Showing 15001 words to 18000 words out of 391264 words

Chapter 6 - Cigaban Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel

11 Feb 2025

3510

idanuwanta sun kaWa jawur, daga gani kukan take cikin yi

In a calm voice Ya furta"ina fata ban katse maki baccin ki ba"

Muryarta adisashe tace"ban kaiga Yin baccin ba,"

Jinjina kai yayi"Uncle ne yace in kira ki, su na a falo shi da su mamie da abie"

Shiru tayi jimmm kamar bazata motsa ba, har saida ya maimaita mata maganar tukunna tace Toh, ka jirani mu tafi atare"

"Okey"

Maida ?ofa tayi ta rufe ta, badajimawa ba sai gata ta fito sanye da doguwar riga, ta yafa mayafi akanta,

Jin ta ru?o hannun shi acikin nata ne yasa shi saurin kallonta, sam hankalinta ba akwance Yake ba, bai yi yun?urin raba hannun shi daga nata ba, A haka suka nufi falon, sai da suka kusa isa yayi saurin zame hannun shi daga nata, Takun tafiyarsu ne Yaja hankalinsu mami ga dubansu

Cikin girmamawa Ana ta gaishe da su, tare da samun wuri gefen Aneelerh ta zauna tana faman jan numfashi, bayan mahboob Ya zauna.



Abie dake kallon Ana Ya soma Magana a tsanake



"Inaso ki natsu ki saurare ni," jinjina mashi kai tai alamar toh

"Ki Wauka tamkar mahaifanki ne suke yi maki magana, kada ki ji shakkun faWa mana abun da ke damunki, saboda mu kaWai ne makusantanki a yanzu, Ha??inmu ne mu kula da rayuwarki, Idan wani abu ya same ki ba zamu ji daWi ba" wani irin sanyine ya ratsa zuciyarta, ha?i?a kalaman abie sun yi tasiri a zuciyarta.

Uncle Wan Iya ya Waura da cewa"banji daWin abun da Ummi ta fada min ba, baki kyauta mana ba, ashe baki Wauke mu yarda muka Wauke ki ba, meyasa zaki zauna abu na damunki ki gaza gaya ma kowa? Meye amfanin 6oye mana eye"? Muryarshi da faWa yake yi mata magana, alamar ranshi ya 6aci.



Sunnar dakai ?asa Ana tayi yayin da idanunta ke akan Yatsun hannayenta

"Meke damun ki ne, inaso ki faWi mini gaskiya"? Ya jefa mata tambayar, Su Aneelerh da su mami sun natsu suna kallon ta.

Numfashi taja tare da sauke shi A hankali ta furta"Idan na 6ata maku rai, dan Allah ku yafe ni, Aunty Aneelerh, mami, ummi, Zahra, Mahboob, abie, uncle, Allah ne kaWai zai Iya biyanku, duk da kasancewata yar aiki agidan nan, Sannan ba musulma ba amma kun daukeni tamkar jinin ku, ko dan saboda nuna damuwar da ku ka yi akaina zan fada maku gaskiyar abun da ke damuna...." ta faWa tana mai ?an?an da kanta, gaba Waya duk sun ?agara da suji meke damunta, musamman Mahboob Ya kasa Wauke idanunsa daga kan fuskarta, wani irin tsantsar sonta da ?aunarta yake ji, ga matsanancin tausayinta dake addabar zuciyarsa.

"Cikin kwanakin nan, Ina yawan yin mugayen mafarkai, waWanda suke neman haukata ni, bansan meyasa hakan yake faruwa dani ba, idanuwana suna gane min abunda yafi ?arfin gani na wanda silar hakan yasa nafara zaucewa, ni gani nake ma kamar mutuwa zanyi..... " muryarta na rawa ta ?are maganar nan take ta fashe da kuka mai sautin gaske, Hankalin su ba ?aramin tashi yayi ba, Jikin kowannansu yayi sanyi

"Kiyi shiru, Kukan Ya isa haka, Ki faWa mana me kike gani a cikin mafarkin naki"! Uncle Wan Iya ne yai maganar

