Showing 93001 words to 96000 words out of 391264 words

Chapter 32 - Cigaban Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel

11 Feb 2025

2625

dinga yi mata a karshe da sukaga bata da niyar bari su ta6a ba, aiko da gudu suka nufeta gaba daya suka Wauke ta suka Waga ta sama suna jujjuyata, tuntana kuka tana fadin su sauke ta ?asa, Har dai ta fara ti?ar dariya ba don ta gane su ba, sai don jin dadin abun da sukeyi mata, sauke ta kasa sukai da sauri Haris ya rungumeta ajikinshi suka ?an?ame juna, ta yi lamo tana faman sauke ajiyar zuciya kamar tana son ta tuna shi sai dai takasa.



Ru?o hannun Mubeen Angel tayi acikin nata, idanunsu cike tab da ?walla suke kallon juna, ta ji tausayin shi, ba zata ta6a manta abun da ya faru lokacin da zasu bar kurkuku ?addara ya yanke jiki ya faWi haka suka haura kafa suka barshi, bawan Allah ashe har ciwo yayi,

Huggin dinsa tayi a kirjin ta, hannayenta daddafe da bayan shi, shima ya dafe ta cike da kaunar junansu,

Hankalin danish bai kai kansu ba, ya basu ya baya, hannayen sa suna acikin na salsabeel sai faman sakar ma juna murmushi sukeyi, wani irin dadi ne Ya lullu6e kowannan su

"Kaine silar komai danish" salsabeel ne ya fada yana dan bubbuga shoulder din sa alamar jinjina



Duk wannan abun dake faruwa akan idon sheikh imam babu wanda Ya lura da shi, Shigowar sa kenan falon Ya taras da abun farin cikin dake faruwa hakan yasa shi tsayawa abakin kofar yana kallon abunda yai matu?ar faranta ransa.



Hatta Taj da big guy murmushi ne Wauke akan fuskokinsu, kamar waWanda akai wa albishir da gidan Aljanna babu wanda basu burge ba acikin su, sun tausayawa rayuwar su, ga wani irin son yaran da kaunar su da ya mamaye zuciyoyin su.





Ummin america dake ta kallon su, idanunta sun yi jawur saboda kukan da tasha, dama ba ta jima da gama yin shi ba, gaba Waya idanunsu na akan prisoners dake ta tsalle tsallen farin ciki a tsakar falon suka rurru?e hannayen junansu tare da kewaye kawunansu suka haWasu guri guda gwanin ban sha'awa yadda kasan fararen furanni a garden tsabar kyan da sukayi.....



Cikin Harshen Larabci sheikm Imam Ya fara karanto masu addu'o'i yayin da yake ?arasa shiga cikin falon gaba Waya hankali ya dawo kan shi, da sauri suka raba kawunansu tare da Waga hannayensu sama suna amsa mashi da ameen ameen, mutun Wayane baya amsa addu'ar sheikh imam wato Danish, har Yanzu bai matsa daga gefen Salsabeel ba.





Bayan ya gama jera masu addu'o'in kowan nan su Ya shafa akan fuskarsa.



Kafin su sauke hannayen su, sautin takalman mutanan da ke shigowa falon taja hankalin su ga duban su



Chefs din dake girka abincin gidan ne suka shigo hannayen su ru?e da ?aton Cake stand mai hawa bakwai an ?awata shi yayi matu?ar jan hankulan su.



Bayan sun sauke masu cake din akan glass table, ba su tafi ba, tsayawa sukai don ayi shagalin da su.



Cikin harshen turanci Waya daga cikin chef din yace"muna tayaku murnar haWuwa da ?an uwanku, kuma muna tayaku murnar samun ?an ci arayuwar ku, sannan muna yi maku fatan Allah ya dawwamar da farin ciki arayuwarku" gaba Waya suka haWa baki wurin yi masu godiya.





"Bismillah, wannan na ku ne, chief ne Ya bada Umarnin A haWa maku Cake, saboda ku ji daWin yin shagalin murnar ganin yan uwanku" Waya daga cikin chefs dinne Ya faWa, bayin Allah saboda farin ciki hawaye ne suka cicciko idanunsu waWanda suka kumbura saboda kukan da suka sha.



