Showing 141001 words to 144000 words out of 391264 words

Chapter 48 - Cigaban Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel

11 Feb 2025

2632

sunan mai kiransa yayi mamakin ganin aunt saratu, Cos Ya manta when last Yar tahalikar nan ta kira da sunan tayi magana da shi.

Picking call din yayi tare da kara phone din a kunne, Cikin ladabi Ya yi mata sallah tare da gaishe da ita

Ko sallamar shi bata amsa ba ta furta"Owais, bayan sallar magbrib, Ka same ni a pool yard, Ina son yin magana dakai"! Cike da bada umarni ta furta, bata jira amsar shi ba, Ta katse kiran.

Kurawa screen din wayar ido yayi ba tare da ?yaftawa ba..."

"Yalla6ai, Mun ?araso"! Big guy ne Ya fargar da shi, sam bai lura sun karaso ba, Fitowa yayi da sauri Ya nufi Cikin main falo din gidan

Yana shiga bedroom dinsa, Ya rage kayan jikin shi, Ya shiga toilet domin Yin wanka,

*HAJJATY*

Safa da marwa Take Yi atsakar dakinta, tun safe take sa ran zuwan pravin shuru bai leko ba, Hankalin ta ba karamin tashi yayi ba, gani take kamar wani mugun abunne zai faru da ita, saboda abun da ya faru jiya yayi matu?ar daga mata hankali.

Yanke shawarar fita neman shi tayi, da sauri ta dauko mayafi ta yafa akanta, Tana kokarin fita suka ci karo da juna har saida ta bangaji kirjin shi, da sauri taja da baya tare da dafe gefen kanta da hannu daya

"I'm sorry wifey, Ina zaki je ne"? yayi maganar yayin da yake nufar cikin dakin idanunsa akan fuskarsa

From head to toe Ya kalle ta, farat Waya ya gane akwai wani abu dake damunta, da alama ko wanka batayi ba.

"Baki da lafiya ne" ya yi maganar tare da ru?o hannunta suka zauna gefen gadon ta

"Baki ji ina magana ba? Fashewa tayi da kuka tare da kifa kanta akan kafadarshi

Hankalin shi yayi matu?ar tashi jin kukan hajjaty, yana daga cikin abunda Ya tsana arayuwarshi.....

Cikin shesshekar kuka tace"pravin ina cikin tashin hankali, Saboda akwai mai bibiyar rayuwata, daren jiya bana acikin kwanciyar hankalina, a tsorace na kwana, ko baccin kirki banyi ba, ina ta jira ka dawo shiru baka zo ba..."

Tuni yanayin fuskarshi Ya canza zuwa tsantsar 6acin rai,

"Fada min meya faru dake a daren jiya? Wani ya shigo ne"?....Wagowa tayi da kanta hawaye na sintiri kan kuncinta ta kwashe komai ta sanar da shi...

Tafukan hannayensa ya daura kan fuskarta,A hankali Ya fara share mata hawayen ta

"Ki yi hakuri, in sha Allah koma wanene ke naman ki da sharri kan shi zai koma, Allah Yana atare dake wani bai isa Ya cutar min dake ba! ...." bai kare maganar ba, tace"bansan ya zanyi ba, wallahi ina jin tsoron ranar da asirinmu zai tonu, pravin bana son abunda zaija mu rasa kimarmu da darajarmu a idon mutanan gidan nan, saboda ina ji araina akwai wanda ke son ya tona mana asiri shiyasa aka fara bibiyana.." ta faWa tana jan numfashi kafin taci gaba da cewa"saboda fargaban abunda Ya faru daren jiya, ko abinci banci ba tun safe har yau kamar mai azumi, wanka ma nakasa yin shi...."

Ta ?are maganar, tana kallon cikin idanunshi

"Tuntuni saida naso In siya maki gida daban inda zakiyi rayuwarki cikin kwanciyar hankali, amma sai kika nuna bakison rabuwa da su....abunda nake jiye mana kenan...

"Duk laifinka ne, Abunda kayi min awurin dinner din hateem shine Yaja har wasu suka fara zarginmu, kuma ni gaskiya bazan bar gidan nan ba, kawai ka nema min mafita ..."

Jinjina kanshi yayi tare da ruko hannayenta acikin nashi"zan tambaye ki wani abu" daga mashi kai tai alamar toh

"Idan kika kama 6era adakin ki Yana yi maki 6arna, kuma kinsan zai iya haifar maki da gagarumar matsala wani hukunci zaki masa"?