Cikin shesshe?ar kuka tace"wallahi duk yadda zanyi maku bayani ba lallai ku fahimce ni ba, ni kaWai nasan halin da nake aciki, ni kaWai nasan bala'en da nake gani, Ba tun yanzu ba, tun ina ?aramata idan nayi mafarki mummuna yana zama dagaske, hatta rasuwar iyayenmu saida nafara yin mafarkin zasu yi hatsarin mota, sai gashi ya tabbata, uncle Wina ma ni nayi mafarkin mutuwarsa kuma ya tabbata, da wuya inyi mafarki mummuna bai zamto gaske ba, ni damuwata mutanan da nake a tare da su bana son wani abu ya sami wani daga cikin ku...." tashin hankalin da ba'a saka mashi date, A matu?ar ruWe Zahra take kallon Aneeleerh, Ummi ta kalli Mamie, Idanuwansu azare, mahboob kuwa kusan suman zaune yayi.



Shiru tayi Tana faman yin shesshe?ar kuka,

Abie dake kallonta, nazarin maganarta yakeyi, yaso ace musulmace ita, kodan ya bata shawarar ta run?a yawaita yin azhkar, da sauran addu'o'in neman tsari.

Tsawon lokaci falon yayi tsit, babu mai magana acikinsu, sai kallon kallo da suke jefawa junansu.

Muryar Uncle Wan Iya ce ta katse Shirun nasu

"Ki daina sanya damuwa aranki, Mafarki ba gaskiya bane, shaidan ne yake assasashi, Ki yawaita yin addu'a, muma kuma zamu tayaki, Allah shi yake tsare bawansa, in sha Allah babu abun da zai same ki, damu kanmu,"

Ajiyar zuciya ta sauke, Cikin sanyin murya tace"in sha Allah uncle, zanyi hakan"

"Aneelerh, Idan zata kwanta bacci ki rakata dakinta, Ki yi mata addu'a," Ya fada yana duban Aneeleerh, Cikin girmamawa Ta amsa mashi da toh,

Kwantar mata da hankali suka cigaba dayi, Kowa sai da ya sanya bakin shi wurin Lallashinta da bata baki, Har saida suka tabbatar Ta samu saukin damuwarta tukunna mamie tace"daga yau kada ki sake ware kanki a daki! Kina jina ko"? Daga mata kai tayi toh

"Kidaina kuntata kanki adaki, ki dinga fitowa waje wurin su Aneelerh Kuna yin fira, hakan zai Webe maki kewa don na fahimci hada kaWaici ke damun ki" jinjina kai ana tayi alamar toh.

Gyaran murya abie yai tare da cewa"Idan kina bu?atar wani abu, Ki fadama Aneelerh ko zahra, su sanar dani in sha Allah zamuyi maki shi, kada kiji komai ki dauka tamkar Iyayenki ne" wannan maganar da abie Ya furta mata ba karamin ta6a zuciyarta yayi ba, nan take ta fashe masu da kuka mai tsuma zuciya, sautin muryarta dakyar yake fita wurin yi masu godiya.

"Ku tashi ku rakata daki ta kwanta ta huta" Ummi ce tayi maganar tana nuna su zahra, ru?o hannun Ana Aneeleerh tayi atare suka mi?e, Zahra tabi bayansu, Har cikin dakinta suka kaita, Bayan ta kwanta Aneelerh da zahra sukayi mata addu'o'i, Kafin daga bisani suka yi mata sallama, Kamar karsu barota haka suke ji, bayan sun fito daga dakin sun kulle mata kofar, zahra ta kalli Aneelerh

"Nifa tsoro yakamani aunty na, tun da naji Ana tace mafarkinta yana zama gaskiya, wallahi bana so wani abu ya samu Waya daga cikin mu"

Ita kanta Aneelerh hankalinta ba akwance yake ba, zuciyarta taki Aminta da kalaman ana, sai dai tayi kokarin danne damuwarta wurin kwantar ma zara da hankalin ta



"Zahra kin riga kin sani, mafarki ba gaskiya bane, Ni ko kadan hankalina bai tashi ba, kema kuma inaso ki kwantar da hankalinki, In sha Allah babu abun zai faru, face alkhairi"



Cikin sanyin murya zahra tace"Allah Yasa" Ta fada a yayin da suke shiga falon, komawa sukayi saman carpet suka zauna kowa zuciyarsa da fargaban maganar Ana.



