Showing 174001 words to 177000 words out of 391264 words

Chapter 59 - Cigaban Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel

11 Feb 2025

2658

ce, tazo duba jikin benazir ne"

A ruWe tace"meke damuntane? Ke zeenatu ya akai? Ko bakison zuwane aka matsa maki? Muryarta kasa kasa ta furta"bana jin dadin jikina..."

"Haba shureim kasan bata da lafiya ka taso ta? Ko likita kukazo gani ne"?

"A'a mami, lafiyarta qalou, zanyi maki bayanin abunda ke damun ta, mu shiga daga ciki....."



___________________________________
'?



A lokacin Unaisah tana zaune kan chair din gaban gadon Benazir, hannun ta ruke da glass na ruwa, magani take bata in ta sanya abaki saita bata ruwan ta sha, ta maida kanta kamar ?aramar yarinya agaban unaisah, har yanzu bata daina binta da kallon kurullan ba...

"Mommy ki maida hankali kan ruwan da kike sha, kada ki shake" murmushi taskar mata"bana gajiya da kallon ki ne, Kin sace min zuciyata" da mamaki unaisah take kallonta, kalaman matar suna sanyata kokwanton kamar ta dawo hayyacin ta

Shigowarsu dr shureim dakinne Yaja hankulansu ga kallon kofar,

"Benazir yau Allah yayi, zeenatu tazo dubaki, sai dai kamar bata jin dadin jikin ta,..." da wani irin yanayi benazir ke kallon zeenatu wadda ta 6oye fuskarta jikin shureim...cikin sanyin murya ta furta"Zeenatu...."! shiru bata amsa mata ba, Unaisah dai ta zuba ido tana kallon matashiyar dake kankame da shurem, jikinta sai kerma yakeyi kuma ta?i dago da fuskarta...

"Zeenatu bakiga auntyn naki ba"? In a low voice ta furta"bana son ganinta" waro ido waje benazir tayi sam ta manta da pretending din da takeyi saboda ruWewar da tayi, lamarin ya daure masu kai, arude hajiya layla ta kalli shureim suka hada ido, unaisah dake kallon su abun ya bata mamaki aranta ta ayyana kowacece wannan take ta wani boye fuskarta? Yanzu haka bawani kyan kirki gareta ba, in banda wulakanci hada wani cewa bata son ganin mamanta, yanzu haka yar kishiya ce... Acikin zuciyarta take wannan sambatu

Banezir kuwa jikinta yayi sanyi lakwas zuciyarta ta karaya da jin kalmar da zeenatu ta furta abun Ya girgizata sam takasa magana sai motsa la66anta take

"Pls kada hakan Ya dame ku, bayin kanta bane, Ina tunanin iska ne suka shiga jikin ta..." calmly ya zayyana masu komai dangane da abun da ya faru ranar farko da ya koma gida har yayi mata maganar benazir ta share shi, har zuwa ga abunda ya faru yau, mami ta tafa hannu tana ambaton "inna lillahi wa'inna ilaihirraji'in zeenatu Allah ya baki lafiya, Allah ya yaye maki abunda ke damunki, baiwar Allah ashe shiyasa tadaina zuwa asibitin, sannu zeenatu ta faWa tana le?en fuskarta, banza tayi da ita, benazir dai takasa magana kallon su kawai takeyi, ita dai unaisah ta baza kunne tana sauraron su bakomai ya bata haushi ba face Yarinyar da take ta boye fuska.



"Yaya shureim ka maidani gida! Kada daddy ya dawo ya iske bana nan!..."

Cikin kwantar da murya yace"ko ya dawo ba abunda zaiyi maki, ai ni na fito dake, da anjima zan maidaki, mu karasa ciki ki zauna..." yai maganar yana kokarin janyota cikin dakin, aikuwa ta turje tana yan fizge fuzge Hankali atashe mami tace"shureim abun da ban tsorofa kamar ba zeenatu ba, pls ka maida ita gida, tunda ta nuna bata son zama nan din..

Shi dai baison Ya maida ta gida saboda bai shirya komawa ba

"Mami babu kowa gidan, ita da kanta ta nuna batason zama ita kadai shiyasa na taho da ita..." ya fada fuskarshi ayamutse...

Saukowa Benazir tayi daga kan gadon ta tsaya agabansu cikin karyayyar murya ta furta"zeenatu! dagaske bakison gani na"? da wata irin tsiwa ta furta"Bana son ganin ki, ki daina yi min magana...." kafin ta ?are maganar, Benazir takai hannu ta dam?i shoulder dinta dakyar ta rabata daga jikin dr shureim ta jijjigata da karfi har mayafin daya rufe fuskarta ya zame kan kafaWarta....



