Showing 69001 words to 72000 words out of 391264 words

Chapter 24 - Cigaban Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel

11 Feb 2025

2608

Allah shine Ya hadani dakai ta silar yarka, Ina jinta tamkar kanwata, muhsin Ya sanar dani komai dangane da abun da ya faru dakai wanda yai silar bacewarku, in sha Allah mutanan da suka yi maku wannan aika aikar sai sunyi danasanin kasantuwarsu a doron duniyarnan......."



kwantar masa da hankali chief ya cigaba da yi har saida yaga ya fara samun nutsuwa tukunna yace mashi zai jira ya yanke shawara...." ai tunkafin ya karasa maganar taj yace mashi ya amince, zai basu hadin kai, babu wata shawara da zaiyi, saboda shi bashi da mafita kwara su tallafa masa ya nemo yarsa.....



Sunji dadin yadda taj ya amince masu batare da 6ata lokaci ba chief, Yace mashi su fara shiri zasu tafi abuja tare da shi, saboda Yana so ya sama masa muhallin da zai zauna akusa dashi sannan yace zai sama masa gurbi a hukumar su ta Isod bayan ya kar6i training dinsu, bayan tafiyarsu tajudeen abuja, rayuwarshi ta sauya, chief owais ya gatanta shi, a cikin gidansa ya ware masa part Waya, inda zai zauna tare da danejo bayan haka ya bashi kyautar mota, cin su da suturarsu gaba Waya shine yake daukar nauyin su, Kafin taj Ya fara kar6ar training din Isod sai da yafara auran danejo saboda yana son su ?ara kusanci da juna, bayason tayi kewar rashin wani nata.



Big guy shi ne mutumin da ya shiga gidan Uzair, aranar da Aneelerh taje gidan har ya Wauke mata baby junaid, bayan haka sune jami'an sirrin da suka kaita gidansu har su ka yi mata tambayoyi da suka shafi 6acewar su Angel.



Sauke numfashi yayi bayan ya gama basu labarin cikin sanyin murya yace



_"Kunji yadda akai na tsira daga hannun mutanan da suka so rabani da rayuwana, hakika cheif yayi min halaccin da bazan ta6a mantawa ba, ya kyautata min, ya faranta min a lokacin da gwiwata ta sage na fidda rai da rayuwar duniyar nan, badan Allah ya ?addarar haduwata dashi ba, da yanzu bansan awani hali zan tsinci kaina ba"_







*Daga Al?alamin Boss Bature=؋?
'
'?*





*Littafin kurkukun ?addara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura*Buy bestselling books online



3196407426



First bank



Bature Hafsat Muhammad,



*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida ta wannan layin 08169856268*

Sponsored Post
Tags
Kurkukun Kaddara
YOU MIGHT LIKE
POST A COMMENT
Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.


Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
Facebook
twitter
YouTube
Instagram
Whatsapp
SUBSCRIBE US

OPINION
FACEBOOK
COMMENTS
CATEGORIES
Africa
(1)
Al'adu
(1)
Alkamawa
(3)
Article
(3)
Blogger Tips
(1)
Economy
(5)
Education
(2)
Entertainment Gist
(1)
Gyaran-Jiki
(5)
Health
(13)
Jikar Iya
(11)
Kimiya
(1)
Kiwon Lafiya
(54)
Kukan Zuci
(5)
Kwalliya
(4)
Labaru
(23)
Lifestyle
(1)
Ma'aurata
(1)
News
(300)
Nigeria
(5)
Noma
(1)
Opinion
(3)
Picture
(3)
Politics
(15)
Profile
(2)
Q&A
(1)
Ramadan
(9)
Ramadan Tafsair
(1)
Siyasa
(1)
Sports
(72)
Tarihi
(5)
Technology
(1)
Tips
(3)
Video
(3)
YouTube
(5)
Zain Abeed
(1)
Zamantakewa
(1)
Novels Elite
Get the Most Exciting News and Read Your Favorite Hausa Novels. Let us be your source for exciting news reports worldwide, as well as access to a wide variety of blogs and blogging tools. We also offer novels in different languages including Hausa so you can easily read what interests you! Plus with our Google Adsense partner program, monetize when readers engage with your content.

Novels Elite
SUBSCRIBE
Posts
Comments
Links
Post a Job

LATEST POSTS

ADVERT
Novels Elite
Copyright ? 2024 Novels Elite | All Rights Reserved
DMCA.com Protection Status
Disclaimer |
Privacy Policy |
Terms and Conditions[14/10, 6:05 PM]  Amin@ M Yusuf Yol@: Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Page 17 Complete
by
Novels Elite Admin
June 09, 2024
Sponsored Link

Novels Elite English
_ *~
'=؋?BOSSLADIESWRITERS=؋?
'~*_







3,F 'DB/=؋?=?%?=؞?





