi ce ta yi maganar aranta ta ayyana Samun wuri.

Batool sai faman hadiyar yawu take yi, ba yunwa take ji ba, Amma yadda taga Chief na ciyar da Unaisah yasa taji dama ya bata itama.

Taj kuwa Ransa fari fat da farin ciki kamar ya zuba ruwa a ?asa ya sha, Burinsa yana daf da cika, abun da ya daWe yana jira abunda yafi burgesa yadda Chief ya nuna kulawa agare ta agaban shi inaga idan sukai aure? Allah kadai yasan gatancin da zata samu a gurin sa, Shi yasan Unaisah ta gama morewa.

Tun tana jin kunyar ya bata abaki har ta dan saji jiki ganin daddynta bai nuna wani abu ba..
duk in ya bata one spoon sai sun haWa ido da juna launin idanunsa da take kallo bakomai yake tariyo mata ba face kyawawan idanuwan Danish kasancewar launin idanunsu daya hatta shape dinsu kamar an zana saboda kyau.

"My Angel" muryarsa ce tay mata gizau a cikin kunnanta...

Lumshe idanunta ta danyi wasu zafafan hawayene suka taru a cikin su sam bata son kowa ya gani.


Nutsuwa ya yi yana kallon fuskarta, tuni Ya dakata da bata abincin ganin halin da ta shiga.

"Unaisah" muryarta na rawa tace"Naam"

"Pls don't shed your tears"!

jinjina mashi kai ta yi.


"Na koshi da abincin, Ina so zan shiga toilet" bata jira amsar shi ba, Ta mike har zata fara tafiya taj yace"har kin kammala cin abincin ne"? danne damuwarta tayi"Eh, Inaso zan shiga toilet"

Da sauri ta nufi dakin su, Tana shiga toilet taja kofa ta datse, tare da jingina kanta jikin bango wani jiri jiri take gani kamar zata kife kasa, sai faman jan numfashi takeyi tare da zare gray eyes dinta.

Har yanzu ta gaza yarda cewa man dinta baya atare da ita, bata taba zaton zata iya rayuwa batare da shi ba.

Duk irin burin da ta ci akan shi in sunyi aure zata kyautata mashi saboda halaccin da yai mata yanzu gaba daya plan dinta Ya lalace.


Saitin Zuciyarta ta dafe da tafin hannunta"My man, na gaza yarda cewa ka mutu, Ina ji araina kana raye, shiyasa har yanzu zuciyata take harbawa, don da ace baka raye babu makawa saina bika nima"


*Mr President*

Around ?arfe shabiyu na dare bai runtsa ba, ya wuni da bakin cikin da owais ya kunsa masa, har ciwon kai saida yai, kayan bacci ne a jikin shi ya zuba hannayensa a cikin aljihunsa wandonsa, Sai sintiri ya ke yi a tsakar katafaren bedroom din Hajiya laura, ya rasa meke masa dadi? Komawa yai window Ya dafe glass din da tafin hannunsa Ya zuba ma sararin samaniya idanunsa da suka kaWa jawur..


"Why Owais? why? girgiza kai ya danyi"Ni nasan bayin kanka bane Owais, akwai wanda ke son Ya shiga tsakanina dakai, amma meyasa zaka zargeni kamar bakasan wanene mahaifinka ba"?

Bai aune ba Yaji tayi hugging dinsa ta baya tare zagayo hannayenta kan flat tommy insa.

"My big boss, pls ka fada min meke damunka? gaba daya yau nakasa gane maka, kwata kwata babu walwala a tare dakai.

"Ina da damuwa amma bazan iya fada maki ba kawai ki tayani da addu'a Allah ya kawo min mafita"


Kwantar da kanta tayi kan shoulder dinsa"in sha Allah zanyi maka addu'a, amma pls muje mu kwanta, dare yayi sosai kana bukatar hutu"

"No kije ki kwanta bana jin bacci yanzu" zagayowa tayi tagan shi tare da jinginar da bayanta jikin window glass din a hankali yake dubanta, Nightgown ce a jikinta shara shara rigar.



