Showing 219001 words to 222000 words out of 391264 words

Chapter 74 - Cigaban Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel

11 Feb 2025

2651

da abun da yake sakawa aran shi, musamman Benazir ta kosa ta ga taj da Angel dinta murmushi kawai take saki ita kadai tasan dadin da take ji



"Bani junaid din in ruke maki shi" mi?a mata shi anila tayi bayan Benazir ta kar6e shi ta rungume a kirjin ta, Jami'an dake kai komo sai kallon su suke yi.



"Ina zamu nufa"? Benazir ta fada tana kallon Anila, tayi shiru saboda batasan ina zasu dosa ba, har ta yanke shawarar kiran Taj, kwatsam Horn din mota Ya karaWe kunnuwan su, kusan atare suka dubi hadaddiyar motar dake tunkaro kirar black Mercedes





Agaban su motar tayi parking, sun ?ura ido suna jiran ganin wanene mamallakin ta.



Ta ciki aka buWe car door din, gently ya fito daga ciki gaba daya suka bi shi da ido, yana sanye da kayan kakinsu na isod ya rufe fuskan shi da mask, zagayawa yai ta other side Win motar ya buWe murfin, slowly chief ya fito daga cikin, hannun shi ru?e da wayar shi, fuskarshi sanye da face mask, gaba daya dr shureim Ya kasa dauke ido daga kallon su, musamman Benazir gabanta har faduwa yakeyi gani take kamar taj ne sai dai takasa gasgata hasashenta saboda face mask din dake akan fuskar shi yasa ta kokwanton anya shi ne? sai kallonshi take yi shi kuwa ya haWe fuska yama ki yarda su haWa ido da juna don kada ta samu sararin da zata gane shi ne, Hankalin Anila ba karamin kwanciya yayi ba, aranta ta ayyana ashe ma suna atare da chief din tasan already ya fada mashi kwa6ar da tayi masu, fatanta Allah yasa kada ya tuhumeta.



Cikin girmamawa Anila ta gashe da su, chief ya amsa mata, dr shureim Ya mika masu hannu sukayi musaba a mutunce suka gaisa da juna.



Anila ta lura da taj, dama tasan za'a rina, ita ta gane shine kuma tasan saboda Benazir ya sanya face mask, sannan yaki tanka masu don kada taji muryar shi.





"Ya jikin naki" muryar chief ce ta katse mata zancen zucin nata, da sauri ta kalle shi har saida taji gabanta ya fadi, kwata kwata bata kalli fuskar shi ba, sai da yayi mata magana, ta so ta ruWe sai taji kamar muryar Zaki.



jin tay shiru bata amsa ba yasa Aneelerh tayi saurin ce mashi"jikinta da sauki, Alhamdulillah" A hankali ya dubi taj sarai ya fahimci dagangan ya?i magana saboda ex-wife dinsa, ita kuma baiwar Allah ta tsareshi da ido saboda ta gane shi ne.."

"Bismilla..." ya fada tare da nuna masu walkway din da zasu bi



Gaba yai tare da taj su Aneelerh suka bi bayansu, baiwar Allah Benazir ta zama kamar mutun mutumi, jikinta duk yai sanyi la?was cikin muryar raWa tace ma anila"taj ne ko"? Jinjina mata kai anila tayi" shine amma kiyi hakuri dan Allah, kada ki sanya damuwa aranki, har yanzu yana akan dokin zuciya ki bashi lokaci nasan zai kula ki." hawaye ne suka cicciko idanunta, ganin shi da tayi ya fama mata ciwon son shi dake a cikin zuciyarta.





Gaba Waya ya canza mata, ba kamar taj din da ta sani bane ada, Ya zama babban mutun dashi, ga kyawun sura da cikar kamala, har wani ?warjini yayi mata, lallai da da yanzu ba Waya ba, cos ba zata taba manta yadda ta azabtar da shi da soyayyarta ba, ta gasa mashi aya hannu, ta raina shi kamar bawanta haka take sarrafa shi sai abunda taga dama akeyi agidan su, yanzu kuwa taj yafi karfinta, ita kanta ta shaida hakan, dr shureim dake abiye da su kwata kwata bai lura da halin da Benazir take a ciki ba, hankalin shi baya akan su



abakin wata glass door suka dakata da yin tafiyar, Chief ya buWe masu kofar, Sanyin a c ne ya fara busowa ta cikin Wakin mai dadin gaske, atare chief da taj suka shiga, Benazir da Aneelarh suka shiga daga bayansu kafin dr shureim ya shigo, sitting room ne Ya gaji da haduwa, a saman sofas suka zauna, anila da benazir da dr shureim suna akan sofa mai mazaunin mutun uku, yayin da chief da taj suke a zaune kan 2 seater dake fuskantar su.