~Takun ?arshe=?%?~







Dedicated to Aunty Kubra=؋?=؞?







B5) -( 1HE'F3J) :J1 9'/J) (JF 'D3,F'! E9 *7H1'* E9B/)=؋?=ؘ?=??Best gifts for your loved ones





An extraordinary romantic love story between prisoners with complex twists d'=؋?=ؘ?







Daga al?alamin Boss Bature=؋?
'











__________________________
'?









Shesshe?ar kukan su ta cika Wakin, babu mai lallashin wani a cikin su, tsananin tausayin taj ne ya kamasu jin irin kalubalen da ya fuskanta, A hankali unaisah ta Waura tafukan hannayenta dake kerma kan fuskarshi ta share mashi hawayen shi, cikin sanyin murya tace"daddy, ka yi ha?uri, ka daina zubar da hawayenka, bana son ganin su, kallonta yai da rinannun idanunsa muryarsa na Wan rawa yace"My Angel, ni nawa ?aluban dana fuskanta bakomai bane akan naku! Ku ne kuka ga rayuwa, ku yakamata a jajanta mawa, a kuma tausayama rayuwarku....." gaba Waya hankulansu Sajeed na akanshi, da ruWani unaisah tace"daddy, kasan abun da ya faru dani bayan na gudu daga rugar su danejo"?

Lumshe idanunsa yai hawaye na sintiri ya Wan jinjina kanshi kafin ya motsa la66ansa"na san abun da ya faru dangane da rayuwar kullan da ku ka yi a GIDAN KURKUKUN ?ADDARA, da kuma irin ba?ar izayar da suke yi maku, ranar da mu ka fara ji daga ni har chief duk irin juriyarmu sai da muka zubar da hawayen mu saboda abun ya Waga hankulanmu, ya razanar da mu, bazan iya misalta maku halin da muka shiga a lokacin da muka ji labarin abun da ake aikatawa a GIDAN KURKUKUN ?ADDARA.



Kallon kallo Su Naufal suka soma jifar junansu da shi idanuwan kowannansu sunyi jawur da su, saboda kukan da suka sha, bakomaine yasa su kallon juna ba face mamakin yadda akai daddyn Angel Yasan abun da ake aikatawa agidan kurkukun ?addara, Unaisah ce kadai batai mamaki ba saboda tasan dama sun sani watakil abakin salsabeel suka ji komai.



Murya na rawa Batool Tace"daddy dama kunsani? Meyasa baku kawo mana dauki ba? Kunsan kuwa irin ?untatar rayuwar kullan da mukayi a gidan kurkukun ?addara? Ta fada hawaye masu Wumi suna sintiri akan kuncin ta, muryarsa a raunace ya furta"mu kan mu ba mu jima da sani ba, da ace tuntuni mun san da zaman ku da har rayukanmu zamu iya sadaukarwa don mu ceto rayuwarku"



Ummin dake kallon batool jikin ta har tsuma yakeyi saboda tsabar ?agara da son jin tarihin rayuwarsu babban burinta taji menene ma'anar gidan kurkukun ?addara da taji sunata ambato a bakunansu.



Jan numfashi batool tayi kafin ta Waura da cewa"mun rayu tun kafin mu mallaki hankulanmu, bamu ta6a ganin hasken rana ba, babu shige babu fuce, a Waki Waya muke a kulle, kullum cikin uniform Waya, abinci sau Waya arana, bamusan dadin rayuwar duniyar nan ba, duk wani hakkinmu na rayuwa an tauye mana shi, mu bamu san dadin iyaye ba, sannan babu mai jin kukanmu, balle a kawo mana dauki, anjuye mana tunaninmu balle musan cewa muma mutane ne masu ?an ci kamar kowa.... ..." bata ?arasa maganarba saboda kukan daya tokare makoshinta, tamkar zatayi kakarin amai.




Cikin karyayyar murya Unaisah tace"tsohuwa tamira ta ta6a fada min cewa na jininmu ne kadai zai Iya sadaukar damu, har yau nagaza yarda da maganar na???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?n, Ina kokwanton tayaya za'ay iyayen da su ka yi silar zuwanka duniya ko wani naka ya sadaukar dakai inda za'a azabtar da rayuwarka? Daddy wanene ya sadaukar daniS'



A matu?ar ruWe ta jefa mashi tambayar tana kallon shi.



