Showing 162001 words to 165000 words out of 391264 words

Chapter 55 - Cigaban Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel

11 Feb 2025

2619

"ba kai kadai ba shureim, nima yarinyar ta burgeni, ga wayau daga gani tana da kaifin basira, iyayenta sunyi mana hallaci kuma basu nemi komai daga gurin mu ba, ko da yake naga yarinyar ma ?ar masu arziki ce...."

Dr shureim ya ce "Mommy zan wuce gida dare yana ?ara yi, pls ki kula da yarinyar nan, kinga dai yadda yan'uwanta suka dam?a mana amanarta, bana so asamu matsala..."

"In sha Allah Shureim, ay bazan yi sakaci da rayuwarta ba, dole inyi takatsantsan tun da naga Wiyar manya ce, hada fa jami'ai cikin waWanda suka kawo ta"

?ara tattaunawa suka yi kafin ya yi mata sallama ya buWe motar shi ya shiga ciki, akan idon ta motar ta fuce daga asibitin, ajiyar zuciya ta sauke kafin ta juya ta nufi ciki cike da zumudin son ganin yarinyar..

______________________________
'?

Bayan su taj sun rako chief part dinsa, saida suka ga shigarshi cikin bedroom dinsa kafin suka sauko falo, har sun kusa fita suka tsinkayi muryar ummi daga bayan su

"Boss sannun ku da zuwa"! Atare suka juyo tare da kallonta, sleeping gown ce a jikinta, ta yafa mayafi akanta, da alama ta fara bacci ta farka

"Yawwa Ummi, me kike yi har yanzu bakiyi bacci ba"?

Fuskarta ayamutsa tace"na kasa bacci saboda damuwar rashin unaisah, tun wuraren karfe takwas da rabi muke ta nemanta saboda muyi dinner shiru babu ita, ko'ina mun duba, ?an uwanta ma dakyar na kwantar masu da hankali har su ka yi bacci, nayi zaton ko taje part din ka ne" Tay maganr tare da nuna taj



Big guy dake kallon ta from head toe gaba daya ta jefa shi ayanayi, saboda kayan baccin jikinta sun bayyana surarta,



"Ummi, unaisah ba agida zata kwana ba, taje asibiti" bai ?are maganr ba, ummi ta zaro ido tare da dafe kirjin cike da tashin hankali tace"inna lillahi meke damunta? Bata da lafiya ne"? abun da yasa ta ruWe saboda halin data ganta dazu a daki, abun ya tsaya mata arai, har jiran zuwanta tayi kamar yadda tace mata zata zo amma shiru bata neme ta ba...

Kwantar mata da hankali taj yai"lafiyarta ?alou ba ita ce ke bata da lafiya ba, yar uwar chief ce...." bayani yayi mata dalla dalla, lokaci daya ta sauke ajiyar zuciya,

"Hankalina har ya kwanta, amma banji dadin tafiya da tayi batare data yi mana sallama ba, yanzu sai yaushe zata dawo gida"?

"Bani da masaniya, amma bana tunanin zata dauki lokaci, pls ki kwantar ma yan uwanta da hankalli banaso su sanya damuwa aransu"

"In sha Allah, mu kwana lafiya boss, agaida min da madam" ya amsa mata da toh, satar kallon big guy tay ya wani tsareta da ido, harara ta dan watsa mashi haWi da yin murmushi ta juya ta nufi ciki, harta bace ma ganinsa bai kauda idonsa ba, sai da taj ya bugi kafadarsa kafin ya juya suka fuce kowa ya nufi part dinsa..

______________________________
'?

Prisoners Shield=ؔ?

Bawan Allah, kwata kwata baya acikin hayyacinshi, Yasha bakar wahalar radadin da zuciyarshi keyi mashi, tun safe har kawo iyanzu da dare ya ratsa ko ruwa bai gifta makoshin shi ba, saboda tashin hankalin da yake a ciki, yayi haukan yayi kukan amma babu abunda Ya canza nadaga kuncin da yake ji, babu wanda yayi tunanin ya leko dakinsa yaga awani hali yake ciki, saboda su kansu yan uwan nashi yanzu mantawa su ke yi da shi tun da suka fahimci bayason shiga cikin su kuma baya son kowa ya ra6e shi, a fahimtarsu, unaisah ita kadaice ta damu da shi, bata iya wuni batare da ta leko dakinsa ba, ta damu da shi fiye da yadda ta damu da kanta, itace farin cikinsa kuma gatansa, baya jin zai iya rayuwa batare da ita ba, Unaisah kaddararsa ce! Bugun zuciyarsa ce.