"Meyasa kayi min wannan tambayar"?

"Kedai ki bani amsa"!

Shiru tayi jim kafin tace"hannayen da yake yin amfani da su wurin yin 6arnar su zan na?asa, sannan in murje bakin shi ta yadda bazai iya daukar komai da shi ba...." murmushi pravin ya sakar mata"kin kawo shawara mai kyau.." arude tace"bangane me kake nufi ba"
Bai bata amsar tambayarta ba, sai cewa yai muje bathroom In taimaka maki kiyi wankan da kika kasa"

Ajiyar zuciya ta sauke tare da mikewa suka nufi toilet atare almost 18 mins Ya fito dauke da ita a hannunshi, dukansu sun daura towel a waist dinsu,
Taimaka mata yayi ta sanya kaya, shima ya maida nashi

"Tashi ki je kitchen ki shirya mana abinci mu ci atare" amsa mashi tayi da toh,

Bayan fitarta da yan mintuna ta dawo hannunta ruke da try na kayan abinci, ta ajiye masu kan rug, saukowa yayi daga kan gadon suka zauna atare suna ci.....

___________________________
'?

Bayan kammala sallar Magbrib, Owais Ya nufo pool yard din gidan baba obie, Jikin shi sanye da farar jallabiya, tunkafin Ya ?arasa Ya hango Hajiya saratu zaune kan kujera ta Waura ?afa Waya bisa Waya, Hankalin ta na akan wayar hannunta da take dannawa


Cikin kunnanta ta tsinkayi muryarsa"Assalamau alaikum" ba tare da ta kalle shi ba tace"wa'alaikum salam,"
Zukunnawa yayi daga gaban kujerar da take Cikin girmamawa Ya gaishe da ita, Har cikin ranta taji daWin hakan da yayi mata sai dai bata nuna a fuska ba, wai don kada ya raina ta
"Lafiyalou My son, ina fata Ka wuni lafiya? Ya aiki"?
"Alhamdulillah.."
"Bismilla ka zauna" ta fada tare da nuna masa chair din dake facing dinta, mi?ewa yayi bayan ya zauna ya Wago da ido ya kalle ta, babu alamun zata kalle shi

"Mommy, kince kina son ganin na, zamu yi magana" sai da ta mula ta sha iska kafin tace"eh, magana ce mai mahimmanci, Ina fata zaka bani aron hankalin ka.."

Amsa mata yayi da toh, tsawon mintuna biyar ta shanya shi, kafin ta fara kora mashi jawabi dangane da zuwan su Zahra, da alfarmar da suka nema a wurin ta...." tun da ta fara maganar, Yake dubanta da alamun rudani akan fuskarshi.


"Ita zahran da ta kawo min maganar, tana Waya daga cikin interior designers din da suka yi mana aiki aranar dinner din hateem a hall dinne taga yarinyar, sunan yarinyar ta wurinsu Angel amma asalin sunan ta Unaisah, har hotonta sun nuna min, sunyi kama sosai da yarinyar wurin ka,"

Cike da son jin ?arin bayani yace"ko ta fada maki sunan Baban Yarinyar da sunan mahaifiyar ta"? Shiru tayi tana kokarin tariyo sunan su ....can tace"na tuna, sunan mahaifin yarinyar zaheer tajudeen, mommynta kuma sunanta benazir"

." Bari na kira Daddyn nata, naji idan Ya san su" da mamaki hajiya saratu tace"oh dama mahaifin yarinyar yana atare da ku"?
"Eh," ya bata amsa atakaice, har cikin ranta taji dadin jin hakan....
Phone dinsa Ya curo daga aljihu Ya danna ma Taj Kira, Tana fara ringing Ya saka wayar a handsfree don taji abunda zasu ce

"Yalla6ai barka da marece, Na shigo gidan na taras baka nan.."

"Ina agidan grandpa, zuwa anjima zan shigo"

"Allah ya dawo kai lafiya"

Am so nake na tambaye ka, Wa cece Aneelerh! Kamar na ta6a jin sunan abakin ka"

"Yalla6ai ka kamanta ne halan, matar aminina ce uzair, kamar mahaifiya take awurin Angel Wina..." murmushi hajiya saratu tasaki jin abun yazo mata cikin sauki

"Zamuyi magana idan na shigo gidan" amsa mashi yayi da toh, bayan yayi rejecting call din Ya Wago Ya kalli hajiya saratu dake kallon shi

"Yarinyarsa ce..."