Cikin sanyin murya yace"unaisah ni kaina a rude nake, bansan wa zan zarga ba Allah shine yasan wanene mugun da yayi maki wannan aika aikar"

Muryar ummi araunace tace"dan Allah ku fahintar dani, tun Wazu inata magana kunki bani amsa! Inaso naji meya faru da ku? Sannan Ina ne GIDAN KURKUKUN ?ADDARA"!?



Da?yar Unaisah ta lallashi zuciyarta dake yi mata radadi, kafin ta Waura idanunta akan fuskar ummi"zan fada maki komai da kikeson ji aunty ummi" A hankali ummi ke kallon fuskar unaisah



Lokacin da tafara bata labarin rayuwarsu wata irin zuface ta soma wanke fuskar ummi, jikinta ya hau yin kakarwa saboda razanar da tayi, ko a mafarki bata ta6a jin labari mai matu?ar firgitarwa irin wannan ba tuni hawaye sun soma yar tseral kan kuncinta.



Abunda yafi tsaya mata arai cikin labarin da Unaisah ta bata shine mutuwar Unaizah yar gidan daddy, ba ita ba harta taj Jikin shi Ya gama mutuwa saboda bakomai suka sani ba dangane da rayuwarsu saida unaisah tafara basu labari, chief dake atsaye bakin door yana sauraron su kasa jurewa yayi, wani irin jiri jiri Yake gani acikin idanunsa, zuciyarsa har wani tafarfasa take yi tamkar zata kone kanta tsabar 6acin rai da fusata, jijiyoyin wuyansa tuni sun fito rudu rudu kan goshinsa, juyawa yai da sauri Yabar kofar dakin, A hanzarce big guy yabi bayansa gudun kada zuciya ta debe shi Ya je yai ma kanshi Illa.



Zuciyar ummi dake hauhawa tana harbawa da wani irin mahaukacin bugu na tashin hankali tama rasa ina zata jefa kanta taji dadi gaba Waya taji ta tsani rayuwar duniya, Hakika Labarin su Unaiza Ya karya mata zuciya, ya ?ara mata karfin imani sai yanzu ta gane babban kuskuran da tayi nagaza daukar ?addarar rayuwarta, cikin shesshekar kuka mai haWe da gunjin kuka ta furta



"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!! Wannan wata irin musibace? Ku fadamin Tayaya akai har kuka Iya jure wannan ukubar da ?ananun shekarun ku batare da zuciyoyinku sun buga ba? La66anta na kerma ta fada tana dubansu kafin taci gaba da cewa "Zuciyata tagaza yarda da abun da kunnuwana suke jiye min! hankalina Ya tashi! Zuciyata ta karaya! Wannan wani irin zaluncine? Su wanene wadannan Fasikan mutanan mugaye azzulamai marasa imani da tausayi, wadanda basu Wauki ran dan adam abakin komai ba, wai su wanene su dan uban su? Wasu irin dabbobine su jahilai, Masu matattar zuciya, Anya kuwa suna da zuciya a kirjinsu? Anya kuwa mutanene su kamar kowa? Ina kokwanto akansu..." gaba daya ummi ta burkice masu sambatu kawai takeyi kamar sabon kamu ahauka, da alama abun ya razana kwakwalwarta.



Rashin imanin da akai ma yaran ya Waga hankalin ta, fashewa ta kuma yi da kuka kafin taci gaba da fadin"sun manta cewa zasu mutu su koma ga Allah? Wai su basa tunanin makomar su ne? Duniya kaWai suka sa agaba, ko Sun manta cewa duk wani abu da suka mallaka aduniyar nan zasu barshi? Daga su sai halin su za'a binne su!?...."



Waya bayan Waya take kallon su jemimah dake ta kuka aranta ta ayyana yanzu gaba dayansu nan an lalata rayuwarsu har da yan ?ananan cikin su wani irin yunkurin amai ne yazo mata da gudun gaske ta mike ta fuce daga dakin, Har batool ta yunkura zata bita taj yai saurin ru?e hannunta,

"ku barta tayi kuka ta hakanne zata samu saukin abunda take ji aranta" jiki asanyaye batool ta zauna.