Kamar daga sama sukaji Sautin fashewar glass kusan atare suka kai dubansu ga Unaisah wadda ta mi?e a sukwane tana faman zazzare idanun ta, tsantsar tashin hankali da rudani ne akan fuskarta

"Azeezaty meya faru...." hada baki sukayi wurin tambayar ta, la66anta sai kerma sukeyi gaba Waya ta rikice ta kasa magana, gabanta na faduwa ta nufi zeenatu wadda ke ta kerma tana zare blue eyes dinta akan fuskar Unaisah



Wani irin gumi ne ya wanke fuskar Angel duk da sanyin A.c din dake a dakin, ta sanya tafukanta ta murza idanunta saboda tana kokwanton ko dai gizau takeyi mata ne? In ba haka ba tayaya mutumin daya mutu zai dawo araye? Ta kasa yarda da abunda idanunta ke nuna mata, kusan sau uku tana murza su don su dawo dai dai, Hankulan su dr shureim na akanta, sun rasa gane meke damun ta! Ko dai tasan zeenatu ne? Meyasa ta razana da ganin zeenatu harta fasa water glass din hannun ta! Dukansu kansu ya daure

Agaban zeenatu ta tsaya suka fuskanci juna, ido cikin ido, dafe kai unaisah tayi da hannayenta biyu saboda wani irin sara mata da yayi, zuciyarta ta fara dakan uku uku, Muryarta adabarbace ta furta*"UNAIZAW'S'*

*Daga Alkamin Boss Bature=?%?
'?*

*Ga me bukatar karanta littafin kurkukun kaddara, 500 ne za'a tura Via Opay, 8103884440 Hafsat Bature Muhammad, shaidar biya za'a tura ta whatsapp, 08103884440*

Sponsored Post
Tags
Kurkukun Kaddara
YOU MIGHT LIKE
POST A COMMENT
Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.


Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
Facebook
twitter
YouTube
Instagram
Whatsapp
SUBSCRIBE US

OPINION
FACEBOOK
COMMENTS
CATEGORIES
Africa
(1)
Al'adu
(1)
Alkamawa
(3)
Article
(3)
Blogger Tips
(1)
Economy
(5)
Education
(2)
Entertainment Gist
(1)
Gyaran-Jiki
(5)
Health
(13)
Jikar Iya
(11)
Kimiya
(1)
Kiwon Lafiya
(54)
Kukan Zuci
(5)
Kwalliya
(4)
Labaru
(23)
Lifestyle
(1)
Ma'aurata
(1)
News
(300)
Nigeria
(5)
Noma
(1)
Opinion
(3)
Picture
(3)
Politics
(15)
Profile
(2)
Q&A
(1)
Ramadan
(9)
Ramadan Tafsair
(1)
Siyasa
(1)
Sports
(72)
Tarihi
(5)
Technology
(1)
Tips
(3)
Video
(3)
YouTube
(5)
Zain Abeed
(1)
Zamantakewa
(1)
Novels Elite
Get the Most Exciting News and Read Your Favorite Hausa Novels. Let us be your source for exciting news reports worldwide, as well as access to a wide variety of blogs and blogging tools. We also offer novels in different languages including Hausa so you can easily read what interests you! Plus with our Google Adsense partner program, monetize when readers engage with your content.

Novels Elite
SUBSCRIBE
Posts
Comments
Links
Post a Job

LATEST POSTS

ADVERT
Novels Elite
Copyright ? 2024 Novels Elite | All Rights Reserved
DMCA.com Protection Status
Disclaimer |
Privacy Policy |
Terms and Conditions
[14/10, 6:05 PM]  Amin@ M Yusuf Yol@: Novels Elite
Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun ?addara Takun ?arshe page 35 Complete
by
Novels Elite Admin
August 31, 2024
Sponsored Link
Takun ?arshe

DAGA AL?ALAMIN BOSS BATURE
'?=؋?
'=?%?
Agaban Zeenatu ta tsaya suka fuskanci juna, ido cikin ido, dafe kai Unaisah ta yi da hannayenta biyu saboda wani irin sara matan da yayi, zuciyarta ta fara dakan uku uku, Muryarta adabarbace ta furta"UNAIZAW'S'

Arude Hajiya Layla ta maimaita sunan Unaisah

Dr Shureim yace"wacece Unaizah"? Cike da fargaba Unaisah ta nuna Zeenatu da yatsan ta"ita ce, Yar uwarmu Unaizah...." gaba daya ta rikita lissafin ?wa?walwarsu, Zeenatu da ta gama ruWewa idanunta Azazzare ta furta"bani bace! Ni bansan ki ba, ban ta6a ganin ki ba. ..." Sautin muryar Zeenatu ya ?ara rikirkita ta, runtse idanunta tayi brain Winta ta fara tariyo mata muryar Unaizah idan tana magana! Tabbas wannan Unaiza ce ta dawo...."



fashewa tayi da kuka ta cakumi hannayen zeenatu"wallahi ke ce, Unaizah din mu, yar uwarmu wadda ta rasu tayaya akai kika rayu bayan kin mutu ..."? Tashin hankalin da ba'a saka mashi rana.