Kashe murya tayi"ko dai kazo muje mukwanta ko kuma In kira Sarauta In fada mata abun da ke faruwa tunda ni kaki sanar dani" tana fada ta juya zata nufi cikin dakin donta dauko waya da sauri yakai hannu Ya dam?i waist dinta Ya janyo ta ta dawo Jikin shi.

"Ba sai kin kirata ba, naji zan kwanta" kashe mashi ido daya ta yi"ai da ka bari na kirata, kai kasan me zai biyo baya"

Baisan ya zaiyi da laura ba, sometimes indai yana tare da ita koma mashi take yarinya duk da yana jin dadin hakan sosai.

Lallaba shi tayi harta samu yabita suka kwanta.

______________________________bayan wani lokaci

A kwana A tashi ba wuya wurin Allah, yau Wata daya Cuf dakai farmaki gidan kurkukun Kaddara.

meya faru a yan kwanakin nan a kowani Family?

A bangaren Aneelerh cikin kwanakin da suka gabata, ta kasance cikin tsananin damuwa abun duniya ya ishe ta, ta rasa ya za ta yi, kullum tunanin ta wa yakamata ta tunkara da maganar? Ga shaida tana da ita a hannu sai dai tasan mawuyacin abune a yarda da ita, bayan haka tana jin tsoron ta sanarma wani maganar ta koma masa, akarshe ta jefa rayuwarsu cikin hadari.

tuntana 6oyewa har sai da ta kai ga kowa na gidan Ya fahimci Akwai abunda Ke damunta saboda yawan razanar da takeyi da zarar ankira sunan ta, In tana cin abincin Yatsun hannunta kerma suke kaf kaf, bayan haka takan raba dare bata runtsa ba.

Babu irin magiyar da basu yi mata ba akan ta fadi abunda ke damunta tace itafa ba bakomai lafiyarta qalou, Har abie Yasa aka kirata a falo suka zauna duka mutanan gidan Ya matsa mata akan ta fadi meke damunta a karshe tayi masu karya tace dama a kwanakin nan tana yawon yin mafarkin Uzair da Taj shiyasa ta shiga damuwa, har kuka ta yi masu, duk don su Wauki maganarta Serious, tausayin ne ya kama su, gaba daya suka haWu suna lallashinta hada uncle dan iya shine kan gaba, har ila yau bata ta6a yin kuskuren da zai gane tasan wani abu game da shi ba.

___________________________________
'?


Idan muka koma bangaren Unaisah, sai dai muce Alhamdulillah, jikinta ya fara murmurewa, damuwarta ta ragu saboda gatancin da take samu agurin mutan dake bata kulawa, Aunty Ummi, Batool, Taj uwa uba Chief, cikin kankanin Lokaci Shakuwa mai karfi ta shiga tsakaninsu, baya gajiya da bata lokacin shi, kulawar shi, soyayyar shi.

kullum ne sai sun haWu da juna, mafi yawan lokutta atare su ke yin breakfast da dinner agaban kowa yake bata abinci abaki tun tana jin kunyarsa yanzu har ta saba da wayewar shi ganin Taj bai taba nuna ya damu da hakan ba saima dadi da ya ke ji.


Ha?i?a Chief yayi namijin kokari gurin samun lafiyarta, kullum cikin faranta mata rai ya ke yi, Yanzu atare suke motsa jiki a gym room dinsa, bayan haka atare suke yin Kallo a tv room dinsa, har garden din gidan suke zuwa atare su yawata ba karamin nishadi take samu ba, komai ta ke so shi ya ke yi mata, saboda tsantsar kulawar da yake bata ko tari tayi wanda bai kwanta masa arai ba sai ya kira dr don yazo ya duba ta, saboda baya wasa da lafiyarta.

duk wani abu da daddynta Ya fada masa wanda tafi so tuntana Yarinya sai da Chief yasa aka kawo mata shi agidan.