Idan muka koma 6angaren su Ummin america tun bayan kammala sallar magbrib, tayi wanka ta shirya cikin Ba?ar jallabiya, tayi rolling veil akanta, ta bi ko'ina na jikinta ta feshe da turare, bakomai take jira ba face kiran Boss man, tun da ya fada mata yana son magana da ita gaba daya ta rasa sukuni ta kosa taji me ya ke son faWa mata, tana cikin yin safa da marwa a room dinta, wayarta tayi ringing a hazarce tayi picking call din, muryar boss ce ta isar mata da sakon ta same shi a down, jiki na rawa ta fito daga dakin ta sauko down stairs babu kowa a falon, duk suna a dakunansu



A falo ta same shi tsaye cikin shiga ta jallabiya, ya goya hannayensa akan kirjinsa, fuskarsa a sanye da face mask.



Da fara'a ta nufe shi batare da 6ata lokaci ba, suka jera a tare suka nufi swimming area din gidan, ko'ina ka kalla hasken fitilun lantarki ne tamkar da rana.



"ina sauraron ka Yalla6ai, tun da muka fito kayi shiru baka ce komai ba" ummi ce ta fada tana kallon Taj dake a gefenta.



"ga dukkan alamu Kin ?agara da kiji dalilin kiran da nayi maki"

Jinjina mashi kai tayi alamar Eh, A yayin da suke zama saman kujerun dake a bakin pool din masu kyan gaske, suna fuskantar Junansu.



"Nasan zakiyi mamaki idan nace maki chief ne Ya bada Sako A fada maki"

A ruWe tayi mashi farfari da idanunta cikin kagara ta furta"A message from the chief for me? Does he know about me? So what did he say?



Calmly Boss Ya furta"Yeah Yasan da zaman ki fiye da tunaninki, chief da kike gani baya zama wuri Waya da mutumin da baisan tarihin rayuwarsa ba," Wani irin bugu kirjinta yayi mata cike da fargaba ta furta.



"I don't understand what you mean! Chief ya san komai dangane da rayuwana! How is that possible?"



Dariya boss yayi ganin yadda ta shiga ruWani

"Ki kwantar da hankalin ki Ummi, Amsarki tana atare dani, ki natsu ki saurari me zan fada maki" fuskarta a yamutse ta amsa mashi da toh.

Numfasawa yayi kafin Yaci gaba da fadin"sakon da chief Yace A fada maki shi ne, Gobe Idan Allah ya kaimu, zamu fita tare da Yaran nan zuwa cikin estate din su, muna so su halarci Farewell dinner din Uncle Winsa Hateem, amma fa bama so kowa yasan da wannan zancen! Zuwan bazata zamuyi tare da su, ke kuma abun da muke so daga gare ki, ki yi kokarin shirya mana su.... " kafin Ya kare Maganar tace"wai kana nufin prime minister Hateem na canada ne za'ayiwa dinner din? Waga mata gira yai alamar eh, but amma meyasa naji kace zuwan bazata za'ayi da yaran"? Ta faWa tana mai neman ?arin bayani.

Bai 6oye mata komai ba, dangane da budurin da aka sha lokacin da Danish ya rikiWa, na?in amincewa da zaman su a family din"

Jikinta yai sanyi"Allah sarki, ashe abun da ya faru kenan, ko da yake dama zaiyi wuya su yarda da su, ni kaina lokacin daya rikiWa ba ?aramin firgita nayi ba, saboda abu ne da ban ta6a gani ba, toh su kansu abun da zai sa su ?i yarda da zamansu kenan, bayan haka hukuncin da shi baba obie ya yanke na raba ala?ar prime minister hateem da danish yayi dai dai, a fahimta na yayi hakan saboda gudun kada Wansa ya cutu.... " jinjina kai taj yai alamar gamsuwa da bayanin ta, kafin wani ya qara magana a cikin su, sai ga jami'in isod Ya fito daga ?ofar falo, hannun shi ru?e da plate mai Wauke da mugs biyu na coffee, akan table din dake a tsakatsakiyarsu ya ajiye plate din kafin yabar wurin

Tura mata mug Waya taj yayi"kisha, ni nasa a kawo mana dan muji dadin tattaunawa' murmushi tayi har cikin ranta taji dadin karamcinsa, A hankali ta Wauki mug din ta soma kur6ar coffee din, shima ya dauki nasa yana sha, bayan ta tsagaita da sha ne taci gaba da magana "kowani bawa da irin tashi jarabtar, Idan kaji na wani kai naka ba komai ba, shiyasa a koda yaushe akeson bawa ya zamanto mai hakuri dakai zuciya nesa, ha?i?a ina tausayin wadannan bayin Allah, duk da ban kaiga jin tarihin rayuwarsu ba... ' murmushi taj ya Wanyi tare da cewa"kada ki damu, nan badajimawa ba zaki ji tarihin rayuwarsu, In sha Allah"



GyaWa kai tayi "A ina za'ayi dinner din sannan ?arfe nawa ne zasu je can din"?