Hannayen su ru?e cikin na juna suka kewaye Cake din, Lokaci Waya wani abu ya faWo masu aransu wanda ba komai bane face farkon zuwan Sabbin prisoners gidan kurkukun ?addara, ba zasu ta6a mantawa da lokacin ba har abada, ranar da giants suka kawo masu cake sunata murnar yanka shi akarshe majnoon yayi ajalin shi.



cikin shesshe?ar kuka jemimah tace"Genie Ina majnoon Wina? shi bai dawo ba? Yakamata shima Yazo tun da su deeja ma da suka mutu sun tashi"



kumatunta jawur tayi maganar, gaba Waya ta karya masu zuciyoyin su.



"Jemimah wanda ya mutu ba ya dawowa sai dai idan dama kwanansa ne ba su ?are ba, Majnoob Ya mutu ba zai ta6a dawowa awannan duniyar ba, amma in sha Allah zamu haWu da shi agidan aljanna" yayin da Unaisah take yin maganar bakomai take tunawa ba face fuskar majnoon da unaizah, hakika ba zasu ta6a mantawa da farkon zuwanta gidan kurkukun ?addara ba, lokacin da ta sauko kan stairs cikin shiga ta school uniform red colour, ?ar gayu da ita wayayya ta goya back dinta abayanta.



muryarta ce ta soma yi ma unaisah gizo a kunnanta.



_Hi, Am unaizah ?ar gidan daddy, can i know u_



_that's Impossible, ae ni bana sharing soson wanka, Kuma bana wanka in ba a cikin bathtub ba, I can't stay here i wanna go home, cos daddy ba haka Ya kwatanta min school Win ba, Yace min fa komai irin na Gidan mu ne, but why naga banbanci_



Runtse ido unaisah tayi yayin da take jin wani irin kewarta a zuciyarta, tayi fatan ace gaba Wayansu ne suka rayu sai dai kash Allah baya barin wani dan wani yaji dadi.



Siraran hawaye ne suka wanke fuskar Sajeed tunawa da yar uwarsa Gabriella wadda a halin Yanzu ba shi da tabbacin tana araye kota mutu, lokaci Waya sautin muryarta ya soma cika kunnuwansa farkon kasancewarsu agidan kurkukun ?addara lokacin da za'a raba su da junansu tana kuka tace



_ My twin bro, Ka kula min da kan ka, Duk inda za'a kai ni zan dawo wurin ka_



Kowa da abun da yake tunawa aran shi, ganin jimamin nasu bame ?arewa bane yasa sheikh Imam Yi masu nasiha mai ratsa zuciya, ya dinga jawo masu ayoyin kur'ani Yana fassara masu har saida yaga sun samun nutsuwa tukunna Ya dakata...



"Waye zai fara Yanka mana cake din"? boss ne ya faWa yana kallon su don jin za6in su, Har suna hada baki wurin furta"Unaisah"



Idanunta amarairaice ta kalli faces din yan uwanta kafin ta sanya yatsun hannunta dake kerma ta dauki ?aramar wu?a, har taj ya yunkura zai ru?o hannunta don ya taimaka mata ganin hannun ta na kerma, tunawa da danish yasa shi fasawa don har yanzu bayanshi bai daina yi mashi zogi ba.



A hankali ta yanko cake din tare da Wagowa tana kallon su idanunsu duk suna akanta, tama rasa wa zata fara bama cake din duk da akwai wanda zuciyarta ta aminta da cancantarsa, satar kallonsa tai nan take idanunsu suka shiga cikin na juna,



"Angel ki ba danish, shi Ya cancanta ki bamawa," muryoyinsu sajeed ne suka cika kunnuwanta.



kau da ido tayi daga kan danish ta kalli daddynta, Lumshe mata idanunsa yai alamar ya amince mata.

Murmushi ta Wan saki har dimples dinta suka lotsa, matsawa tayi kusa da danish, ta mi?a masa cake din ya buWe ?aramin bakinsa ta sanya masa, gaba daya suka soma tafa masu, Bayan ta ?ara cirar wani cake din ta mi?a ma daddyn ta Yaci.



daga bisa ni ta mi?a ma Haris Wu?ar, Ya kar6a Ya datsi cake din ya sanya wa deeja abaki, wani irin farin cikine Ya lullu6e su



Bayan ta gama taune na bakinta, ya bata wukar don ta bashi, abunka game tabin hankali, maimakon ta kar6i wu?ar sai ta sanya hannu ta 6allo ?ato ta duma masa abaki har cikin hancinsa ya shiga, gaba Waya suka sanya dariya, cike da nishadi.



