Showing 72001 words to 75000 words out of 391264 words

Chapter 25 - Cigaban Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel

11 Feb 2025

2563

na rawa tace"pravin ka fahimce ni mana, kasan bazan ta6a kin bin umarnin ka ba, hakanan batare da kwakkwarar hujja ba! Ni nayi hakanne saboda bana so wani ya tuhume mu..." yatsansa ya daura kan la66anta, shiru tayi tana kallon shi

Can kuma ta fashe da kuka tasa hannu ta ture yatsan nasa tana fadin"baka kyauta min ba, Tun jiya nake zumudin in nuna maka hoton sajeed Yaron dake kama da danmu amma shine ka fasa min waya..."?

Ta6e la66ansa yai kafin ya furta"ki yi hakuri rainane ya 6aci, " ya fada tare da zukunnawa ya dauki wayar yana fadin"zan siya maki wata"



"bana so, ni dai ka gyaramin tawa, saboda bana son na rasa hoton sajeed"

Harara ya watsa mata tareda cewa"meye alakarki da shi ne? Kawai daga ganin yaro yana kama dake? Mutun nawa kika sani suna da masu kama dasu a duniya? Kamar kanki farau"

"Ni wannan bai dameni ba, Ina son shi saboda inajin shi kamar Wana dana rasa"

Rai a6ace ta fada kafin ta juya ta koma kan gado ta zauna, tana cigaba da matsar kwalla

Murmushin gefen fuska pravin yasaki Yana dubanta,

Komawa gefenta yai ya zauna bayan ya ajiye wayar ya ruko hannunta acikin nashi

"Look, bana so ki sanya damuwa aranki, idan har rashin naufal ne ke damunki, nayi maki alkawarin nan bada jimawa ba zaki haifi wani babyn, sai ki sanya mashi sunan naufal din"

Wani kallo ta jefa mashi batare da tace mashi ?ala ba, lallashinta Yacigaba dayi duk don ya samu yashawo kanta.



HAJIYA SARATU





_safa da marwa take yi a tsakar dakinta, zuciyarta cike fal da tunanin abunda Pravin yayi mata jiya a dakin taro, tun jiya abun ke ci mata tuwo akwarya, abun sai nanu?arta yakeyi, zuciyarta ta gama hasala, wai har ita pravin zai kunyata gaban yan uwanta da abokananta? A ina ya samu ?warin gwiwar yi mata haka? ru?e qugu tayi da hannu Waya fuskarta babu annuri_





*Daga Al?alamin Boss Bature=؋?
'
'?*







*Littafin kurkukun ?addara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura*



3196407426



First bank



Bature Hafsat Muhammad,



*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida ta wannan layin 08169856268*




Kurkukun Kaddara
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Page 18 Complete
by
Novels Elite Admin
June 12, 2024
Novels Elite English
_*~
'=؋?BOSSLADIESWRITERS=؋?*~_







3,F 'DB/=؋?=?%?=؞?





~Takun ?arshe=?%?~







Dedicated to Aunty Kubra=؋?=؞?







B5) -( 1HE'F3J) :J1 9'/J) (JF 'D3,F'! E9 *7H1'* E9B/)=؋?=ؘ?=??





An extraordinary romantic love story between prisoners with complex twists d'=؋?=ؘ?







Daga al?alamin Boss Bature=؋?
'











__________________________
'?







=ث?HAJIYA SARATU=ث?









_safa da marwa take yi a tsakar dakinta, zuciyarta cike fal da tunanin abun da Pravin yayi mata jiya a dakin taro, tun jiya abun ke ci mata tuwo akwarya, abun sai nanu?arta yakeyi, zuciyarta ta gama hasala, wai har ita pravin zai kunyata gaban yan uwanta da abokananta? A ina ya samu ?warin gwiwar yi mata haka? ru?e qugu tayi da hannu Waya fuskarta babu annuri_



Maganganun da suka Tattauna jiya ita da su Har excellency ta soma tariyo bayan fitowarsu daga hall kafin su nufi gidan prime minister.





"Meyesa pravin zai ja hannunta abainar jama'a? Menene alakarsu? Wai ku ba ku zargin wani abu atsakanin su"? Hajiya laurace ta fada babu wasa akan fuskarta



"Najima ina zargin matar nan, na dai yi shiru ne ban fada maki ba, saboda bana so in shiga tsakanin ki da mijin ki, amma ni kwata kwata hankalina bai kwanta da ita ba, tun daga kan yanayin yadda take daukar wanka zaki fahince akwai wata a kasa ba banza ba, ni ay ban ta6a ganin yar aikin da ta samun ?anci kamar hajjaty ba"! Her excellency muhibbat ce tai maganar,

Hajiya jamila tace"yanzu wani hukunci zaki yi masu"? ta fada tana kallon hajiya saratu.



