Showing 189001 words to 192000 words out of 391264 words

Chapter 64 - Cigaban Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel

11 Feb 2025

2629

shatunsu ya fito rudu rudu, sai yaji ba dadi aran shi, ganin irin illar daya yi mashi kuma yayi imanin zafin marin da yayi mashine ya haifar mashi da rashin lafiya a jikin shi kamar yadda yaji Tani tace bashi da lafiya.



Kwata kwata shureim bai lura da Alhaji musa ba, cikin rashin kwarin jiki ya nufi dressing mirror.



"Shureim"!Ya kira sunan shi, Waure fuska yayi batare daya kalli inda yake ba, duk da yayi mamakin jin Muryarshi a cikin kunnanshi aranshi ya ayyana kome yazo yi dakin shi?ya dai san ba hakuri yazo bashi ba abune mawuyaci.



"Da kai fa nake magana"! ya faWa fuskarshi adaure, da farko yaso ya shareshi don yaga iya gudun ruwan shi amma sai ya fasa saboda mutunne shi mai matukar ladabi da biyayya yana ganin girman nagaba da shi bayan haka akwai na annabawa wato hakuri.



Juyowa yayi suka fuskanci juna

Muryar shi kasa kasa ya furta"Uncle, barka da safiya? Ka tashi lafiya"? ya dan yi mamakin tarbar da shureim yayi masa, amma bai nuna a fuska ba,

"ka zauna inason magana dakai" kasa kasa ya amsa da toh, kafin ya juya ya shiga wurin closet dinsa, jim kaWan ya fito sanye da jallabiya fara, a kan couch suka zauna shureim ya kau da idanun shi gefe Waya yana jiran jin dame yazo!



"Shureim dangane da abun da ya faru jiya bana a cikin hayyacina, kasan inada bad temper idan raina ya 6aci bana iya controlling kaina..." yanayin yadda yayi maganar ya Waurewa shureim kai har saida Ya juyo dakai ya kalle shi don ya tabbatar idan dagaske uncle musa ne ke yi mashi magana ba wani daban ba.



haWa ido su kayi da juna da sauri dr. Shureim ya kau da idon shi gefe Waya, hakan bai dame shi ba yaci gaba da magana cikin tausasa harshe"inaso komai ya wuce shureim, ni bana son duk wani abu da zaisa mu samu sa6ani atsakanin mu..." sai da yai wannan maganar shureim ya dube shi dakyau yace"uncle ni wannan duk ba damuwata bace, bana ru?e mutun a zuciyata, tabbas banji dadin kalaman daka jife ni da su ba, sun bata min rai, saboda ban ta6a tsammanin zaka iya furta min su ba, da ace wani na waje ne ya gaya min su bazan ji komai ba, amma kai da kanka uncle why? Saboda na fita da zeenatu yar uwata? Ko dan saboda rungumar da nayi mata wanda nikaina bada son raina nayi ba.." idanun shi cike tab da kwalla ya fada yana kallon cikin idon shi"saboda zafin kalaman daka furta min jiya ko bacci banyi ba, da bakin cikin su na kwana azuciyata" mood din fuskar Alhaji musa Ya canza sosai, kalaman shureim sun karya mashi zuciya sai yaji duk ba dadi.

Ru?o hannun shi yayi a cikin nashi ya ru?e su gam na Wan wani lokaci kafin ya fara magana a tsanake"Allah ya huci zuciyarka shureim, na gane kuskurena kuma in sha Allah zan gyara.."ya faWa yana Wan jinjina kan shi.



"Da akwai wata tambaya da kayi min ajiya, dangane da kullan da ni ke yiwa zeenatu, kace ka fara kokwanto akaina! Shureim ina son jin dalilin dayasa kace haka? Wani irin kokwantone kake yi akaina..." ba tare da jin shakkar shi ba yace"ban yarda da kullan da kake yi mata ba, raina yana bani kamar akwai wani abu da kake 6oyewa shiyasa nake kokwanto akanka, ka hanata cigaba da karatu, ka hanata yin kawance da kowa, sannan ka hana ta fita, kamar baka son kowa ya ganta, ita kanta zeenatun ta fara korafi kan kullan da kake yi.