Kar6ar wukar batool tai, ta ballo cake din ta ba mubeen Abaki Yaci, Kafin Ta sake gutsuro wani ta mi?a ma Rubina itama taci, Waya bayan Waya duk sai da suka ciyar da junan su cake din.



Tunawa da aunty umminsu dake ta kallon su, yasa batool ta sake kar6ar wukar daga hannun Sarah, ta yanko cake din taje gaban ummi ta mi?a mata, murmushi tasaki tare da ru?o hannun batool ta tura shi abaki tana taunarsa Wagowar da zatayi kwatsam suka haWa ido da sheikh iman dake ta satar kallon ta, duk sai taji jikinta yayi mugun yin sanyi, tuni taji wasu hawayen sun cika idanunta, muryarta na rawa tace da batool"ba ki ba sheikh imam cake din ba" tana fadin hakan tai saurin juyawa ta nufi hanyar komawa bedroom dinta, sam yakasa janye idanunsa daga kallon ta hatta su taj sai da suka lura da kallon ummi da yakeyi sai dai basu kawo komai aran su ba.



Jiki asanyaye Batool ta ?ara yanka wani cake din taje gaban sheikh Imam Ta mi?a mashi, sai da Ya fara Waura tafin hannunsa akanta ya Wan shafa shi ya furta"Allah yayi maki albarka" kafin Ya buWe baki ta saka mashi cake din'



Murmushi kowan nan su Yasaki gwanin ban sha'awa.



Da zolaya big guy yace"yau an nuna min wariyar launin fata, Ni babu mai bani cake din"?



da sauri sajeed yace zan baka, girgiza kai yayi"I'm sorry Ni mace nakeso ta bani ba jin sina ba" dariya suka sanya gaba dayan su.



Harara boss yadan jefa masa cikin muryar raWa Yace"kai bana son iya shege fa, halan tazurancin naka ne Ya motsa" ?ar dariya yai har hakoransa suka bayyana.



"Ni zan baka cake din" jemimah ce tayi maganar, da karfin hali fuskarta sharkaf da hawaye, gaba Waya suka sanya dariya,

matsawa big guy yai tare da kai hannu ya dauki Jemimah, kafin Ya bata wukar Ta yanka ta bashi abaki, shima ya karbi wukar ya 6allo cake din Ya sanya mata abaki.

Sautin tafin su Ya cika falon, wunin ranar shagali sukayi babu kakkautawa yadda kasan gidan biki.





_______________________________
'?





Safa da marwa takeyi a tsakar dakin ta, fuskarta dauke da tsantsar farin ciki, gaba daya ta shagala da tunanin Yar ta Angel sam ta manta da zancen tafiyar su, zumuWi Ya hana ta zauna jira take Aneelerh ta tura mata da hotunansu duk tabi ta kosa da son ganin fuskarta



Jin ?arar shigowar sakonni ta whatsapp din da ta buWe ne, yasa tai saurin duba screen din wayar dake ruke a hannunta, wayyo Allah dadi, tsabar zumudin ta buWe sakon Aneelerh yatsun hannunta har kerma sukeyi, lokacin da ta Waura idanunta akan hoton Unaisah ?afafuwanta kasa Waukarta sukai, awani slow ta koma gefen gado ta zauna hannunta Waya dafe da bakinta take kallon hotunan Unaisah, yayin da zuciyarta ke harbawa da karfi da karfi tun da take a duniyar nan bata ta6a jin son wani Wan adam fiye da yadda takeson ?arta, duk da basu taba haduwa ba amma taji wani irin mahaukacin son yarinyar na ?ara shigar zuciyarta.



Hotunan da Aneeleeh ta turo mata na unaisah tun tana jaririyarta nannaWe cikin farin towel, hada hotunan Birthday dinta lokacin ta cika shekara goma aduniya, sunyi kyau hotunan kamar lu'u lu'u



Wani irin sanyine Ya ratsa zuciyar benazir, a kalla ta shafe mintuna tana kallon hotunanta, kafin ta buWe na baby junaid din Aneeleeh, Murmushi tasaki tana kallon kyakkyawan yaron kamar sabon fure ya kwanta mata aranta, Bakomaine Ya faWo mata aranta ba face Fatimar yaya shureim ita kadaice babu acikin su



A hankali ta furta"Allah sarki Aisha ke kadai ce babu jinin ki araye, mun yi babban rashi, Allah yaji?an fatima Allah Yasa mai ceto ce....." idanunta cike tab da kwalla tayi maganar.