Da sauri Hajiya madina tace"please, ku daina tunzurata ku bar ta taji da abun da ke damunta, ni banga abun Waga hankali a maganar nan ba!"



Hajiya saratu da ke sauraronsu Waya bayan Waya sai da ta cika ta batse kafin tace



"Wallahi bazan ?yalesu ba! Daga ita har shi sai sun fuskanci 6acin raina, sai tayi danasanin kasantuwarta yar aiki a gidan nan"! Ta fada a tsiwace tana huci



"Ni shawarar da zan baki kawai ki kore ta daga gidan ta koma can kasarsu acigaba da bautar shanu, idan ba haka ba Allah kaWai yasan muna?isar da take shirya maki, ?wara tun wuri ki yi maganinta kafin ta jaza maki matsala" Acewar hajiya Muhibbat



Dafa kafaWarta hajiya laurat tayi"idan da zaki bi shawarata kada ki tanka masu! Nasan yanzu hankulansu atashe yake saboda sun san dole ki tuhume su, abun da yakamata ki yi shine ki manta da zancen hukunta su, ki yi tamkar babu abun da ya faru, za su yi zaton kin kyale su ne, ki bari sai sun shagala tukunna ke kuma ki fara bincike akan su, ta haka ne kadai zakisan meke atsakanin su amma yanzu idan kikace zaki hukuntasu to ba za ki san menene alakarsu ba, kwara ki fara bin diddiginsu har zuwa lokacin da zakiyi nasarar kama su dumu dumu"




Jinjina kai hajiya saratu tay alamar gamsuwa da shawarar Hajiya laurat..



Bayan ta dawo daga duniyar tunanin taja gauran Numfasawa haWi da Wan jinjina kanta, cikin takun sauri ta nufi wayarta dake ajiye kan pillow ta dauka ta kira landline na kitchen.



Tana fara ringing akayi picking, kara wayar tai a kunnanta.



"Inason ganin Marwa, ta same ni adaki bana son bata lokaci"



ta fada tare da katse kiran ta ajiye wayar



Cigaba da zagaye bedroom din tayi, yayin da take dunkule tafin hannunta na dama tana tura shi ana hagu kamar ?ar dambe.



Knocking kofar da akayi mata ne yasa ta dakata.



"Wanene"?



"Aunty ni ce marwa"



"Okey shigo ciki"



Turo kofar tayi, Jikinta sanye da uniform na ma'aikatan gidan ta shigo, cikin girmamawa ta gaishe da hajiya saratu, bata amsa mata ba, sai tay tamkar ba ta ji me tace ba.



Tuni marwa ta sha jinin jikin ta, tsoranta kada ace wani laifin ta aikata da yasa hajiya saratu ta kira ta don tasan halinta masifaffiya ce.



Muryarta na rawa tace"Am.. Aunty gani, naji kina nemana"



Wurga mata harara hajiya saratu tayi da sauri ta dukar da kanta kasa

Tsawon lokaci bata tanka mata ba, gani ta ke kamar zubda ajine ta nemi taimakon yar aiki, sai dai ba yadda zata yi itace kadai hanya mafi sauki agareta.



Zama tayi gefen gadonta, cike da isa ta dubi marwa"ke zonan"! da sauri marwa ta dawo ta zukunna agabanta.



"Wani aiki nakeso kiyi min, bana so kowa ya sani daga ni sai ke! Na yaba da hankalin ki ne shiyasa na za6e ki saboda nasan zaki Iya......" Tun da tafara magana marwa ta soma zare idanunta cike da fargaba.



"Kafin na faWa maki, zan gindaya maki sharadi, Idan har na kuskura naji maganar nan abakin wani, ko kika bani matsala wallahi thumma tallahi na lahira sai yafi ki jin dadi...." Wani irin yawu marwa ta haWiya jiki na bari tace"in sha Allah zan kiyaye."



Ta6e baki tayi kafin ta Waura da cewa" me kika sani dangane da head maid din gidan nan? ya mu'amalarta daku take? Sannan Wacece aminiyarta acikin ku? Shin tana fada maku sirrinta"?