Shiru Alhaji musa yayi tamkar bazai yi magana ba, can kuma ya saki Murmushin gefen fuska kafin yace"zan fada maka dalilin dayasa nake kullanta, in har hakan zai goge zargin da kakeyi akaina.." ya fada yana kallon shi.



Kafin ya Waura da cewa"Dalilin dayasa nake kullan zeenatu, is that I'm a famous politician with many enemies who want to harm me. Zeenatu is my weakness, bayan haka itace ?a Waya tak da nake da ita akusa dani, in har ban bata kariya ba, rayuwarta tana a cikin hatsari saboda akwai masu bin diddiginta, bana so inyi ganganci da rayuwarta, makiyana sun sha turo min sako akan zasu halaka zeenatu, shureim taya bazan killace ta agida ba"? Maganar Uncle musa tayi tasiri a cikin zuciyar shureim jikinshi yayi sanyi zuciyarshi ta karaya, hankalin shi ya tashi da jin abunda ke faruwa da rayuwar zeenatu!



"May be zeenatu ta manta bata fada maka ba, lokacin da tana zuwa high school, kusan kullum in zataje makaranta sai an samu wadanda suka kai mata farmaki, don ma Allah yasa akwai bodyguards da suke kula min da ita ay da tuni zeenatu babu ita araye" ya faWa tare da dukar da kan shi ?asa ya marairaice fuska kamar ba Alhaji musa ba.



Cikin sanyin murya Dr shureim Ya furta"Uncle, hankalina ya tashi da jin maganar nan, yanzu na fahimci dalilin dayasa kake kullanta, ni kaina bazanso abun da zai cutar da ita ba, amma kullan yayi yawa tun da har ta fara takura, bai kamata saboda wasu ahanata jin dadin rayuwarta ba, bayan haka Allah shi yake tsare bawansa aduk inda yake, kuntata rayuwarta agida bashi bane mafita ba, wlh duk tsaron dake agidan nan bazai hana a cutar da ita ba, amma idan muka cigaba dayi mata addu'a, in sha Allah makiyanka ba zasu ta6a yin nasara akanta ba!" wasa wasa dr shureim ya 6uge dayi mashi nasiha har saida ya tabbatar Ya samu nutsuwa Kafin yayi shiru yana jiran jin me zaice..



"Shureim nagode da shawararka, zanyi tunani akai in sha Allah, sannan akwai magana da nakeson yi dakai idan na samu lokaci..." bai kare maganar ba, wayar shureim ta fara ringing,

"Zan Waga kira"

"Okey, pls ka sameni a dining, zeenatu tana jiranka, tace bazata iya cin abinci in ba atare dakai ba..." jinjina kai shureim yayi bayan fitar Alhaji musa ya nufi gaban mirror ya dauki phone dinsa Ya duba sunan mai kira, mommyn su ce da sauri yayi picking ya kara a kunnanshi

Tunkafin yayi sallama muryar hajiya layla ta katse shi"shureim wai lafiya tun jiya inata kira bana samunka ko wani abu ya faru ne?



Cikin sanyin murya yace"a'a mommy, kiyi hakuri, wayar tana a kashe ne ban jima da kunnata ba"



Yanayin muryarshi ya sa ta tunanin kodai ba lafiya gidan?



"Ya jikin Benazir din? Ko har dr Ya sallame ku"



"Abun da yasa na kira ke nan, don in tuna maka, karfe 11 da rabi za'a sallame mu"



Agogo Ya kalla karfe 9, ajiyar zuciya ya sauke"In sha Allah yanzu zan shigo asibitin" amsa mashi tayi da toh, da sauri ya karasa shiryawa cikin shigar larabawa, ya Wauki facemask ya zura a aljihun shi da niyar in sun fita zai sanya ma fuskarshi, don baison mommyn su taga tabon marin da Alhaji musa yayi mashi yasan muddin tagani sai ta tada 6alli.



Adai dai lokacin daya fito daga dakin, sai ga Hajiya sarah ta kimtsa cikin riga da skirt na atampa, ta kashe daurin kallabi mayafinta akan kafada ta daura shi, ta ruke purse dinta a hannu, kasa karasawa tayi gare shi ganin tabon dake akan fuskarshi cos tun jiya da abin ya faru kowa ya shiga dakin shi basu kara haduwa ba, taji nauyin hada ido da shi duk saitaji ba dadi.