Shi kanshi bazai Iya misalta irin kunar da zuciyarshi take yi mashi ba

Cikin muryar lallashi Yace da su"Idan na ce kuyi hakuri kamar na cuce ku ne, saidai ba yadda zakuyi hakurin nan dai shine yakamace ku, Allah Baya barin hakkin wani akan wani, wadanda suka azabtar da rayuwarku In sha Allah za su ga mummunar sakayyar da Allah zai masu tun agidan duniya zasu fara WanWana kudarsu kafin su koma ga mahaliccinsu su fuskanci makomarsu......." da?yar Ya samu ya shawo kansu, kafin ya bi su daya bayan daya yayi huggin dinsu duk don ya kwantar masu da hankalin su, sai da ya tabbatar ya share masu hawayensu tukunna yace



"Dan Allah kada ku sanya damuwa aranku, ku kwantar da hankulanku in sha Allah komai yakusa zuwa karshe, yanzu ku koma dakunanku ku yi wanka ku kwanta ku huta, nasan baza a rasa masu fama da ciwon kai a cikin ku ba, zanyi magana akawo maku breakfast har bedroom dinku"



muryoyin su adisashe suka amsa mashi da toh,



kafin suka mike kamar wadanda aka zarewa laka haka suka nufi kofar dakin suka fuce.



Bayan fitarsu Ya rage daga Unaisah sai batool sai kuma Taj,

Mikewa batool tayi jikinta tamkar na wadda tayi zazza6i ganin ta nufi kofar dakinne Yasa taj yi mata magana"Ina zaki je ne"?



"?akin Aunty Ummi" amsa mata yai da okey, bayan ta fuce ya maida dubanshi ga unaisah, janyota yai tare da kwantar mata da kanta kan kirjinsa hannunsa akan kafadarta

"Ina fata yanzu babu abunda ke maki ciwo"? muryarta kasa kasa tace"eh daddy,"

Da yar zolaya yace mata"ya rashin ji ko da yake naga kin daina Yanzu"? ?ara shige mashi tayi tana yar dariya, bubbuga bayanta yai da hannunshi, kafin ya janyeta, ya mike kan gwiwowinsa ya fuskanci alkibla yakai goshinsa kasa yai sujjada murmushi tasaki tana kallon shi, da sauri itama tayi sujjadar kamar yadda yayi, tsawon mintuna kafin suka dago da kansu fuskar kowan nan su dauke da annurin farin ciki

"Daddy fada min me ka ce acikin sujjadarka"

Numfasawa yai kafin yace"nayima Allah godiyane da ya bayyanar min da ke da ranki da lafiyarki"



"Nima haka" murmushi suka kuma saki gaba dayansu,



"Daddy Inaso na tambayeka, tayaya akai ku ka hadu da su salsabeel? Ko ya fada maku yadda akai suma suka ku6uta daga kurkukun ?addara"?

Shiru ya Wanyi kafin yace"ki bari idan yazo sai ki ji daga bakin shi, yanzu nafiso ki kara samun kwanciyar hankali" amsa mashi tayi da toh



"ki tashi mu shiga toilet ki wanke fuskarki kizo mu ci abinci"



Ya fada tare da ruko hannunta suka shiga toilet, bayan sun wanke fuskokin su suka fito atare

A gefen gado suka zauna Ya bude masu abincin tray din da suka ajiye kan table

Cikin kulawa yake bata abinci abaki tana ci, tsabar dadi kamar ta zuba ruwa a kasa tasha, wai yau gata ga daddynta



"Daddy, Ina aunty Aneelerh da babynta"?

Murmushi Yasaki kafin Yace"suna nan cikin koshin lafiya, kwanakin baya nabibiyi layin wayarta amma ba'a Waga ba sai wata rana dana ci sa'a aka daga wayar kinsan wanene ya daga" girgiza mashi kai tay alamar a'a yana murmushi yace"?aninki baby junaid," waro idanu waje tayi da tsantsar farin ciki tace"daddy sunan shi junaid" daga mata kai yai alamar eh



"baki ga yaron ba kyakkyawa dashi, ga wayau sai ma in yana surutu.." cike da zumudi tace"daddy inason ganin shi tare da aunty aneelerh, dan Allah ka kaini wurin su nayi missing dinta"



"Zan kaiki in sha Allah, amma ba yanzu ba, ki Wan ?ara hakuri" tur6une mashi fuska tayi, bakinta cunkushe da abincin daya tura mata, yar dariya yai tunawa da kuruciyarta.



"Banji kin tambayeni danejo ba"!

Sakin fuskarta tay, "tana araina daddy, bazan ta6a mantawa da halaccinta agareni ba, ni dai ba abun da zance sai dai inyiwa Allah godiya saboda Ya hadani da mutanan kirki masu sona tsakani da Allah' ta fada fukarta da Wan murmushi,



"Yaushe zaka kaini Wurinta in ganta"?



"Ko zuwa anjima idan kika kara jin sauki sai muje ko"? Daga mashi kai tay alamar eh.



Shiru suka dan yi kafin ta kuma cewa"daddy mommy adama fa? da uncle abdallah!! Suna nan suma"?