"Alhamdulillah, Yanzu gobe da yaushe zasu zo ganin ta? ta tambaya tana kallon shi

"Duk lokacin da yayi miki, su zo kawai" murmushin gefen fuska tasaki, Taji dadin yadda yake bata girma
"Nagode my son, bari nasa akawo mana abun sha" da sauri yace"ina so zan shiga wurin baba"
"Okey, mu tafi tare" mikewa sukayi atare suka jera suna tafiya, abun ba karamin dadi yayi mashi ba, tsawon lokaci basa jituwa da juna, sai gashi silar neman unaisah da yan uwanta sukazo yi Allah Ya haWa kan su, Har fira ta fara jan shi da ita, a haka har suka karasa dakin baba obie...

Idan muka koma 6angarensu Hajiya Layla dake a asibiti, wuraren ?arfe 8 na dare, Hospital staff suka fara sallamar mutanan da ke zuwa dubiya, saboda a dokar asibitin karfe takwas na safe visitors suke zuwa da zarar takwas Na marece Yayi kowa zai tafi za'abar majinyaci karkashin kulawar nurses
Hajiya layla tace ita fa ba inda zataje, dole ta kwana don ta kula da yar ta, dr shureim ma ya goyi bayanta, tunawa da barazanar kashe benazir da ake Yi, Idan suka tafi ba lallai nurses su san lokacin da za'a farmake ta ba, duk da akwai cctv camera a kowani daki na marasa lafiya, bayan hakan asibitin Yana da tsaro sosai, kawai dai bai yarda subar benazir ta kwana ba tare da wani nata akusa ba
Hospital staff din basu Yi masu gardama ba, ganin sanannu ne a idon jama'a, kuma da ma ire irensu sunayi masu alfarma, kodan saboda matsayin dake gare su, musamman hajiya Saratu da takasance former firstlady ta kasar, tun da ta sanya baki a maganar suka amince hajiya layla ta kwana tare da ita.

Gaba dayansu sun hallara a harabar ajiye motocin asibitin, Sun fito domin tafiya gidajen su,
Mami da abie suna atsaye, Ga Aneelerh da Zahra da mahboob, Aneeleeh taso abarta tayi jinyar benazir,
"Mu zamu wuce, Ubangiji Allah Ya bata lafiya, Allah Ya tashi kafadunta, in sha Allah zamu cigaba da tayata addu"a" abie ne yai maganar tare da mi?a ma Alhaji ubaid hannu suka yi musabaha
"Mungode sosai, Allah yakaiku gida lafiya,"
Mami tace"dan Allah duk halin da ake ciki game da rashin lafiyarta ayi kokarin sanar damu"
Hajiya sarah tace"in sha Allah zamuyi kokarin hakan"
bayan abie da mami sun shiga mota, Hajiya layla ta ruko Hannun Aneelerh acikin nata fuskarta dauke da matsananciyar damu tace
"Dan Allah kiyi kokari Aneelerh, Zuwa gobe, Ku tuntu6i iyayen yarinyar da kikace tana kama da yarta, ku rokar mana alfarma awurinsu, su ara mana ita, idan ma suna bukatar mu biyasu kudi su faWi nawa suke so, ko nawa ne zamu biya, wallahi bana so na rasa benazir, ina matu?ar jin tausayinta...." la66anta na kerma ta ?are maganar, tuni taji hawaye sun wanke fuskarta
Wani irin tausayinta ne Ya kama Aneelerh, bata san sa'adda itama ta fara share kwallar ba, Yau dai sun sha kuka bayin Allah
"Mommy in sha Allah zanyi kokarin ganin sun bamu yarinyar, Indai akan benazir ne wallahi sai inda karfi na ya ?are...."
"Pls kukan Ya isa haka, Ku yi hakuri, mu cigaba dayi mata addu'a Allah Ya bata lafiya..." acewar hajiya sarah
Dakyar sukayi sallah da juna, bayan sun aneelerh sun shiga motarsu, A jere motocin suka fuce daga asibitin,

"Zan tafi ba dan naso ba, amma In sha Allah, gobe da wuri zan shigo asibitin"
Fuskar hajiya layla a yamutse tace"Sai Allah Ya kaimu.."
"Duk halin da ake ciki, pls ki sanar dani" ta amsa mata da toh,
"Allah Ya bata lafiya" ta amsa mata da ameen, dr shureim ne ya buWe mata murfin motar, Ta shiga daga ciki, kafin Ya datse mata, akan idonsu motar hajiya sarah ta fuce daga asibitin
Ya rage saura su uku dake atsaye suna kallon juna,