"Aunty, barka da safiya, kin tashi lafiya" fuskarshi dauke da murmushi ya nufe ta.



Tuni taji idanunta sun ciko tab da kwalla cikin sanyin murya tace"shureim ka yi hakuri da abunda ya faru jiya, wlh bakin cikine Ya hana in leko dakin ka, banji dadin ganin yadda tabon marin ya bata gefen fuskarka..."

Cikin sauri yace"pls komai ya riga daya wuce, kada ki damu kanki, lafiya kalou, ay uncle dinma yazo har daki ya bani hakuri harma mun sasanta kanmu" kallon shi kawai takeyi gwanin ban tausayi, ta dade bata ga mutumin mai saukin kai da hakuri irin dr shureim ba.

Ganin tayi tsaye tana kallon shine yasa shi furta"nayi waya da mommy ta fadamin karfe goma za'a sallame su, yakamata muyi sauri muyi breakfast sai mu wuce..." girgiza kai tayi da sauri ta share kwallar data zubo mata, tabi bayan shureim suka nufi dining

___________________________________
'?



Around karfe 10 na safe, Unaisah tana a zaune kan kujerar gaban gadon Benazir, har ta kammala shirin ta cikin abaya maroon colour, tayi rolling veil akan ta, baiwar Allah jikinta yayi sanyi, zuciyarta batayi mata dadi, sam bata son rabuwa da Benazir ta kamu da kaunarta, duk yadda take zumudin son tafiya don taga yan uwanta, saida taji ba dadi, sabo kenan turken wawa...



Gaba Waya ta shiga zurfin tunanin rabuwa da ita, benazir dake zaune gefen gadon ta ?ura mata ido tana kallon ta ko kyaftawa batayi, ta fahimci kamar wani abu yana damun yarinyar, ita kan ta faduwar gaba take ji kuma ranta yana bata kamar wani abu zai faru



"Babyna me kike tunani"! Cikin kun nanta ta tsinkayi muryar Benazir, wadda tayi silar dawo da ita daga duniyar tunanin data lula..



Numfasawa tayi a hankali take kallonta, tuni taji hawaye sun cika tab da idonta, hajiya layla tana a tsaye bakin kofar toilet tana kallon su fuskarta duk ayamutse, damuwarta halin da Benazir zata shiga idan aka raba ta da yarinyar, ita kanta ta shaku da yarinyar tana son ta, sai dai ba yadda suka iya dole su yi hakuri su rungumi kaddara.



Tattausar murmushi Unaisah ta sakar mata, tare da mi?a mata kwayar maganin dake a hannun ta"mamana ki sha maganin ki," dakyar ta ?are maganar tamkar zata fashe da kuka saboda tasan maganin bacci ne dr jazz ya bata don ta ba benazir tasha, duk don su samu tayi bacci ko sun tafi da unaisah....



Baiwar Allah Benazir kamar tasan me suke kokarin yi gabanta sai faduwa yakeyi, buWe baki tayi unaisah ta sanya mata kwayar maganin, ta kanga mata glass din ruwan hannunta ta shanye shi, ?an mintuna ?alilan Benazir ta fara gyangyaWi idanunta suka fara kokarin rurrufewa wani irin karfi maganin ke gare shi dr jazz ya iya aika aika...cikin karyayyar murya ta furta"babyna, kada ki tafi ki barni, inaji ajikina kamar tafiya zakiyi..." Wan zaro ido unaisah tayi da sauri tace"ki daina wannan maganar mamana, ina atare dake babu inda zanje" dafe kai benazir tayi da hannu Waya, dakyar take buWe idanun ta masu Wauke da matsanancin bacci ta ?urama unaisah ido cikin sanyin murya tace"dan Allah ki yafe min Angel, nasan ban kyauta maki ba, amma kada kice zakiyi fushi dani, kada ki tafi ki bar ni, wallahi ina sonki, Allah shine shaida ta bada son raina na tafi nabar ki ba, nayi maki alkawarin zan baki gatan da kika rasa na rashin uwa atare dake, zan tarairaye ki in baki kulawa Angel" a matu?ar ruWe Unaisah ke kallon Benazir, kalamanta sun ta6a mata zuciya, sun fama mata ciwon dake a zuciyar ta, amma sai tayi tunanin watakil tana sambatune akan yarta da ta rasa.