Mi?ewa taj yai ya nufi benazir, tayi azan zaiyi mata magana ne harta fara dan sakin murmushi bai ko kula ta ba, ya sanya hannu ya kar6i junaid daga hannunta, Ya koma ya zauna tare da kwantar da shi kan kirjin shi.



Da ido Aneelah tayi mata alamar tayi hakuri ta kwantar da hankalin ta, dukar da kanta kasa tay tamkar zata sanya kuka ba dan bata so dr shureim ya gane gaskiya ba ai da tuni ta cakumi rigar taj ta rungune shi.



Takun tafiya ne Yaja hankulan su ga duban mai shigowa, wani jenior agent ne Ya shigo hannun shi ru?e da wooden tray mai Wauke da softdrinks and snacks ya ajiye masu akan table kafin ya juya ya fuce



"Bismillah, zaku iya sha" Taj ne ya fada tare da yi masu nuna da table din, Anila ta Wauki juice ta zuba masu a cups ta mi?a ma dr shureim ya kar6a, koda ta mika ma Benazir girgiza mata kai tay alamar a'a, jiki asanyaye Anila ta fara shan wanda ta zuba mata.



falon yayi tsit baka jin sautin komai sai sanyin a.c din dake ratsa fatar jikin su.



Gaba daya hankalin benazir na akan taj, Ta kasa janye idanunta daga kallon fuskar shi, so take ya Wago su hada ido ya?i yarda, sai ma Ya maida hankalin shi akan junaid dake rungume a kirjin shi, a hankali yake shafa sumar kan shi da hannun shi, son yaron yake kamar yadda yake son Angel dinsa.





"Dan Allah kuyi min bayani wanene daddyn Azeezaty a cikin ku? ina son nasan shi" dr shureim ne ya katse masu shirun nasu.



Da hannu chief ya nuna mashi taj,

murmushi dr shureim yayi"Allah sarki, dama inaso ne in ?ara yi maku godiya, wallahi munji dadin taimakon da kukayi mana, Allah ya saka maku da alkhairi..." atare suka amsa mashi da ameen.



"Daddyn Azeezaty, Ina tayaka murna, ka ?ara gode ma Allah daya baka yarinya mai hankali irin na manya, ga kaifin basira gata da saurin shiga rai" murmushi taj yai har cikin ranshi yaji dadin yabon da shureim yayi ma angel dinsa"thank you so much," ya faWa yana mai nuna jin dadin shi.



"You should call her" chief ne ya faWa tare da mikewa Ya nufi hanyar fita daga dakin.



Curo waya yai daga aljihun kakinsa Ya kira layin Unaisah



Bayan ta Waga yace"daughter kina ina ne"?



On the other hand tace"ina adakin mu" Wagowa yai tare da kallon su anila, gaba daya hankalinsu na akanshi.



Kwantar da baby junaid yai kan sofa, yai ma anila nuna da hannu da sauri ta mike taje ta dauki baby junaid ta rungume a jikinta.



Mi?ewa taj yayi ya nufi bakin kofar dakin ya tsaya saboda baison su ji abun da zasu tattauna, muryar shi kasa kasa ya ci gaba da yi mata magana



"Auntynki tazo tana son ganinki" yana juyo sautin ihun farin cikin data saki

"Daddy, atare da baby junaid tazo"?

"Eh, harma da aunty Benazir dinki,"



"Wayyo Allahna, gani nan zuwa daddy" da sauri yace"ban gama magana ba" nutsuwa tayi tana sauraron shi



"Ina yan uwanki suke"?



"Suna a falo"



"Okay, bana son kizo da kowa, ke kaWai zaki zo..."