Shiru marwa tayi aranta ta ayyana to fa! Ko me hajjaty ta aikata ma aunty masifatu da take neman karin bayani dangane da ita? Watakil watan cin ubanta ne ya tsaya



A fili kuma tace "Abun da nasani dangane da ita, macace mai saukin kai, tana da mutunci kuma tana kyautata mana, ba ta shiga sabgarmu, sannan bata cika zama yin fira da mu ba, macece mai kamun kai bata da surutu, sannan bata da aminiya acikin mu balle har wani yasan sirrinta, wannan shine Iya abunda sani"



Tur6une fuska hajiya saratu tayi, ita ba haka taso taji daga bakin Marwa ba.



"Okey, ki nutsu ki saurareni," jinjina mata kai tai

"Daga yau inaso ki fara shisshige mata, saboda ina zarginta, inason kisan duk wani sirrinta, ki zama aminiyarta, bayan haka duk wani motsinta ya kasance a tafin hannunki, idan har kikaga wani abu ba dai dai ba, to kiyi hanzarin sanar dani," amsa mata tayi da toh



"Idan har na samu abun da nakeso nayi maki alkawarin zan baki mukamin da take da shi agidan nan, bayan haka zanyi maki kyauta ta musamman, kin dai san wacece ni, basai nayi maki bayani ba"



Wani irin farin cikine Ya lullu6e marwa musamman da taji Hajiya saratu ta ambaci zata bata mukamin hajjaty ga kuma kyautar da zata samu, aranta ta ?udiri aniyar saita yi ma hajjaty kutse koda kuwa bata kama ta da laifin komai ba, ita zata ?ala mata sharrin da za'a sauke ta daga kan mukaminta.



Shu'umin murmushin gefen fuska tasaki.



"Baki da matsala dani aunty, in sha Allah zaki samu abunda kikeso"



"Zaki iya tafiya" mikewa marwa tayi zuciyarta cike fal da murna, dama ta jima tana jin haushin hajjaty saboda yadda tayi masu zarra agidan, komai itace akan gaba, gata head maid ga farin jini awurin mutanan gida, bayan ba wani aiki takeyi ba acikin gidan sune masu wahalar girka abinci, ita aikin ta tsara abunda za'a girka ne da kuma bada umarnin yadda abu zai kasance.



Dole ta Wana mata tarkon da bazata Iya fidda kanta ba, ko dan ta ?wace mukamin ta, wannan alwashine ta daukarwa kanta!



Ta fada aranta, yayin da take nufar hanyar komawa kitchen



Bayan fitar marwa, hajiya saratu ta sauke ajiyar zuciya, yanzu ne ta samu kwarin gwiwar shiga toilet yin wanka



Lokacin da fito, A zaune ta same shi gefen gadonta, sam bataji alamun shigowarshi ba.



Tun da ya Wago suka hada ido da ita yai saurin sunnar da kanshi kasa, wani irin nauyinta yaji, baisan ta ina zai fara shawo kanta ba, Yasan dole ta tuhume shi akan abun da Ya faru jiya.



Kau da ido tai daga kan shi, Ta juya ta nufi closet, jim kaWan Ta fito har ta sanya riga bubu ta atamfa, gaban mirror ta tsaya tare dakai hannu ta dauki turare ta soma feshe jikin ta da shi, yadda ta share shi kamar batasan da zaman shi a dakin ba.



Shi kuwa gogan Ya kasa dauke idanunsa daga gareta.



Kamshin turarenta ne yakai mashi karo har ya gaza jurewa duk da shakkarta da ya ke ji ?arfin hali yai wurin furta"Har Yanzu fushi kike dani? Banza tayi da shi

Mikewa yai tsaye ya nufeta, daga bayanta ya dan dakata Yana bin ta da kallo.



Kafin cikin sanyin murya yace "Tun jiya nake ta so na baki hakuri, nasan ban kyauta maki ba, ni kaina ba'a hayyacina na aikata hakan ba, bansan meyasa na ruko hannunta ba, wallahi sharrin shaiWanne"



Murmushin gefen fuska tasaki, ba tare da ta bari ya gani ba, dama dagangan ta dauki wankar da zai zautar da shi



"Na cancanci kowani irin hukunci daga gareki, a shirye nake dana kar6e shi, ni dai bana son 6acin ranki"



ya faWa tare da Waura kansa saman kafadarta saboda karfin hali irin nashi

Lumshe idanunsa yai tare da shakar kamshin turarenta.