Kukane Ya kwacema Hajiya layla da sauri ta toshe bakinta da tafukan hannayenta saboda batason ta Waga masu hankali.



Baccin ne Ya rinjayeta, jikinta ya saki a sukwane ta kwantar da kanta saman pillow, ta lumshe idanunta har lokacin bata daina yin sambatu tana ambaton sunan Angel.



A hankali unaisah take binta da kallo zuciyarta na harbawa da karfi da karfi gani take kamar in ta tafi ba zasu ?ara haduwa ba, lokaci Waya taji tsantsar tausayin matar ya kamata, tayi fatan ace zata cigaba da kula da ita sai dai tasan daddynta bazai barta ba, after that yan uwanta suna bukatarta ita kanta bazataso tayi nesa da su ba, ruwan hawayen da suka taru acikin idanunta ne suka fara yar tseral kan kuncin ta.



"Azeezaty! Ke nake jira muje ko"? Dr jazz ne yayi maganar yana daga tsaye bakin kofar Wakin, mi?ewa tayi daga kan kujerar, kamar wadda aka zarewa laka, ta sunkuyar dakanta saitin fuskar Benazir ta manna mata sumbata har sau biyu kafin ta juya taje ta Wauko backpack dinta, ta kalli hajiya layla mi?a mata hannu tayi alamar tazo, da sauri unaisah ta ?arasa gareta, hajiya layla ta rungumota a kirjinta.



"Toh Azeezaty, mungode Allah yasaka maki da alkhairi, Allah ya baki ilimi mai amfani duniya da lahira, Allah ya baki miji nagari, zamuyi kewar rashinki, Wan zaman da mukayi dake mun saba dake, benazir zatayi kukan rashin ki, Ubangiji Allah ya albarkaci rayuwarki, Allah yasakama iyayenki da alkhairi..." amsa wa tadinga yi da ameen kamar kar su rabu da juna.



"Ki gaida min da mutanan gidan, in sha Allah zamu zo wata rana har gidan naku"



Murmushi Unaisah tayi"Allah ya kawo ku lafiya, Allah ya ?ara ma mamana lafiya, nima daddyna yace zai kawo ni gidan ku" murmushi hajiya layla tayi taji dadin maganar, sallama sukayi da juna, A hankali take tafiya tana waiwayon Benazir dake kwance tana ta sharar baccin ta....

Dr jazz harya fara gajiya da jiranta, sai faman duba wrist watch dinsa yake yi baya son chief ya karaso don yasan bai son jira.



Har fa ta kusa fitowa daga dakin sai kuma ta juya da sauri ta koma gaban gadon Benazir ta manna mata peck a goshin ta.



Ganin abun nata bame karewa bane yasa dr jazz shigowa dakin Ya tasa keyarta gaba suka fito, baiwar Allah tana tafiya tana waiwayon dakin hajiya layla tana tsaye bakin kofar room din, hawaye sun cika idanunta har saida suka bace ma ganin ta kafin ta juya ta koma ciki zuciyarta cike fal da kewar Azeezaty.



A dai dai lokacin da suka fito, hamshakiyar motar chief ta kunno kai ta entrance gate din asibitin yar uban su launin ash colour har sal?i take da daukar ido, yanayin yadda motar take tafiya slowly yayi matu?ar jan hankalin visitors dake zarya a arean wurin, suka bi da ido har saida ta tsaya a parking sace.



"Muje, Ina tunanin shi ne ya karaso" jaz ya fada tare da jan hannunta, tunkafin su ?arasa take ta kallon hamshakiyar motar, tayi mata kyau, lokacin dayazo kawota ba irin wannan suka hau ba.



Bayan sun ?arasa gaban motar, ta ciki aka buWe mata cardoor din wani daddaWan fragrance ne Ya daki hancinta, mai haWe da sanyi A.c.



"Ki shiga ciki" jazz ya faWa tare da nuna mata hanya, sunkuyar dakai tayi tare da shiga ta zauna, wurga ido tayi akan shi har saida taji gabanta ya fadi saboda wani kyau da taga yayi mata, ya kare gefen fuskarshi da phone dinsa, da alama waya yakeyi, fuskarsa tana asanye da mask.