"A cikin Estate din nan, Bayan sallar la'asar"




Shiru tayi alamar tana nazarin wani abu, yayin da yake binta da kallo.



"Menene dress code din da za'a sanya a wurin dinner din"? ta tambaya tana kallon fuskarsa.



"abaya matan za su sanya, A cikin suturunsu mun sanya masu abaya na larabawa kala kala, A ciki za'a daukar masu masu kyau na mutunci, sannan bama son suyi shigar da zata baiyana sumar kansu, a rufe masu ko'ina na jikin su.



GyaWa kai tayi"okey, in sha Allah amma baza'ay masu make up ba"?



"Duk kyan da Allah yayi masu"? Ya faWa da murmushi kan fuskanshi, Itama ummin murmushin takeyi"masu kyaun ma su na yin make up, ko da yake naji ka ce arufe masu ko'ina na jikin su, ba bu?atar yin make up, Waga mata gira yai alamar eh.



"Tare da ni zaku tafi ne"?

"Idan kina ra'ayin zuwa"

Girgiza kai tayi alamar a'a

"Meyasa"?

"Nafi so kubarni a gida, nasan Su Unaisah zasu bani labari, har ma su daukar min video na dinner din in gani nima"



"Ban yarda ba, yakamata kema ki shirya mu tafi tare dake, zaki ji dadin shiga cikin family Win Obinna," jim ta Wanyi tana wani tunani aranta.



"Kinyi shiru baki ce komai ba"

Numfasawa tayi tare da cewa"ka yi hakuri amma zuwana ba lallai ya zama alkhairi agare ni da ku kan ku ba, bana so na 6ata maku shagalin ku, nasan ka fahimce ni" jim ya Wanyi yana jujjuya mug din hannunsa, tabbas ya fahimci me take nufi,shi kanshi yasan ba lallai chief Ya amince su tafi da ita ba, yadai Wan bugi cikinta ne don yaji idan tana son zuwa sai kuma akaci sa'a bata ra'ayi.



"Alfarmar da nake nema a wurin ku, dan Allah ku barni in fita gobe, Inaso zan ziyarci gidan ?awata dake aure anan abuja"



"Bani da wannan hurumin, Amma in sha Allah zanyi kokarin nema maki alfarma wurin chief, but inaso kisan da sani duk inda zaki je jami'in mu ne zai ka??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????i ki," har cikin ranta taji dadin maganarsa.



"Idan akwai abun da kike bu?ata ki faWa min" cikin kulawa yayi mata maganar yana dubanta.



"Dan Allah ka fadamin shin dagaske ne chief Yasan komai dangane da rayuwana"? Ta fada cike da fargaba.



Jim ya Wanyi yana dubanta kafin Yace" "I'll give you an assignment. If you can find the answer, then I'll tell you what you want to hear," A ?agare ta ke kallon shi, A hankali Ya sanya yatsun hannayen shi tare da zame mask din fuskarshi.



Wani irin kallo ummi ta soma binshi da shi, Yau ne karo na farko da ta fara Yin tozali da fuskar Boss man, bata ta6a tsammanin Yana da kyawun fuska har haka ba.



"Dama haka kake da kyau"? da alamun mamaki ta furta maganar, Murmushin gefen fuska Ya sakar mata har dimple dinsa ya lotsa, nan take ta soma kokarin tariyo inda tasan fuskarshi sai dai kash takasa tunawa amma tabbas tana ji aranta ta ta6a sanin shi ko kuma wani ne me kama da shi.



"Ina da aure, Ki daina kallona, matana tana da kishi, zata iya yin komai akaina" da zolaya taj yayi maganar.