Al'amarin yayi matu?ar Waure masu kai, Hankali atashe Benazir ta furta"babyna wacece Unaiza? Shiru Angel ta yi hawaye na sintiri kan fuskarta...

Dr shureim yace"kodai tayi maki kama da yar uwarki ne? Ita wannan sunan ta Zeenatu ba Unaizah ba, bayan haka naji kin ambaci yar uwarku wadda ta mutu in banda abunki wanda ya mutu ay baya dawowa watakil sunyi maki kamane...." kalaman dr Shureim Sunyi tasiri a cikin zuciyarta, amma taya haka zai yiwu? Komai nasu iri Waya kamar mutun Waya! farar fatarsu, da launin idanunsu blue, hatta blonde hair dinsu iri Waya, bugu da ?ari surar jikin su, tun daga kan sirantakar su har big boobs din iri Waya.



Gaba Waya ta jefa kanta aruWani, su Benazir sun kafe ta ido suna kallonta,

Kokwanto ta fara yi kodai gizau fuskar Unaizah takeyi mata akan fuskar yarinyar? Nan take tayi believing da abun da zuciyar ta ke fada mata saboda tasan ba mai yiwuwa bane, wanda ya mutu ya dawo, abu Wayane zaisa ta yarda da abun da idanunta suka gane mata, wanda bakomai bane face ?an uwanta suga yarinyar nan! muddin suka ruWe suka ambaci sunan ta da unaizah to anan ne zata gasgata abunda idanunta suka gane mata...."



Lokaci Waya ta sauke ajiyar zuciya, sam takasa janye idanunta daga kallon fuskar Zeenatu, A hankali ta kau da idonta tare da kallon su shureim wata irin kunyarsu ce ta kama ta, muryarta na rawa ta furta"dan Allah, ku yi hakuri, na ruWe ne, wallahi tayi min kama da wata dana sani, amma ita tama mutu tun da jimawa...." nannauyar ajiyar zuciya suka sauke, har suna hada baki wurin furta"Allah yaji?anta da rahama.."



Yawu Unaisah ta haWiya mai zafi a makoshin ta, kafin ta sake kallon Zeenatu dake kallon ta"sister kiyi hakuri dan Allah, na tada maki hankalin ki, kuskuren fahimtane...." murmushi zeenatu ta sakar mata, su kansu saida sukayi mamakin murmushin da tayi ma Unaisah

Cikin sanyin murya ta ce"Kada ki damu, babu komai...." mi?a mata hannu Angel tayi don su gaisa, da sauri zeenatu ta zira hannunta acikin nata sukayi musabaha, yau ne karo na farko da suka fara sanin junansu amma ga dukkan alamu sun kamu da kaunar juna, tabbas da ace lokacin da aka kawo masu Unaiza ta fada mata twins ne su wlh da ba abunda zai hana ta dafe alkur'ani tayi rantsuwar wannan Yarinyar Twin sister din Unaizah ce!! Ta dai bar abun aranta har zuwa lokacin da Allah zaisa ta hadu da su Batool sune zasu kara tabbatar mata da abunda take zargi na kamannin ZEENATU da UNAIZAH.........=ؔ?.



Kafin wani ya ?ara furta kalma a cikin su, wayar shureim ta fara ringing, a hanzarce ya curo wayar daga aljihu yai picking call Win



"Shureim! Ka dawo da zeenatu gida, Ina jiran ka" rass yaji gaban shi ya faWi, tun daga kan yanayin muryar Alhaji musa ya fahimci ba lafiya, ko jiran amsar shi baiyi ba ya katse kiran.



"Wanene Ya kira"? Hajiya layla ta fada tana kallon fuskarshi



"Uncle ne, Yace in maida zeenatu gida"



Ta6e baki hajiya layla tayi ba tare da tace komai ba



Har lokacin Zeenatu bata cire hannun ta daga na Unaisah ba, sun ?urawa juna ido kowa da abun da yake sa?awa aranshi......