Cikin ikon Allah bacci mai nauyi ya Wauke shi, hakan ba karamin relief ya sama mashi ba, yayi bacci sosai har na tsawon awanni, gab da za'a fara kiran sallar asuba, ya fara mutsu mutsu, yatsun hannayensa dana kafarsa suka fara kerma....."

Farat Waya ya buWe idanunsa waWanda suka kaWa jawur tamkar garwashin wuta, Gaba Waya rasa ?warin gwiwarshi, kamar matacce Sam ya kasa motsawa daga kan floor, ko yatsansa Ya gaza Wagawa, wani irin gumi ne Ya wanke jikinshi kamar wanda aka tsamo daga cikin teku, ta ko'ina zufa ke tsatsafo mashi, ga wani azababben zafi da jikin shi ya Wauka.



shatun jijiyoyin goshinsa sun fito rudu rudu kan fatarsa,a kalla ya shafe mintuna yana kokarin sarrafa zuciyarsa gudun kada evil heart dinsa ta motsa, bakomai idanunse ka hango mashi ba face fuskar Unaisah.



Dakyar ya samu kwarin gwiwar motsa gabban jikinsa, Ya lalla6a Ya mi?e tsaye kan ?afafunsa, jansu ya dinga yi saboda wani nauyi da sukai mashi dakyar yakai kan shi toilet ya faWa ciki yana jan numfashi, agaban sink ya tsaya yana faman sauke ajiyar zuciya.



Sannu a hankali brain dinsa ta fara tariyo mashi abunda Ya faru daren jiya atsakaninsu, yaga komai a mafarkinsa.



Wago da hannayensa yayi tare da saita su saitin fuskarshi Ya ?ura ma tafukansa ido Yana kallon su ....da sauri ya girgiza la66ansa na kerma ya furta"bani bane! Bada son raina ba, bansan na akaita ba, bana a cikin hayyacina!...." dafe kansa yai da hannu Waya ya cusa yatsunsa acikin sumar kanshi, ya cigaba da cakuWata gaba daya ya haukata gashin kanshi, duk ya rikice saboda ya gane shine da kafafuwansa Yaje dakinta adaren jiya har yayi mata aika aikar nan sai dai yayi imanin bayin kanshi baneW' cije la66ansa yayi har saida suka fashe jini ya fara WiWWigowa, wani irin tsanar kanshi ne Ya kama shi, kamar ya kashe kanshi haka Yake ji, da karfi ya buga forehead dinsa jikin sink nan take fatar wurin tayi jawur kamar zata fashe, buga kanshi yacigaba dayi yana sambatu yana fadin Ni ne da kaina na cutar da Angel dina? tana kuka tana rokona dan in taimaka mata amma nagaza share mata hawayenta, bani da tausayi, ni mugune, na tsani kaina..." jinine ya fara gangarowa ta kofofin hancin shi, wani irin jiri ya fara kokarin kwasarshi, ya fara tangal tangal zai kife kasa kwatsam ba zato ba tsammani Yaji hannu mutun akan damtsensa, gaba daya ya janyo shi tare da rungume shi akan broad chest dinsa, ya zagayo da hannayensa akan bayan shi, bawan Allah baya gane komai, idanunsa sun makance, ji yake tamkar angel dinsa ce ta rungume shi, hakan ya shi ?ara ?an?ame mutumin da ya rungumeshi duk ya 6ata mashi gaban Rigarshi da jininsa, hakan baidame shi ba, babban tashin hankalin shi halin da yaron yake aciki! Ya tsorata da ganin yadda yake kokarin kashe kan shi W'lamarin yayi matukar gigita shi..

"Ki yafe min Angel, ba yin kaina bane, bazan iya cutar dake ba, sharri akaimin, ba halina bane, ki tausayama rayuwata, ke kadai ce farin cikin da nake da shi a duniyar nan, bani da gata daya wuce ke...." gaba Waya sambatunsa acikin kunnan sa, Ya nutsu Yana sauraron shi, har lokacin bai Wago da kan shi ba, balle har yasan wanene Ya rungume shi.

___________________________________
'?

*Ga me bukatar karanta littafin kurkukun kaddara, 500 ne dukanshi za'a tura Via Opay, 8103884440 Hafsat Bature Muhammad, shaidar biya za'a tura ta whatsapp, 08103884440*

Sponsored Post
Tags
Kurkukun Kaddara
YOU MIGHT LIKE
POST A COMMENT
Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.


Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
Facebook
twitter
YouTube
Instagram
Whatsapp
SUBSCRIBE US

OPINION
FACEBOOK
COMMENTS
CATEGORIES
Africa
(1)
Al'adu
(1)
Alkamawa
(3)
Article
(3)
Blogger Tips
(1)
Economy
(5)
Education
(2)
Entertainment Gist
(1)
Gyaran-Jiki
(5)
Health
(13)
Jikar Iya
(11)
Kimiya
(1)
Kiwon Lafiya
(54)
Kukan Zuci
(5)
Kwalliya
(4)
Labaru
(23)
Lifestyle
(1)
Ma'aurata
(1)
News
(300)
Nigeria
(5)
Noma
(1)
Opinion
(3)
Picture
(3)
Politics
(15)
Profile
(2)
Q&A
(1)
Ramadan
(9)
Ramadan Tafsair
(1)
Siyasa
(1)
Sports
(72)
Tarihi
(5)
Technology
(1)
Tips
(3)
Video
(3)
YouTube
(5)
Zain Abeed
(1)
Zamantakewa
(1)
Novels Elite
Get the Most Exciting News and Read Your Favorite Hausa Novels. Let us be your source for exciting news reports worldwide, as well as access to a wide variety of blogs and blogging tools. We also offer novels in different languages including Hausa so you can easily read what interests you! Plus with our Google Adsense partner program, monetize when readers engage with your content.

Novels Elite
SUBSCRIBE
Posts
Comments
Links
Post a Job

LATEST POSTS

ADVERT
Novels Elite
Copyright ? 2024 Novels Elite | All Rights Reserved
DMCA.com Protection Status
Disclaimer |
Privacy Policy |
Terms and Conditions
[14/10, 6:05 PM]  Amin@ M Yusuf Yol@: Novels Elite

Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun ?addara Takun ?arshe chapter 33 Complete
by
Novels Elite Admin
August 29, 2024
Takun ?arshe

'?

EPISODE 33

Sai da yayi mai isarshi kafin A hankali chief ya raba jikinsu daga na juna ya tallabo fuskarshi da tafukansa, kwata kwata babu kuzari a jikin shi kamar lagwanin fitila, fuskarshi ta 6ace da blood dinsa, idanunsa sunyi nauyi dakyar ya iya buWe su ya kalli chief yana faman jan numfashi, wani irin tausayin shi ne ya kama shi ga tsananin ?aunar yaron da yake ji, duk da baisan meke damun shi ba, a sambatun da yayi, chief ya fahimci sun samu sa6ani ne tsakanin shi da Unaisah! Shiyasa jiya a mota ta dinga yi mashi kuka, har tayi mashi karyar bata jin dadin jikin ta, yanzu kuma ga Wan uwanta yana sambatu akanta har yana yunkurin halaka kan shi, hakan na nufin akwai wani abu daya shiga tsakaninsu wanda yayi silar jefa su halin da suke ciki?! Abun ya daure mashi kai.!





"Bansan meke damunka ba! banji dadin yadda kake kokarin illata kanka ba! Meyasa ba zaka nemi taimakon mu ba uhyum?



Cikin kulawa yayi mashi maganar, shiru Danish bai tanka mashi ba saboda wani irin jiri jiri da yake gani a idanun shi



Ru?o hannun shi chief yayi da niyar su fita daga toilet din don Ya duba lafiyar shi, da sauri Danish Ya fuzge hannun shi, dakyar sautin voice dinsa ke fita



"I don't want to see anyone! Just leave me alone! ka tafi kawai..."



"No bazan iya ?yale ka ba, Idan kai baka damu dakanka ba, Ni na damu dakai, Please, Danish, let's go treat your nosebleed."



Girgiza kai Danish yayi"bana so, lafiyata qalou, zan kula da kaina, kawai ka tafi ni bana son ganin ka.. "



"Ni kuma ina son ganinka, ba inda zan tafi, in kaga nabar dakin nan to ka samun sau?in abun da ke damun ka ne" babu wasa a fuskarsa yayi maganar tare da harWe hannayensa kan kirjin shi, kallon kallon suka fara jefawa junan su, chief ya rasa yanda zaiyi da shi, yaron yafiye taurin kai ga kafiya, da ?iwuya kamar yaron goye ...




?wara ya lalla6a shi su wanye lafiya, idan ba haka ba zai iya illata kan shi..