Ummi tace"tasan tana da kishi meyasa ta auri namiji mai kyan sura? Ay kamata yayi ta auri mummuna, ni fa bazan 6oye maka ba, ka jima kana bani mamaki kai da abokin aikin ka big guy da chief din ku, tun da nataso rayuwata da wuya a samu namijin zan gifta awuri batare daya bi ni da kallo ba harma ya neme ni, amma ku sam babu wannan tunanin aranku, zuciyarki a tsarkake take, hakan ba karamin daure min kai yake yi ba, shi chief mace ko kallo ma bata ishe shi ba, wata irin dakakkar zuciya ce da shi.



?ayataccen Murmushi Taj Ya sakar mata batare daya furta mata ?ala ba



"Wallahi nasan ka, sai dai bazan Iya tuna a ina nasan ka ba, ni hatta muryarka na jima ina son tuna ina na son ta," still face dinsa da murmushi Yake dubanta.



"Amma meyasa kake yi min kama da Unaisah? Ko dai idanuwana ne suke nuna min badai dai ba"?



"Ba laifin idanuwanki bane, Unaisah ?ata ce, Jini na ce, Ni mahaifinta ne, asalin sunana Tajuddeeen,"



"I can't believe it, Unaisa fara ce zan iya sanyata a jinsin larabawa, kai kuma daga ganin ka hausa fulani ne"

"A salin sunana Zaheer Tajudeen, Zaheer sunan Mahaifina ne, Tajudden kuma sunana ne, Ki tambayi Unaisah menene full name dinta zata fada maki da bakinta, Ita kanta ayanzu haka batasan cewa Ni mahaifinta bane ?addara ce ta rabamu, sai gashi cikin ikon Allah mun sake haWuwa," murmushi ummi tayi"Allah sarki, Na tayaka Murna, amma mahaifiyarta wani jinsi ce"?

"Hausa Arab ce" Dariya Ummi tayi cikin raha ta furta"hausa arab! Bayan hausa fulani har Hausa rab ke da akwai, ban ta6a ji ba sai akanka"

"Ina nufin Half cast ce, Mahaifinta hausa fulani ne, mahaifiyarta kuma Balarabi ce" gyaWa kai tayi"masha Allah, shiyasa yarinyar taka takasance fara sol, Ga gashi tubarkalla amma tsakanin kai da mahaifiyarta halin wa ta Wauko"? murmushi yasaki yana dubanta yace"meyasa kika tambaye ni"?

"Unaisah tana da faWa, daga ka kalli idanunta zaka shaidan hakan, ga wayau da kaifin basiri Allah Ya bata fiye da sauran ?an uwanta" ha?i?a Yaji daWin Yabon da ummi tayi mata,

"Haka mutane suke cewa, shiyasa nima nake alfahari da ita, Inason Unaisah, fiye da yadda nakeson kaina, A halin Yanzu bani da tamkarta a duniyarnan, Itace ta rage min wadda nake gani naji sanyi araina, silar unaisah nasamu alheri da dama wadanda idan na fada maki su zakiyi mamaki, Waya daga ciki Unaisah itace silar haWuwana da Chief" da mamaki Ummi ta Wan zaro mashi sexy idanunta haWi da buWe baki, Jinjina mata kai yayi" Murmushin gefen fuska tasaki"Ina ?ara tayaka murna, Yarinyarka Jarinka ce, Allah Ya albarkaci Rayuwarta" amsa mata yayi ameen, daga ita har shi sun ji daWin zaman firar da su kayi, Ha?i?a taj ya Webe mata kewar kaWaicin dake damunta, ta ?ara ganin mutuncinsa da ?imarsa a idanunta, Sai dai tarasa gane meyasa take jin kamar ta ta6a sanin shi? Musamman daya faWa mata sunan shi sai yawo yake mata akai.



Ni'imtacciyar Iskar dake kaWawa ta ?ara masu ?aimin firar ta su, kafin wani lokaci taj yace da ita"kada na cika ki da surutu, ko zaki koma ciki ne"? Fuskarta da fara'a tace"no ko kusa, ni baka takuramin ba, saima Webe min kewar da ka yi, naji dadi fiye da tunanin...... " bata ?arasa maganarba sakamakon sautin dirar motar daya ratsa kunnuwanta, kusan atare suka juyo suna duban motar.




Bayan sojan dake driving din motar yayi parking, Ya fito Ya zagaya ya buWe mashi murfin back seat dinta, ?afarshi kaWai


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login