"Amma daddy suna son ganin baby junaid, na riga na fada masu mun hadu da aunty anila kuma sun kwallafa rai da son ganin ta"



"Look, kija baki kiyi shiru, kada ki fada masu game da zuwanta, kin riga da kinsan komai ba sai nayi maki bayani ba, idan har yaran nan suka zo zasu iya furta wata kalma da zaisa agane wani abu game daku, kuma hakan ya sa6ama dokar aikin mu, shiyasa nace kizo ke kadai, ke ma din dakyar na samu chief ya amince su ganki, Ina fata kin fahimce ni"? Shiru tayi da alama bata ji dadi ba





Fahimtar yanayin ta yasa shi sassauta muryar shi"Idan ki ka kwantar da hankalin ki, next time zasu sake dawowa ne in yaso sai su hadu da su"



ajiyar zuciya ta sauke"toh daddy, na fahimce ka, amma ya zanyi da batool? Ta riga da taji komai, namanta tana adakin, dan Allah daddy kabari in zo da ita"



shiru yayi baice mata komai ba





"Daddy, naji kayi shiru, pls ita kadai, batool ba zata bamu matsala ba, tana da hankali, zan ja mata kunne akan kada ta furta komai da zaisa su san wani abu dangane da rayuwar mu, nasan zata fahince ni"



Numfasawa yai kafin yace"ya zanyi dake tunda kin matsa akan son zuwa da ita, kuzo amma kinsan Allah idan aka samu matsala ki kuka da kanki" ya fada da zolaya, dariya tayi"ba abunda zai faru in sha Alah"



"Okay," ya fada tare da yi mata kwatancen inda sitting room din yake.



"Pls kada ku dauki lokaci, suna jiranku" cike da zumudi ta amsa mashi da toh, katse kiran yai tare da juyawa ya dubi su dr shureim sunyi shiru suna jiran tsammani, kallon benazir yayi ta kifa kanta kan sofa hand, idan yace baiyi kewarta ba yayi karya, almost 17yrs rabon shi da ita, ta canza mashi ba kaWan ba, ya danyi mamakin girmanta, ta zama babbar mace ba kamar lokacin daya aureta ba, yar siririya da ita sai rashin kunya cike da kai, daurewa kawai ya ke yi ba ya san ta gane ya yi kewarta yafi so ta WanWani irin Wacin da ya ji aran shi na irin bakin cikin da ta kunsa mashi, Abun Ya ta6a zuciyar shi ba kaWan ba, ?wara itama taji ajikinta kamar yadda yaji, batare da sanin su ba, Ya fuce daga sitting room din Ya koma waje Ya tsaya zuciyar shi cike fal da tunaninta, Allah sarki tsohuwar zuma, yajima yana tambayar kanshi meyasa zatay mashi haka? Laifin me yayi mata? bai ta6a tsammanin tsanar da tayi mashi takai harta haifa mashi jinjira ta ajiye acikin kwamin wanka ta gudu tabar su, kusan shekara goma sha bakwai, bata ta6a waiwayarsu ba, taya zai iya yafe mata cikin sau?i? Idanunshi ne suka ciko tab da kwalla, da sauri ya jingina kanshi jikin bango, Allah kadai yasan radadin da yake ji acan kasan zuciyar shi,

Maganar anila ya fara tariyowa inda take ce mashi bafa yin kanta bane, shiga akayi tsakaninsu, bada son ranta ta gudu ba, har yanzu tana son su, girgiza kai yai cikin karyayyar murya ya furta"ban yarda ba, nasan wacece Benazir, zata iya aikata fiye da haka ma, dama ba sona takeyi ba..." shi kadai yake sambatun shi abunne ya dame shi.



"Har yanzu shiru basu ?araso ba, ko dai Azeezatyn tana a school ne"? Dr shureim ne yayi maganar

Anila tace"nima nayi tunanin hakan, watakil sai an daukota daga school, mu dan kara hakuri" ta fada tare da kallon Benazir da ta langwa6e kai jikin sofa, ta lumshe idanunta... Tsantsar tausayinta ne ya kamata, dr shureim yayi tunanin saboda azeezaty ta shiga halin damuwa hakan yasa shi yi mata gyaran murya ta buWe ido ta kalle shi"meke damunki ne? Tun da muka shigo na lura da yanayinki! Nasan bai wuci saboda azeezaty bane ko"! Murmushin ya?e ta sakar mashi cikin sanyin murya tace"kamar ka sani ya shureim,
wlh na ?agara da in ganta, kamar zan zauce" yar dariya yayi tare da mi?a hannu kan table din gaban sofa din, Ya dauki juice Ya zuba a cup, yana kokarin kaiwa bakinsa Ya Wan dakata Yana sauraron muryoyin da kunnuwanshi suke jiyo mashi



"Mu je ciki mana"

"Dan Allah ki fara shiga, ni wallahi kunya nake ji,"

"Meye abun kunya a ciki, Aunty Anila ce fa, tare da aunty Benazir, ni ki wuce mu shiga..."