Cikin sigar lallashi Yace"pls Danish, ka bani damar da zan baka kulawa, ba cutar dakai zanyi ba, bana jin dadin ganinka a halin da kake a ciki, na damu dakai Danish, ina jinka tamkar Wan uwana, A shirye nake dana taimaka maka wurin ganin mun shawo kan abunda ke damun ka."



tun da chief ya fara magana cikin sanyin murya, Danish ya nutsu yana sauraron shi kamar yana fahimtar shi.



"Nayi maka al?awarin ba zaka ta6a dana sanin yarda dani ba...." bai ?are maganar ba, raunanniyar muryar danish ta katse mashi hanzarin shi"bazan ta6a yarda dakai ba, ?an uwana kadai na yarda da su, amma ku ba abun yarda bane! duk halin ku Waya, kuna da son zuciya, ba ku da tausayi, Tun ina jariri na taso rayuwata a gidan kurkukun ?addara, bansan komai dangane da duniyarku ba, saboda an tauyemin hakkin rayuwata, ina da ciwon zuciyar abun da iyayena suka aikata min, bansan wani jin dadi na duniya ba, unaisah itace farin cikina......." wasu zafafan hawaye ne suka wanke fuskarshi, zuciyar chief ta karaya, baisan sa'adda hawaye suka cika idanun shi ba, sambatun Danish sun ta6a zuciyar shi, shi kanshi baisan Yana furta kalaman ba, rashin Angel ya fara zautar da shi, dama kuma abun ya jima yana ci mashi tuwo a kwarya.



Da sauri chief Ya ?ara huggin dinshi tighly a kirjin shi, kamar zasu koma mutun Waya, a hankali yake shafa bayanshi da tafukan hannayen shi cikin kwantar da murya ya soma yi mashi raWa a kunanshi



"Danish ba duka muka taru muka zama Waya ba, ina rokon alfarma a wurinka, ka jarabani nayi maka alkawarin zan sanya farin ciki acikin rayuwarka, inaso na samu kusanci dakai, saboda na share maka hawayenka in kuma baka kulawa, bayan haka zanyi kokarin sasanta tsakaninka da ?ar uwarka unaisah duk da bansan meya faru atsakaninku ba"




Cikin sanyin murya ya furta"tayi fushi dani, ta daina sona, nasan ban kyauta mata ba, amma bayin kaina bane, ina so na bata hakuri koda ba zata cigaba da kula ni ba, ni burina ta yafe min kada ta ruke ni a zuciyarta, hukuncin yayi min tsauri bazan iya jure ba...ka taimaka min dan Allah..." a karo na farko da Danish Ya ambaci sunan Allah, ba tare da shi kanshi Ya lura da furucinsa ba, lumshe ido chief yayi, wani irin sanyine ya ratsa zuciyar sa, har lokacin suna a rungume da juna, yaji dadin damar daya samu dama burinshi yaja shi a jikin don su samu abunda suke so, yanzu ya samu mafita, ya riga daya gane lagwonsa wato Unaisah, yayi imanin badan sun samu sa6ani atsakaninsu ba, da bazai ta6a samun damar da har Danish zai kula shi ba, murmushin gefen fuska ya saki aranshi ya furta yanzu wasan zai fara=?%?



"Zan taimaka maka in sha Allah, zanyi iyakar bakin kokarina gurin ganin kun sasanta tsakaninku, amma fa sai ka yi hakuri ka cire damuwa aranka, yanzu muje ayi maka treatment na bleeding dinka"



"Bani bu?ata, zan iya gyara kaina" ya fada tare da raba jikin su daga na juna, ya sanya hannu ya matse hancin shi, nan take jinin ya daina Wiga.



"Inason zanyi wanka" fita chief yayi daga Wakin, ya tsaya a bedroom dinsa Yana jiran shi, tufka da warwara ya fara dangane da yadda zai ja shi a jikin shi , yaso yaji meya faru atsakaninsu sai dai ya fahimci baya son sanar dashi, kamar yadda itama unaisan taki sanar da shi, bai damu da hakan ba, saboda shima baison yaji abun da zai hana shi runtsawa kwara atafi ahaka yana dai kyautata masu zato.



Kafin fitowar Danish Ya kira landline na kitchen Ya isar da sakon Yana bukatar breakfast a kawo mashi a dakin Danish



Within 10 mins chef Ya shigo hannun shi ru?e da tray na kayan abinci har saida gabanshi ya faWi ganin jinin dake agaban jallabiyar chief bai dai tanka ba, tun da ya gaishe shi Ya sauke masu akan table kafin Ya fice daga dakin.