Saboda kyautatawar da yake yi mata ne yasa ta fara Jin shi sosai a cikin ranta, da tunanin shi take kwana da shi take ta shi, In ta farka daga bacci shine mutun na farko da take kwaWayin ta hada ido da shi.

Har yanzu Danish Yana aranta sai dai ta rage damuwa da rashin shi, ta dauki dangana tama fidda rai da shi, saboda ya taba fada mata bazai iya tafiya yabarsu ba, tabbas da ace yana a raye da tuni ya dawo gare su amma yau har one month shiru babu alamun shi.

Abu daya da bata fashi shine yi mashi addu'a har yau bata fasa tashi tsakar dare tayi nafilfili saboda shi ba =ؔ?

A bangaren yan uwanta dake a part din Taj Har yau basu san meke wakana ba, abu biyu ne ke damun su, Kulle su da akayi a part din taj da kuma rashin dawowar su Unaisah Part din, amma saboda yawan kiransu video call da sukeyi Yasa hankalinsu Ya dan kwanta In suka bukaci suna son yin magana da Danish ita keyi masu wayau ta gyara muryarta ta koma irin tashi da yake ta kware gurin iya kwaikwayon muryar Danish Ba zaka taba gane ba shi bane, Ta hake take shawo kan su, ko da sun nuna suna son suyi video call da shi sai tace masu sun manta Danish baya kallon camera? In ta fadi hakan sai suce eh sun tuna fa.

wani sa'in kamar zasu saka mata kuka su dinga mata magiya akan su dai suna so su dawo nan su zauna atare da su, tace su kara hakuri suma suna jirane sai su Danish sun tafi sai su dawo nan.

Alhamdulillah duk da suna a kulle part din Taj suna samun kulawa chief bai barsu hakanan ba, ya sanya masu duk wani abu na more rayuwa da zai shagalar da su ya kawar masu da damuwarsu, Basu da matsalar komai, Hutu kawai suke sha, rana ta farko da Unaisah tayi video call da su saida ta yi mamakin ganin yadda Kumatun parveen suka cuccuko, sunyi kiba sunyi haske kamar ya'yan turawa, Duk in zasu yi waya sai sajeed Ya tuna mata akan ta fada ma Danish Yar uwarsa dake a prison dan Allah kada su manta da ita su taimaka su Wauko ma shi ita...=ؔ?
__________________________________

'?

Idan Muka Koma Obie Estate tuni sun fara shirye shiryen Bithday din Owais da family meeting kasantuwar saura kwanaki kalilin ya rage, prime minister harya kira baba Obie awaya ya fada masa ranar da zai shugo Nigeria yakuma ce su fara shirin tarbarsa.

saboda gabatowar ranar Baba Obie Yasa aka fara gyara Estate Din tare da ?awatasa yadda kasan Masarauta saboda kayan alatun da aka wadatasa da su.


A bangaren Hajjaty tuni tayi watsi da maganar Marwa, kuma tayi blocking contact dinta saboda bata bukatar ta karajin koda muryarta, tun da tayi ma Praveen kazafi taji ta fita aranta.


BENAZIR=ؔ?


A Zaune take kan Mirror chair, Hannunta ru?e Da wayarta, hotunan Unaisah take kallo Idanunta sun cuccuko tab da kwalla, Baiwar Allah Hankalin ba akwance yake ba, ta damu da rashin samun su awaya, In ta kira Unaisah kiran baya shiga, shi kuma, Taj ko ta kira baya picking sometimes rejecting call din yakeyi har sako ta tura ma sa tace dan Allah idan ma bazai kula ta ba, ya hada ta da Unaisah tana son yin magana da ita, shiru bai kirata ba kuma bai mayar mata da reply ba, ta rasa ina zata tsoma ranta taji dadi! Gashi since last da sukai waya da Unaisah Bata kara bacci Cikin kwanciyar hankali ba, saboda munanan mafarke mafarken da ta ke yi akan ta da kuma tana ji aranta wani abu na faruwa da su, Har tunanin zuwa estate din ta yi sai dai tasan Ba lallai ta samu hanyar shiga ba ko da taje, tunda ba wani gareta ba, Taj da take takama da shi baya kula ta amma tasan indai ta nemi Anila da maganar zata taimaka mata suje tunda dama ita ta hadata da su kuma ta san Taj yana ganin girman Aneela.