Kusan atare Anila da Benazir suka dubi ?ofar sitting room din, su biyu ne Waya ta rurru?e Wayar da ta turje akan ba zata shiga ba, Kamar zasu yi dambe, kwata kwata basu ga fuskokin su ba, Ita Batool mayafin da ta yi rolling akanta ne ya warware ya rufe fuskarta, sakamakon ingizatan da unaisah takeyi, Yayin da ita kuma Unaisah take abayanta tana kokarin tursasa mata akan ta shiga, murmushi Anila da benazir suka saki suna kallon ikon Allah

Cikin sanyin murya dr shureim Ya furta"Ki bi ta a hankali pls, kada ki ja ta fadi taji ciwo"


Sponsored Post
Tags
Kurkukun Kaddara
YOU MIGHT LIKE
POST A COMMENT
Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.


Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
Facebook
twitter
YouTube
Instagram
Whatsapp
SUBSCRIBE US

OPINION
FACEBOOK
COMMENTS
CATEGORIES
Africa
(1)
Al'adu
(1)
Alkamawa
(3)
Article
(3)
Blogger Tips
(1)
Economy
(5)
Education
(2)
Entertainment Gist
(1)
Gyaran-Jiki
(5)
Health
(13)
Jikar Iya
(11)
Kimiya
(1)
Kiwon Lafiya
(54)
Kukan Zuci
(5)
Kwalliya
(4)
Labaru
(23)
Lifestyle
(1)
Ma'aurata
(1)
News
(300)
Nigeria
(5)
Noma
(1)
Opinion
(3)
Picture
(3)
Politics
(15)
Profile
(2)
Q&A
(1)
Ramadan
(9)
Ramadan Tafsair
(1)
Siyasa
(1)
Sports
(72)
Tarihi
(5)
Technology
(1)
Tips
(3)
Video
(3)
YouTube
(5)
Zain Abeed
(1)
Zamantakewa
(1)
Novels Elite
Get the Most Exciting News and Read Your Favorite Hausa Novels. Let us be your source for exciting news reports worldwide, as well as access to a wide variety of blogs and blogging tools. We also offer novels in different languages including Hausa so you can easily read what interests you! Plus with our Google Adsense partner program, monetize when readers engage with your content.

Novels Elite
SUBSCRIBE
Posts
Comments
Links
Post a Job

LATEST POSTS

ADVERT
Novels Elite
Copyright ? 2024 Novels Elite | All Rights Reserved
DMCA.com Protection Status
Disclaimer |
Privacy Policy |
Terms and Conditions
[14/10, 6:06 PM]  Amin@ M Yusuf Yol@: Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun ?addara Takun ?arshe page 44 Complete by Boss Bature
by
Novels Elite Admin
September 06, 2024
Sponsored Link

BOSS BATURE
'

Jin maganar dr shureim yasa ta saki Batool da ke ta faman yin haki, tana ta ?o?arin Gyara veil Winta daya rufe fuskarta Unaisah taja hannun ta suka nufi Ciki, Gaba Waya idanun su Benazir na akan su, Yadda suke tafiya a tsanake cikin nutsuwa yayi matu?ar burge su, Tamkar tagwaye komai na jikinsu kala Waya, gwanin ban sha'awa suke kallon su, Batool sai kiciniyar gyara mayafin takeyi takasa ga Wan kunnanta da ya ma?ale gashinta kwata kwata Unaisah bata lura da halin da take a ciki ba, sai janta ta ke yi.



"Babyna" Benazir ce ta kira ta da sauri ta dubi inda take atsaye lokaci Waya ta saki murmushin farin ciki, ta saki hannun Batool cike da zumudi ta nu fe ta Benazir ta rugumota a kirjinta kamar zasu koma mutun Waya, wani irin sanyi ne Ya ratsa zukatan su, kamar sun yi shekara ba su haWu ba sunyi kewar juna.



Fuskar Aneelerh Wauke da murmushi take kallon su har cikin ranta taji dadin faranta ransu da ta yi...