"Kinyi shiru baki ce min komai ba" sai da ta mula tasha iska tukunna Tace"laifin me kayi min"?



"Kin riga da kin sani"



"In dai dangane da abunda ya faru jiya ne to ka manta kawai, bana son tada maganar, ko alokacin abunda yasa raina ya 6aci saboda ina kishin ka ne banji dadi ba, amma yanzu komai ya wuce"



Tsabar mamakin kalamanta yasa shi saurin Wagowa yana duban fuskarta ta cikin mirror.



"Amma dai wasa kike min ko"? Murmushi ta sakar mashi tare da cewa"na taba maka wasa irin wannan"?

Girgiza kanshi yai"a'a, baki taba min ba, amma dai nayi mamaki, Allah yasa ba mafarki nake ba" juyowa tayi suka fuskanci juna, fuskar ta dauke da ?ayataccen murmushi ta Waura hannayen ta a kan kafadunsa.



Lamarin ya Waure masa kai gaba daya ta canza mashi kamar ba hajiya saratun daya sani ba.



Cikin sanyin murya tace"hubby, kada ka ?ara maimaita kuskuran da kayi, bana so, kasan inada kishi, akan ka zan iya komai daga ciki har da kisa"



Zaro idanunsa yayi"in sha Allah hakan bazata faru ba, zanyi kokarin ganin na kiyaye duk wani abu da zai bata maki rai"



Ba zato ba tsammani yaji tayi huggin Winsa tare da zagayo da hannayenta kan waist dinsa, tuni yafara jin shi awani yanayi.



Sumbatar wuyansa tayi kafin ta dago da bakinta saitin kunnanshi cikin muryar raWa mai hade da kwarkwasa tace"fadamin me ka ke so nayi maka wanda zai faranta ranka"



"Nagaza yarda da abinda kike fada min, anya kuwa kece? Ko dai aljanune suka shige ki? Nifa ina kokwanto bana so saina shagala ki canza min ainihin kala dinki"



dariya tayi cike da nishadi tace"ka daina kokwanto akaina, ni ce dai hajiya saratun daka sani, matarka uwar ya'yanka"



Murmushi pravin yai cike da jin shaukinta



"Ka yi breakfast ko insa a kawo mana mu yi a daki nima banci komai ba"



"In ban da abunki ay kinsan bana iya cin abinci idan ba atare dake ba, don ma ke dince wani lokaci baki jira na"



"I'm sorry Yanzu bari na kira akawo mana a daki, me kake son ci"?



Yana faman washe baki yace "Duk abin da zaki ci, zabinki ay shine nawa"



Shu'umin murmushin gefen fuska hajiya saratu tasaki tare dakai hannu ta dauki waya ta kira layin kitchen ta isar da sakon akawo masu abinci, bayan abla ta kawo masu atare suka zauna suna ci, kamar sabbin ma'aurata abaki ta fara bashi har sai da suka cinye kafin ta soma jan hankalin shi.



Gaba Waya nema take ta zautar dashi da salonta, kasa jurewa yayi da sauri ya ?ara tighting nata a jikinsa.



_________________________________d'
'?





Bayan shigar chief bedroom dinsa a zafafe Ya faWa Bathroom dinsa don ya watsa ruwa ko ya samu zuciyarsa ta lafa daga radadin da ta ke yi masa.



ganin ya shiga toilet yasa big guy sauke ajiyar zuciya, yayi tunanin zaiyi yadda ya saba ne idan ransa ya 6aci da wuya in bai yi ma kan shi illa ba, wani lokacin mirror yake kaima naushi ya tarwatsa shi har sai hannun shi ya faffashe saboda tsabar zuciyar dake gare shi.



Kafin fitowarshi da sauri big guy ya fita na tsawon mintuna ya dawo hannun shi ru?e da wooden tray mai dauke da breakfast din chief.



Yayi mamakin ganin shi kwance kan gado, jikin shi sanye da bathrobe ya Waura hannunsa Waya kan lallausar sumar kanshi, ya lumshe wadannan kyawawan idanuwan nashi, bakomai yake tunawa ba acikin zuciyarsa face tarihin rayuwar prisoners, labarin yai matu?ar ta6a zuciyar shi.