Kifa kanta ta yi gaban mirror tana shesshekar Kuka.

"Aunty Benazir" Cikin kunnanta ta tsinkayi muryar Zeenatu, Kasa dagowa tayi saboda bata son yanayinta ya jefa zeenatu a hali na damuwa

Shigowa dakin zeenatu tay, jikinta sanye da jallabiya fara.

Ganin Benazir zaune ta kife kai gaban mirror yasa ta nufe ta.

"Aunty Benazir, lunch is ready, we're waiting for you" ta fada tare da karasawa gaban ta.

Jin shiru bata dago ba yasa zeenatu tayi tunanin ko bacci ta ke yi.

Dafa bayanta tayi"aunty Benazir, Wake up pls, " taji tayi shiru bata tanka mata ba.

tasan in har ba magana ta yi mata ba, ba tafiya za ta yi ba, a yanzu bata son kowa a kusa da ita tafi son kadaici.


"Zeenatu! Pls ki kyale ni, basai kun jira ni ba, Ki tafi kawai ku ci abincinku,"

ras gabanta ya dan fadi jin yadda Benazir take magana cikin shesshekar kuka arude ta furta"Aunty Benazir! Meke damunki? Baki da lafiya"?

Bata san sa'adda ta daka mata tsawa ba"bansani ba, Zeenatu! Nace ki kyaleni, Ki rabu dani, bana son ganin kowa akusa dani..."

zazzare blue eyes dinta tayi, abunka ga shagwababba ta fashe da kuka ta juya ta fuce da gudu ta nufi dining area.


A lokacin Mami da Hajiya sarah tare da Dr shureim da Alhaji Ubaida suna azaune kan dining Chairs har sun fara cin abincin, Kukan zeenatu ne yaja hankulansu ga dubanta, azabure suke mike suna kallonta, Ta na karasawa ta fada jikin mommynta tana ci gaba da kuka, Hankali atashe suka dubi juna kafin suka maida idanunsu akanta.


" Zeenatu meya faru? Ina Benazir din? Wa ya tabaki"? Alhaji ubaid ne ya tambaya.

Mami tace"ki bude baki kiyi magana mana! Wani abunne Ya hadaki da Benazir dinne"?

Dago da ita Hajiya sarah tayi"Daughter, Daina kuka, Fada min meya faru"! Cikin kula tayi maganar tana share mata hawayen fuskarta
Cikin shesshekar kuka tace"Ah.. an.. aunty Benazir ce take kuka, Nace tazo muci abinci shine ta daka min tsawa tace in tafi bata son ganin kowa a tare da ita"


Dr shureim bai tsaya ya karasa sauraron maganar Zeenatu ba, Ya zame jiki Ya nufi dakin Benazir tunkafin Ya karasa shiga Ciki yajiyo sautin kukanta, gabansa na faduwa ya afka ciki Ta cikin madubi Ya hango fuskarsa sharkaf da hawaye ta zabga uban tagumi kamar wadda ta rasa gata a duniya, da sauri ya nufe arude ya furta Benazir! Lafiya kike kuka? Meke damunkin ki ne?


mikewa tayi ta nufe shi ta kwantar da kanta saman kafadar shi tana kuka, bubbuga bayanta ya somayi da hannunsa cikin sigar lallashi yace"pls ki fadamin damuwarki, Zan taimaka maki mu nemi mafita, amma kukan nan bazai amfane ki da komai ba, saima yajaza maki ciwon kai"

dakyar ta hadiye kukan tace"yaya shureim ina ma mutuwa zata zama hutu agareni wlh dana mutu na huta, nagaji nagaji da azabtarwar da zuciya keyi min akan rashin mijina da


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login