"Babyna, nayi kewarki, shi ne kika tafi kika barni, fushi nake dake baki damu dani ba" ta fada tare da Wago kanta ta haWe fuska alamar bata ji dadi ba' rufe fuska unaisah tay da tafukan hannayenta cike da jin nauyinta ta furta"i'm really sorry mommy na, wallahi na damu dake, ban manta dake ba kina araina"



Murmushi Benazir tay, tare da manna mata peck a forehead Winta, ta tallabo fuskarta da tafukan hannayenta, wani irin kallon so da kauna take bin ta da shi kamar zata maida ita cikin cikinta, tuni Unaisah tasha jinin jikin ta da ganin irin kallon ?urullan da take yi mata.



?Bakomai take tunawa ba face lokacin data barta a kwamin wanka yar jinjira da ita cikin jini, sai gashi Allah ya raya abun shi, ta girma ta zama ?ar budurwa da ita, tsakaninta da taj sai godiya yayi namijin ?o?ari gurin rainon Angel, har abada bazata ta6a rabuwa da shi ba, ko da bazai kula ta ba sai ta san yadda tay ta maida auran su ko dan saboda Unaisah, ganin bata da alamun daina kallonta ne yasa ta ?ara rudewa muryarta adabarbace ta furta"Ya jikin naki? Kin ji sau?i"? ??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????Yar dariya Benazir tay don ta fahimce unaisah ta gano ta

?aga mata gira tay"Alhamdulillah my baby, naji sau?i sosai..."



"Yanzu kin gane ni wacece" dariya suka yi gaba Wayan su, Hakan Yasa ta fahimci taji sau?i yanzu tasan ita ba ?arta bace.

.

"Ki Wauka har yanzu ban dawo cikin hayyacina ba, saboda bana so ki daina kira na da sunan mamanki, kuma bana so na rasa kulawar da kike bani" tattausan murmushi unaisah tay"in dai wannan ne baki da matsala dani, zan cigaba da kiranki mamana, babu abunda zai canza"



Gaba Waya Sun maida Hankali akan Unaisah, In ka cire dr shureim wanda gaba Waya ya tattara Hankalin shi akan Batool dake ta ?o?arin gyara mayafinta ga raWaWin da kunnanta ke yi mata duk tabi ta burkice, ajiye cup din hannun shi ya yi kan table tare da mi?ewa ya je gabanta ya tsaya ya ru?o Veil Win Zai gyara mata jin hannun mutun yasa muryarta na rawa ta furta"Earring Wina Ya ma?ale gashina za fi nake ji"?



'Okay, calm down, I'll help you."



?jinjina mashi kai tay, ru?o mayafin yai tare da zame shi Ya sauko kan kafaWarta bai kalli fuskarta ba sai da Ya Cire mata earring Win da ya sar?e gashin, kafin ya Wago da idanunshi slowly ya dubi fuskarta adai dai lokacin ta buWe idanunta kaitsaye suka shiga cikin nashi bai san ya akai ya tsinci kan shi da jin matsanancin faduwar gaba hatta yanayin bugun zuciyarshi saida ya canza tamkar ana buga ganga.



wani irin yanayi mara misaltuwa ne ya ziyarce shi, kamar yadda yake kallon ta haka itama ta ?ura mashi kyawawan idanunta sai faman kyafkyafta su takeyi kamar Yaji ya shiga cikin su, gaba daya ta razana da kallon da ya ke yi mata ga wani yanayi da ta tsinci kanta mai wuyar fassaruwa,? hankalin ta ya Wan tashi, duk tasha jinin jikin ta aranta ta ayyana wanene wannan? Meyasa ya ke kallona? Ko dai jira yake in yi mashi godiya ne"? Muryarta adabarbarce ta furta"Um... thank you.'??



sam Ya kasa tanka mata sai kallon ta ya ke yi, yau ne karo na farko da suka fara ganin juna,? amma dukansu sun ji wani ba?on al'amari a zukatansu





Hankalin su Unaisah kwata kwata baya akan su..



Abunda yaWan Waure mashi kai kaman nin shi da yarinyar, tun da Allah ya halicce shi bai ta6a ganin Wan adam din da yake bala'en kama da shi irin Yarinyar nan ba! Ko Benazir da take kama da shi kamannin su bai kai haka ba, ita wannan kamar anyi photocopy din fuskar sa ne don ma ya Wan manyanta.



"Baby na Who is she? Is she your sister?'? muryar Benazir ce ta katse Kallon kallon da suke jefa ma juna su, ajiyar zuciya dr shureim ya sauke tare da juyawa ya koma kan Sofa Ya zauna yana mai mamakin kaman nin shi da yarinyar yau yaga


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login