"Muje zeenatu" muryarshi ce ta katse shirun nasu, sallama yayi masu hajiya layla, ya ru?o hannun zeenatu suka tafi, Unaisah bata daina kallon su ba, har le?en su tayi abakin kofar dakin itama zeenatun suna tafiya tana waiwayon ta hada Waga mata hannu tayi mata bye bye...=ؔ?



*CHIEF OWAIS=?%?
'*

Slowly dankareriyar motar shi ta kunno kai cikin villa dinsa, yana daga zaune ya hakimce a backseat, su biyu ne a mazaunin baya big guy dake a gefen sa, kowan nansu kaki ne a jikin shi, da alama sun kwaso gajiyar aiki duba da yadda kowan nan su ya lumshe idanun shi kamar masu jin bacci.. .. bayan sun karasa parking space agent din dake driving nasu yayi parking

A hanzarce Wani agent daga cikin jami'an dake kai komo a harabar ya karaso ya buWe masu murfin motar.



"Sir, mu shiga daga ciki" ya faWa yana le?en fuskar shi yayi shiru, soft lips dinsa sun bushe sun Wan ciza kalarsu pink kamar bazai motsa ba, big guy yayi tsammanin bacci yakeyi hakan yasa shi kai hannu ya dafa shoulder din shi, da wata irin kasala ya buWe reddish eye dinsa tare da kallon big guy



"Mun ?araso gida, nayi tsammanin bacci kake yi.." yamutsa fuskar shi yayi, da zolaya big guy yace"ka bani dama in goya ka mana.." harara chief ya jefa mashi tare da zura kafar shi ya fito daga motar, da sauri jami'an dake a wurin suka buga kafa tare da sarah mashi, ko ta kansu baibi ba ya nufi cikin gidan, big guy yana abiye da bayan shi....



Har ya kusa shiga main falo, wayarsa ta fara ringing, gajiya ta hana ya dauki wayar, kaitsaye ya nufi upstairs Yana shiga daki, Ya rage kayan jikin shi ya fada toilet....

Ganin ya shiga ciki yasa big guy yin kwana ya fita daga dakin..

After some mins, ya fito daga wanka waist dinsa a Waure da towel ya nufi walk-in closet dinsa ya shirya kanshi cikin hanley shirt tare da black trouser na shan iska..





Bakomai yake son gani ba face Danish, Yau da tunanin shi ya wuni a office, Yaron ne ya tsaya mashi arai, baisan meyasa yake jin shi sosai acikin ranshi....





Yana ?o?arin zama gefen gadonsa, phone dinsa ta fara ringing sai time din ya tuna da kiran da akayi mashi dazu



?aukar wayar yayi daga kan pillow Ya duba sunan mai kiran nashi

Yayi mamakin ganin kiran ta! saboda basu cika yin waya ba...daidaita nutsuwarshi yayi kafin yai picking ya kara wayar a kunne tare da yi mata sallama ya gaishe da ita cikin girmamawa.



On the other hand muryar sheikha mujeedat ta amsa mashi sallamar shi cike da dattako ta fara yi mashi magana cikin harshen turanci tana hadawa da arabi



"My in-law, did you see the message I sent you on WhatsApp"!



"I just got back from work, ban kaiga dubawa ba..."



"Okay, ka duba yanzu, ina so zamuyi magana dakai" amsa mata yai da toh ta katse kiran..



Zama yayi gefen gadon kafin ya shiga whatsapp dinsa, kaitsaye idanunsa suka sauka akan sakon gimbiya mujeedat, calmly ya fara karanta abun da ta turo ma shi



_*DNA Paternity Test Report* _



A tsanake yake bin bayanan da result din ya kunsa har yakai karshen sakamakon



_"DNA Profile Match: 99.99%. Paternity Index: 100,000,000:1 (extremely high probability). Conclusion: The DNA analysis conclusively confirms that Danish is the biological son of Sheikha Mujeedat bin khalid AlMaktoum._



Lokaci Waya chief ya zabura ya mi?e jikinshi na tsuma, tsantsar ruWani da al'ajabine akan fuskarshi, A kalla ya maimaita karanta sakon yafi sau ashirin kamar irin bai fahimci me aka rubuta ba saboda tsabar kiWima da mamaki! Tayaya haka zai yiwu? wai ma Wani Danish din ne? Na wurin shi da yake ru?o ko wani ne daban"?



Gaba Waya ya ruWe tayaya ma akai gimbiya mujeedat tayi DNA test din? A yaushe? kuma daga ganin result din original ne daga babban asibitin toronto"



Wahallan Yawu ya hadiya da sauri yai scrolling ya shiga contact ya buga mata call yana faman fitar da numfashi mai Wumi.