Daga mata kai yai alamar eh,

"Alhamdulillah Ya Allah" ta furta da matsanancin farin ciki, ashe da rabon in sake ganin yan uwana.



"Ina granny Wina da sauran mutanan buzaye"



Jiki asanyaye ya ajiye cokalin dake a hannun shi, nan take ta fahimci babu lafiya, muryarta adan rude tace"daddy menene"?



Cikin sanyin murya yace"unaisah sun riga mu gidan gaskiya, mahaifina da mahaifiyata, da kuma kakata kusan duk a lokaci Waya suka rasa rayukansu nima sai daga baya naji labari..."



Cikin sanyin murya tace"ubangiji Allah Yajikansu ya gafarta masu, Allah ya jaddada rahama agare su..." amsa mata yayi da ameen

Shiru suka danyi na wani lokaci batare da ya cigaba da bata abincin ba

So take ta tambaye shi dangane da mahaifiyarta sai dai takasa saboda zuciyarta taki bata hadin kai, Har yanzu bata daina jin Wacin radadin abun da tayi mata ba, ta tsani mahaifiyarta fiye da komai na duniyar nan, tana son ta haWu da ita ba don komai ba sai don taji dalilin dayasa ta yi watsi da ita, idan ba ta son ta meyasa ta haife taS'





*HAJJATY =؋?*



A zaune take gaban dressing mirror, fuskarta dauke da murmushi bakomai take tunawa ba face fuskar Naufal, ta kasa mantawa da shi, Yaron ya kwanta mata aranta, daren jiya data kwanta bacci har mafarkinsa tayi,

da alama bata jima da fitowa daga wanka ba, duba da towel din dake daure a chest dinta

Tun dazu takasa tabuka komai gaba daya ta shagala da tunanin naufal, ta ?osa pravin ya shigo donta nuna mashi hoton naufal tasan zaiyi mamakin ganin me kama da ita.



Wayar ta dake ajiye kan mirror din ta dauka ta budo hoton shi tana kallo har zooming din fuskarsa take yi

Jin motsin shigowar mutun yasa tayi saurin juyawa don ganin wanene

Pravin ne ya shigo sanye da farar jallabiya, fuskarshi babu annuri ko miskala zarratin kamar wanda aka fada ma sakon mutuwarsa

Sam bata lura da yanayin shi ba, cike da zumudi ta mike ta nufe shi tana fadin"honey, ina ka shiga tun jiya bansaka a idanuna ba"? Fadawa tayi kan kirkinsa tai huggin nasa kafin ta Wago da fara'arta tace"ka yi shiru baka ce min komai ba"? Wani kallo ya soma jefa mata mai kama da harara, da alama ta manta abunda tayi mashi jiya shiyasa ta za?e tana shige mashi

Ganin baida alamun yi mata maganane yasa tace"fadamin baby, ko dai hajiya saratu ce ta 6ata maka rai"? Banza yai da ita baice uffan ba..

Murmushi tadan saki"nasan itace ta bata maka rai, bari na nuna maka wani abu nasan zakayi farin ciki idan ka ganshi" ta fada da sauri ta nufi mirror

Goya hannayensa yai akan kirjinsa yana jiran karasowarta.



"Baby, duba ka gani, jiya a wurin taro bayan tafiyarka naga wannan yaron mai kama da Wan mu Naufal kyakkyawan gaske" cikin annushuwa ta mika mashi wayar don ya kar6a ya gani, rai amatu?ar 6ace yakai ma wayar bahagon naushi tayi sama ta ?undumo kan tiles ta bada wani sauti mai karfi.



idanunta azazzare ta dago tana kallon shi, Huci yake yi tamkar mayunwacin zaki Ya furta"kin manta abunda ki kai min jiya"? Dafe kai tayi da hannu daya idanunta tuni sun cuko tab da kwalla, ranta abace tace"pravin! Meyasa zaka jefar min da wayata? Laifin me nayi maka? Saboda kawai naki bin umarninka? Wai meke damunka ne pravin? Agaban mutane fa ka ruko hannuna kaja ni zaka fitar dani daga hall tayaya bazan ki binka ba? Ko so kake afara zargin mu ?



Kafin ta ?are maganar Ya daka mata tsawar data firgitar da ita, nuna ta yai da yatsan hannun shi"yi min shiru! Bana son jin komai daga gare ki, ashe harni ban isa in baki umarni ki bi ba! Hankalin ki ya kwanta Kin kunyata ni a idon jama'a..." hawayene suka soma sintiri akan fuskarta, muryarta


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login