"Benazir zaman me kike yi"? Rass taji gabanta ya fadi jin muryar hajiya layla, a hanzarce ta dago tana duban kofar shigowa dakin, Hannunta ruke da trolley din kayanta, fuskarta babu fara'a sai faman huci take yi, Shigowa dr shureim yayi da sauri yana kokarin shawo kanta"mommy dan Allah ki yi hakuri ki fasa tafiyar nan, kinga daddy bai amince maki ba, Yakamata kibi umarninsa ko dan gujewa fushin ubangiji...." harara ta watsa mashi tana fadin"shureim zan 6ata maka rai wallahi, Idan kai bazaka bi ni ba to ka ?yale ni in kama gabana, har yaushe ne zan cigaba da zama ana raina min wayau agidan nan? nafa san me nake yi, ni ba shashasha bace..." mai da dubanta tayi ga benazir wadda tuni ta mi?e tsaye damuwa ce tsantsa akan fuskarta.



"Wuce mu tafi, Idan kema ba zaki bi ni ba, to ki zauna tare da su" ta fada rai a6ace.



Cikin sanyin murya Benazir tace"mommy ki yi hakuri dan Allah, kinsan bazan ?i bi umarninki ba amma bazan iya tafiya ba...." baki asake Layla ke kallon ta.



"Nima ba son zama gidan nakeyi ba, Aneeelerh ce ta kira ni awaya, kiran da muke ta jira, sai yau Allah Ya nufa, dan Allah mami kibarni in hadu da ita inyaso daga baya sai mu tafi"



Girgiza kai hajiya layla tayi"kawai kizo mu tafi, in mun fita zamu fara biyawa gidan su Aneelerhn kafin mu tafi" da ?arfin hali tai maganar, ita kanta tana jin fargaban zuwa gidansu aneelerh saboda bata so Benazir ta gane karyar da tayi mata nacewa su taj sun bar kasar amma a halin yanzu idanunta sun makance burinta su bar gidan duk abun da zai faru ya faru.



Gyada kai Dr shureim yayi"ki bita ku tafi, Allah Ya kiyaye hanya, Ni zan jira daddy"



Tsoki layla taja, tare da juyawa ta nufi kofar fita daga dakin, da sauri benazir ta dauko mayafi, dr shureim ne ya janyo mata trolley din kayanta, lokacin da suka fito falon gidan, yayi dai dai da fitowar su Hajiya sarah da gudu zeenatu ta nufi benazir tana kuka ta ru?e mayafinta.



"Aunty benazir kada ki tafi kibarni, dan Allah kada ki tafi, Mami Dan Allah ku yi hakuri ku zauna, Idan wani abu mukai muku badaidai ba zamu gyara, Ni dai banso ku tafi"



"zeenatu zonan"! Muryar Alhaji musace ta katse mata koke koken nata, jiki ba kwari ta saki mayafin benazir ta koma wurin shi ta tsaya, ru?e hannunta yai acikin nashi, Hajiya sarah kamar an rufe mata baki takasa ta6uka komai sai kallon su da take yi, dakatawa sukai da yin tafiya jin muryar Alhaji ubaid



"Wallahi idan kika sa kafa kika bar gidan nan batare da yawuna ba, to ki sani abakin auran ki"!! hankulansu Dr shureim atashe suke kallon shi har suna hada baki wurin furta daddy meyasa?



Dariyar takaici layla tasaki tana tafa hannu tace"sai me donka sake ni? Ni dama ay najima da gajiya dakai tun lokacin da na gane kai bakomai bane face rakumi da akala, Ina amfanin zama da namiji solo6iyo irin ka"?



Rai a6ace ta faWa tana kallon cikin idon shi, Kalamanta sun ?ona masa rai, da?yar Ya iya hadiye yawu mai Waci ba tare da ya iya furta komai ba.



Dauke idonta tayi daga kanshi ta kalli Alhaji musa, dake atsaye ya harWe hannuwansa kan kirjinsa fuskarsa babu fara'a



Harara ta watsa mashi kafin tace



"Hankalinka Ya kwanta Ka shiga tsakanina da mijina, In sha Allah zaka ga sakayyar hakan" wani kallon ?asan ido Ya watsa mata mai wuyar fassaruwa.