Kiran na shiga Gimbiya Mujeedat ta Waga..." la66ansa na kerma ya furta"mommy, ki yi min bayani, ki fahimtar dani! Na gaza yarda da abun da nagani I can't believe! I was confused, is this DNA test true? ya fada hankali atashe.



Sanyayyar muryar gimbiya Mujeedat ce ta ratsa kunnanshi



"Owais, kamar yarda hankalinka Ya tashi ka shiga rudani, nima haka na shiga, zanma iya cewa fiye da yadda ka shiga! Owais tun arana ta farko danayi tozali da yaron nan naji a jikina Wana ne! Jini na ne shi, duk da bani da tabbaci But what strengthened my suspicions is the unconditional love Hateem has for him"



Shiru ta Wanyi kafin taci gaba da cewa" na san zakayi mamakin tayaya akai nayi gwajin!" bayani ta fara kora mashi dangane da yadda ta yanki gashin danish batare da sanin shi ba.



jikin chief yayi mugin yin sanyi kamar wanda aka zarewa laka, gaba Waya yasha jinin jikin shi, ya girgiza bilhakki..."



"My trusted doctor conducted the test. When the results came out, I was shocked, wlh har zazzabi nayi owais..." muryarta na rawa ta ?are maganar cikin rauni na murya



"Owais ka fadamin me kake tunani akan yaron? Kaima kana zargin jininmu ne"?



Numfasawa chief owais yayi wata juwace ta nemi daukar shi da sauri ya koma ya zauna, yana faman jan numfashi sam ya kasa bata amsar tambayar ta, abunne ya rikirkita shi.


??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????
"Owais naji kayi shiru bakace komai ba! Ni raina yana bani Omair dinmune, jinjirin dana haifa ba araye ba, amma in shine tayaya zamu iya gano gaskiyar lamarin? ni dama tun time din dana haifi yaron hankalina baikwanta da yadda aka hana mu ganin koda gawarsa ba, na dade da radadin abun a zuciya ta..."dakyar chief ya samu kwarin gwiwar furta"kin fadama uncle sakamakon DNA test din"?



"Ban fada masa ba, saboda bana so in daga mashi hankalin.." jinjina kanshi yai kafin ya furta"bazan boye maki ba, tunaninmu yazo Waya, nima ina zargin babyn da kika haifa ne! Amma har yanzu bamu da ?wa??waran hujjar da zamu tabbatar da hasashenmu in gaskiyane! Dole saimun fara yin bincike mun gano tayaya akai jinjirin daya mutu ya rayu! Sannan su wanene suka sace shi daga asibitin da abun ya faruS'



"yanzu muna da shaida Waya a hannu, ki ajiye result din dakyau, kibar komai a hannuna nayi maki alkawarin zan binciko komai, in har yaron nan Wankune zai dawo gare ku in sha Allah, sannan pls mommy kada ki bari uncle yaga result din nan..." ta amsa mashi da toh, kwantar mata da hankali yaci gaba da yi, daga bisani su ka yi sallama.



Shiru yayi jim yana tunani! idan har ya tabbata dan uncle dinsa ne to wanene ya sadaukar da shi? Yana jin fargaban ace hateem dinne ko wani daga cikin uncles dinsa tun da sadaukarwar na jininka ne kadai zai iya bada kai. W'



Yana jin fargaban ranar da zai gano koma wanene! A sukwane ya fito ya nufi bedroom din Danish saboda ya yi maraicin ganin shi ya ?ara jin ?aunar yaron a zuciyar shi fiye da kullum



Baijima da fita ba, sai ga big guy ya hauro up hannun shi ruke da wooden tray na kayan abinci, knocking kofar yayi jin shiru ba'a bude ba yasa shi tunanin koya yi bacci ne ko yana toilet

Yanke shawarar shiga ciki yayi, ya danna code din kofar ta bude kafin ya shiga da kayan abincin.



A bakin door room din Danish ya tsaya tare dakai hannu yayi knocking almost 3 times ba'a buWe mashi ba, baya jin zai iya juyawa batare daya sanya shi a cikin idanun shi ba.



Tura kofar yayi tare da sakai ya shiga da sallama, yana zura ?afar shi ya fara cin karo da papers din da ya kacaccala ya kekketasu akan floor, murmushi chief yayi aranshi ya furta hmm dakin Wan koyo.



Ya yi ma bedroom din nashi kaca kaca, kamar ance ya Wago da idon shi karaf Ya hango zanen da yayi akan white board din da yake koya mashi rubutu da shi, wata halitta ya zana kamar jagwalgwalo daya ?ura ido saiya gane maca ce, yar diyar roba da


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login