"Allah Ya huci zuciyarka Yalla6ai, ga breakfast dinka, nasan kana jin yunwa" cikin girmamawa yayi maganar



Tamkar bazai tanka mashi ba, sai da ya dauki lokaci kafin Ya furta"ka koma da abincin bana jin zan iya ci"



Cikin sanyin murya big guy yace"ka yi hakuri Sir, kasan ni mai biyayya ne agare ka, bana yi maka jayayya amma yau bazan iya bin umarnin ka ba, saboda na damu dakai, abun da ke damunka nima shike damuna..." ya fada yana cigaba da kallonsa.



"Sir, ?in cin abinci bashi bane mafita, kana bu?atar kwanciyar hankali da nutsuwa, wanda hakan bazai samu ba sai ka jajirce wurin ganin ka kauda damuwarka, sannan yanzu ne ya kamata mu dage damtse mu yi aiki tu?uru don ganin mun gano su wanene azzaluman mutanan da suke aikata 6arna a kasarmu"



DaWaWan kalamai Big guy ya cigaba da zayyano masa yana kara karfafa masa gwiwa da kwantar masa da hankali, A hankali Ya fara jin saukin radadin da zuciyarsa ke yi mashi.



"Sir, har yanzu kana akan bakanka na bazaka ci abincin ba"? Ya faWa yana duban cute face din Ogan nasa



Slowly ya Wan motsa tausasan pink lips dinsa in a low voice ya furta"zan kokarta" gyaWa kai yai

"Zan tafi yalla6ai, Ka huta lafiya" ya fada tare da sara mashi kafin Ya juya har ya kusa ficewa daga dakin muryar chief ta ratsa kunnansa"nagoda da kulawarka agare ni"

Murmushi big guy yai"kada ka damu yalla6ai"

Har zai fuce ya kuma dakatar da shi"please ka duba dakin Yaron nan, kaga Awani hali Yake a ciki, Idan ya farka a tabbatar Yayi breakfast dinsa, idan ya gama ka tambaye shi me yake bukata in ya fada maka ay gaggawar yi mashi, zuwa anjima sheikh Imam zai zo duba shi"



"Okey, Sir"



Ya fada tare da bude door room din Ya fito waje, dakatawa yayi da tafiya yana tunanin tawace hanya zai faranta ran chief? Don ya fahimci har yanzu akwai sauran damuwa aranshi, tunawa da Unaisah yasa shi saurin zaro wayarsa ya danna ma boss kira, tana fara ringing yai picking Call din

Da zolaya yace"masu ?a, halan Har yanzu kana nan ma?ale da ita"



Sautin muryar boss da alamun dariya yace"To Wan sa ido, ka fara tsokanar taka ko"?



Dariya Big guy yayi" inatayaka murna abokina"



"Nagode sosai mutumina, Ina chief ne ina fata yana lafiya"



"Ba lafiya, Har yanzu akwai damuwa aranshi, Kuma kasan halinshi mutunne mai zuciya, yanzu haka ina a kofar dakinsa, na kai masa abinci yace min bazai iya ci ba"



Muryar bos da jimami yace"amma banji dadi ba, pls ka yi kokarin kwantar masa da hankali kafin inzo"



da sauri big guy yace"anya zan iya? Ko dai zaka turo unaisah ko da godiyane tayi mashi, watakil hakan Ya kwantar masa da hankalinsa"



"Nima nayi tunanin hakan, yanzu zan turo ta in sha Allah" murmushi big guy yai kafin yai mashi sallama a hanzarce Ya nufi bedroom diny Danish.





*d'GARKUWA=ت?*





A kishingiWe Yake kan gadon shi, Ya hakimce kamar wani basarake, wasu hadaddun sleeping dress ne a jikin sa launin red colour sunyi bala'en yi mashi kyau, hannunsa Waya rungume da pillow, lallausar sumar kanshi ta lullu6e gefen fuskarshi, yayin da kyawawan fararen idanunsa ke akan hadadden ceilling din dakin, tun da Ya farka daga bacci bai ta6uka komai ba, gaba Waya ya shagala da tunanin Hateem, wani irin kewarsa yake ji, mutumin ya kwanta masa aransa saboda yadda ya tarairayesa ya bashi kulawa kamar wani nashi, bai ta6a tsammanin zaiji tsantsar kaunarsa ba, sai gashi zuciyarsa takasa samun sukuni saboda tunaninsa, da zarar ya lumshe idanunsa fuskar Hateem yake gani dauke da murmushi......"



Yana son ya sake sanya shi a idanunsa, kwata kwata bai fahimci cewa prime minister kasar ya bari ba.



Har Yanzu kamshin turaren daddy hateem bai bar


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login