Harya fara gajiya da tsayuwa, jin motsin buWe kofa Yasa shi saurin kai idon gare shi, Ya fito fess dashi kamar wani abu bai ta6a faruwa ba, towel ne Waure a waist dinshi, tun da ya fito chief yake kallon shi, bai ji dadi zanan tatttoo din da akai mashi ba, daga bayan shi har gaban kirjin shi da damtsen hannun shi zanan waWannan halittunne masu zako zakon akaifu, launin ja da ba?i bawai don baiyi mashi kyau ba, hasalima kyau zanan yayi mashi sai dai abun da yake jimawa ranar daya musulunta dole yaji ba dadi saboda haramunne zanan tattoo kuma daga gani permanent ne nashi irin wanda bai gogewa, sau?in shi Waya Idan ya musulunta bashi da zunubin komai.





har saida ya nufi closet kafin chief ya kau da ido daga kallon shi, ?arnin jinin ne Ya fara takura mashi fucewa yayi daga dakin Ya nufi dakin shi, ya canza kayan jikin shi ya sanya wata jallabiyar kafin ya dawo dakin danish.



A zaune ya same shi akan mirror chair ya sanya short da singlet a jikin shi, ya zabga uban tagumi da hannun shi biyu, har yanzu ba yaji shi daidai.



"Danish bismilla, taso muyi breakfast, nasan baka ci komai ba" cikin kulawa yai mashi maganar

In a cool voice Ya furta"bana iya cin komai, Unaisah nakeson gani..." ya yi maganar tare da mikewa Ya nufi kofar fita daga dakin, da sauri chief yasha gabanshi...

"Unaisah bata nan, ko kaje dakin su ba zaka ganta ba"

Hankalin shi atashe ya furta"ta gudu saboda tana fushi dani ko"? Ya fada idanunsa cike tab da kwalla"

Girgiza kai chief yayi"ba abunda kake tunani bane, muje mu zauna I'll explain everything to you.."


Related Books:

Abban Sojoji (Takun Karshe) hausa novels complete - Novels Elite
Daudar Gora complete book 1 Document.
Daudar Gora Book 2 Complete Document
Jiddatul Khair book 1&2 complete


ya ruko hannun shi suka zauna daga gefen gado suna fuskantar junansu..

Calmly chief ya zayyana mashi komai dangane da zuwanta asibiti, bai boye mashi komai ba ...." bawan Allah har cikin ranshi yaji dadi da unaisah ta haWu da mamanta, sai dai yana jin tsoron ta juya mashi baya tun da ta samu iyayen ta..."



"Angel dina taga mamanta"? Jinjina mashi kai chief yayi,

"Kaima in sha Allah iyayenka zasu bayyana kuma zasu baka farin cikin daka rasa arayuwarka ..." yanayin fuskarshi ne Ya canza zuwa tsantsar 6acin rai.



"Bana son su, bani bukatarsu, bana son ganin su, na tsane su, ni bani da iyaye, unaisah ce gatana" murmushi chief yayi.



"Baka tunanin kaima iyayenka suna kaunarka? Think about it. zai iya yiwuwa wani ne a danginka ya sadaukar dakai ba iyayenka ba, kai da kanka kace tun kana jinjiri aka sadaukar dakai, watakil iyayenka basu san an sace masu kai ba, don ni gaskiya bana tunanin a duniyar nan za'a samu iyayen da zasu haifi kyakkyawan yaro kamar kai su suyi watsi da shi...." shiru Danish yayi baice mashi komai ba, kamar yana nazarin maganar shi, sai dai babu alamun zai fahimce shi.



Cikin dabara chief yacigaba da kwantar mashi da hankali, har ya samu suka ci abinci atare, bayan yayi mashi alkawarin zai kai shi wurin Unaisah amma ya bashi shawarar ya Wan bata tazara watakil ta sauko daga kan dokin zuciyar da tahau...yace mashi bazai iya ba, baya jin dadi in bata atare da shi, yafi son yaganta akusa dashi ko da bazata kula shi ba.. Akarshe yace mashi da anjima zai kai shi wurinta suga juna in har hankalin shi zai kwanta....



Lokacin da su Batool suka farka har yar rige rigen zuwa dakin unaisah su kayi don suga kota dawo amma suna shiga suka iske babu kowa, Hankalin su ba ?aramin tashi yayi ba, wasu har sun fara kuka, saida Ummi ta sauko down ta same su zazzaune kan sofas kowannansu Ya zabga uban tagumi kamar masu zaman makoki.



Suna ganin ummi suka nufe ta"aunty ummi har yanzu yar uwarmu bata dawo ba, dan Allah ina taje ne bata fada mana ba"?

Kwantar masu da hankali tayi kafin


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login