"Shureim Benazir, kada ku bi ta idan har na isa daku, Kubarta ta tafi ita kadai tun da bata jin maganata" acewar Alhaji ubaid.



Murmushin takaici layla tasaki, ba tare da ta ?ara furta kalma ba ta juya a fusace tabar falon



"Ka bar su su tafi" Alhaji musa ne ya fada agadarance.



Da sauri benazir taja trolley dinta tabi mommynta, shima shureim yabi bayanta



A bakin motar shureim ta tsaya zuciyarta a kuntace, batai tsammanin zasu biyo bayanta ba



Dr shureim na ?arasowa Ya buWe mata back seat din motar ta shiga ciki, sannan ya sanya masu trolley din kayan su a boot, daga bisani itama benazir ta shiga ciki.



Bayan ya shiga ya zauna a driver's seat, yai ma motar key, zuciyarsa cike fal da damuwar abunda Ya faru, yaji takaicin yadda Alhaji musa ya nuna halin ko'in kula akan tafiyar mamin su, abun da Yafi bata masa rai furucin mahaifinsu yansu shikenan yana ji yana gani auran iyayensu zai rabu"?



"Shureim! Ya akai naga ka dakata da yin driving din"? Cikin rauni na murya yace"mommy Kiyi hakuri mu koma, idan kika tafi ya kike so muyi da rayuwarmu? Ke kanki bazaki so abun da zai tarwatsa farin cikin mu ba...."



Shiru tayi tana nazarin maganarshi, ga dukkan alamu jikinta yayi sanyi lakwas



"Mommy, kina atare damu Ya muka ?are inaga idan baki nan? Duk wani mai nufin mu da sharri zaiji dadin cutar da rayuwarmu, bayan haka mommy tsawon shekara nawa kuna atare da daddy, auren soyayya kukayi kun tara zuri"a da dadi da ba da daWi kunyi hakuri kun jure zama da juna sai akan wannan dalilin zaki kashe auranki? Mu kanmu bazamu ji dadi ba dan Allah ki tausaya mana mommy ku dubi girman Allah ki fasa tafiyar nan ko dan saboda mu"



benazir ce tayi maganar tana duban fuskar mami kamar zata sanya mata kuka.



Zancen zuci ta soma yi



_wannan hanyar dana Waukarwa kaina ba me 6ullewa ba ce, ?wara in tsaya in ?watar mana ?ancin mu, dole Inyi faWa ko da kuwa zan rasa raina ne saina shiga tsakanin mu da shi_



Ba zato ba tsammani suka ga ta buWe motar, wani irin farin ciki ne Ya lullu6e su, da sauri benazir ta fito shima shureim Ya fito suka dauko trolley dinsu dake a boot suka bi bayanta.



Kamar yadda suka bar su hajiya sarah tsaye a falon haka suka taras da su, sunyi mamakin dawowar Hajiya layla, ko kallo ba su isheta ba, Kai tsaye ta wuce room dinta



Da gudu zeenatu ta nufi benazir suka rungume juna suna dariyar farin ciki,



Fuskar hajiya sarah dauke da murmushi ta dubi dr shureim"ta fasa tafiyar ne"?



"Eh mommy," ya bata amsa, Har cikin ranta taji dadin dawowarsu.



Mutumin kuwa murmushin gefen fuska Ya Wan saki, yayi tunanin security officers din gidanne suka hanata tafiya baisan cewa itace tai ra'ayin kanta ba, fucewa yai daga falon cikin takun isa.



Alhaji ubaid dake kallonsu ajiyar zuciya ya sauke.



"Daddy, dan Allah kuyi hakuri da abunda Ya faru atsakaninka da mommy, ku yi kokari ku sasanta junanku"



Jinjina kanshi yai fuskarshi dauke da murmushi yace"kada ka damu shureim, ni dama ban dauka da zafi ba, itace ke da matsalar, in sha Allah zanje na lallashe ta" ya fada tare dakai hannu yadan bubbuga kafadarsa kafin Ya juya ya nufi dakin layla don su sasanta junan su.



Koda ya shiga Wakin, ya taras da ita zaune agefen gado, kamar mai jin shakkarta Ya raba ya zauna yana duban ta



kafin yai magana tai saurin katse shi da cewa"basai ka bani hakuri ba, ni yakamata na nemi yafiyarka, ka yi ha?uri idan na 6ata maka rai, in sha Allah bazan ?ara ba, zan bi umarninka in zauna har zuwa lokacin da


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login