Hadadden yard din dake ajikin shi Senator cotton material ne light sky blue, rigar short sleeve ce ta bayyana strong arms dinsa, na karfafan maza masu ji da kan su, lallausar sumar kanshi ta sha gyara, ya sabunta military hair cut din sa



Sunnar da kanta ?asa tayi ganin yana ?o?arin juyawa, janye wayar yai daga kunnanshi, Ya Wago suka haWa ido da jazz sai faman sakar sakar mashi murmushi yakeyi

"babban yaya, sannu da zuwa barka da safiya"

Calmy ya furta"lafiyalou jazz, ina fata kaima haka"

"Alhamdulillah"

"Ya mai jikin?

"Taji sau?i sosai"

"Naji dadin jin hakan, zamuyi magana anjima" amsa mashi yayi da toh, har time din bai kalli Unaisah ba, kamar baisan da zaman ta ba sai bayan da jazz ya rufe murfin motar, ta kamo belt zata daura taji ya ruko yana kokarin sanya mata ita wani irin shock taji, muryarta na Wan rawa ta furta"ina kwana"

"Ina lafiya" atakaice Ya amsa mata, agogon hannun shi tabi da kallo kirar rolex daytona tayi bala'en yi mashi kyau....bayan ya kammala sanya mata ya gyara zaman shi,

A hankali ya dago ido ya kalli senior Agent din dake zaune a driver seat"zamu iya tafiya" cikin girmamawa ya amsa mashi okey Sir,

Key yayi ma motar tare da yin reverse ya karya kwana motar ta fuce daga asibitin.



Ajiyar zuciya ta Wan sauke idanun ta akan window glass din motar, asibitin take kallo cike da jin kewar Benazir matar ta kwanta mata aranta, amma idan ta tuna yar uwar chief ce sai taji hankalinta ya kwanta, ta wani bangaren ta kosa su koma gida ko dan taga yan uwanta almost one week tayi kewarsu"



Fragrance din turaren chief Ya hana ta sukuni, ta wutsiyar ido take satar kallon shi, dogon hancin nan nashi ba karamin tafiya yake da ita ba. Hankalin shi na akan phone dinsa da yake scrolling

Tayi tsammanin gida zasu wuce kaitsaye amma sai taga kamar sun canza hanya, ba wadda suka biyo ba aranar da zai kawo ta, aranta ta ayyana watakil wata hanyar ce da bata sani ba.

Tana tsaka da yin zancen zucinta, suka karaso wani katafaren Obie mall luxury plaza



Tayi mamakin haduwar wurin tunani ta farayi ko me zasuyi a mall din? Ta dai zubama sarautar Allah ido.



bayan shigar su ciki agent din yai parking a katafaren parking space na mall din.



Shiru tayi zuru tana jiran jin me zaice, sai da ya shafe 5 mins kafin taji ya furta"Let's go inside." fitowa sukayi atare, da sauri senior agent din ya fito ya take masu baya, Hankalin Ta ba karamin tashi yayi ba ganin wayayyun ?an mata da samari yan gayu suna zarya a wurin duk sai taji ta raina kanta, wata irin kunyace ta kamata, takasa motsawa daga inda take ganin idon mutane ya dawo kansu, duk da facemask din dake akan fuskar chief hakan bai hana mutane kallon shi ba musamman yan matan dake gifta wa wasu kamar zasuyi tuntu6e tsabar yadda suke kallon shi, ga shi ba halin tunkarar shi saboda senior agent din dake atare da su, wani basamuden mutun ne ?ar?arfa babu annuri kan fuskarshi, ga bindigu dake soke a qugun shi.



Ganin bata da alamun motsawa ne yasa shi ruko hannunta a cikin nashi, rass taji gabanta Ya faWi duk sai ta kama yan kame kame tana faman noke kai, duk da yadda taso ta daure kada tai kauyacin saida ta kasa a hankali take satar kallon mall din yayin da suka nufi main entrance, Security guard din dake tsaron wurin sun gane chief, sai miko gaisuwa sukeyi cikin girmamawa kamar zasu durkusa kasa, tun da taga haka sai ta fara jin kanta wata hajiya gata ga chief, murmushin gefen fuska ta dan saki tana wani tafiya taku dai daya tana hura hanci.



Senior agent din ne ya ruke mata shopping cart, ganin taki daukar komai sai


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login