"Shurem muje ko"? Alhaji ubaid ne yayi mashi maganar, Sam baya son tafiya, Gani Yake kamar in ya tafi wani abu zai faru da benazir,
"Toh daddy" Yayi maganar, Tare da ruko hannun hajiya layla
"Mommy, nasan ko ban fada maki ba, zaki kula da ita, amma inaso ki sanya ido sosai, dole sai kin hana idonki bacci in ba haka ba..." bai kare maganar Ba Alhaji ubaid Yace"meyasa kace haka"?
"Daddy akwai wani abu da nake zargi akan benazir, zan sanar daku amma ba yanzu ba, saboda bana son Waga maku hankali, kawai abinda nakeso mommy kada kiyi gangancin kula da ita, in ba haka ba za'a iya samun matsala, duk da munsan Allah ke tsare bawansa amma da bukatar muma mu kula"
Hankali atashe Hajiya Layla ke kallon shi, Muryarta na rawa tace"Shureim dan Allah ka fada min meke shirin faruwa da Benazir dina, ni dama najima ina zargin akwai wanda ke bibiyar rayuwarta, so ake akashe min ita, ko faduwar da tayi a toilet sai da raina ya bani wani mugun abunne Ya faru da ita, in ba haka ba taya za'ace ta fita hayyacin ta? Bata gane kowa dake akanta?..." maganganunsu sunso rikita Alhaji ubaid Ya rasa gane inda zancen su Ya dosa
"Dan Allah kuyi min bayani meke faru ne"?
Da ido Hajiya layla tayi ma dr shureim Alamar yayi shiru saboda tana zargin ba hakanan Aka kyale Alhaji ubaid ba, kada su saki baki su sanar da shi zargin da suke Yi Yana iya zuwa ya sanar ma Alhaji musa, tunda Ya zama kamar ubansa komai zaiyi sai ya nemi shawarar shi
Jinjina kai dr shureim yayi alamar Ya fahimce ta,
"Daddy, Muje gida zan sanar da kai komai" Ya faWa tare da ruko hannun shi, Hajiya layla tayi masu Allah Ya kiyaye hanya, tana atsaye tana kallon motarsu har suka fuce daga hospital din,
Da sauri ta koma Wakin benazir, tana shiga, ta iske Nurse agaban gadon ga benazir zaune jikin ta sai kerma Yake tana ta sambatu
"Daddy, mommy, ku kira min taj, Ya kawo min babayna dana bar mashi, dan Allah ku bani ?ata, kada na mutu ban ganta ba...." lallashinta hajiya layla ta cigaba da yi sam bata fahimtar komai, sunan ?arta da mijinta kadai take ambato,
Har abinci nurse ta kawo mata, kwata kwata ta kasa cin shi, duk yadda mami takaiga lallashinta abun Ya faskara, Addu'oi ta koma tana tofa mata, har dare Ya tsala mami tana zaune kan kujera tana kallon ta, Har dr ya shigo ya kara duba jikinta, Ya bata magungunanta dakyar suka samu ta sha, daga bisani bacci Yayi awon gaba da ita, lokacin da aka fara kiraye kirayen sallar ishai'a, mami ta shiga toilet cike da zullumin kada wani ya shigo dakin Ya cutar da benazir, saboda ta razana da jin kalaman dr shureim, jin motsin mutun adakin yasa tayi wuff ta bangaje kofar toilet din ta f????? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? 
ito tana haki, Ko alwalar bata karasa ba..

*Daga alkalamin Boss Bature mu haWu next page
'?*

*Ga me bukatar karanta littafin kurkukun kaddara, 500 ne dukanshi za'a tura Via Opay, 8103884440 Hafsat Bature Muhammad, shaidar biya za'a tura ta whatsapp, 08103884440*
[14/10, 6:05 PM]  Amin@ M Yusuf Yol@: Y

Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Page 29 Complete
by
Novels Elite Admin
August 07, 2024
Sponsored Link

Novels Elite English

'?





Dafe kirji tayi tare da sauke ajiyar zuciya, ganin likitan dake kula da benazir ne



"Are you okey"? Daga mashi kai tayi alamar eh,



Ganin tana mashi kallon kamar bata yarda da shi bane yasa shi cewa"zan tashi daga aikine, Na shigo na kara duba lafiyarta ne, kafin na tafi...." murmushin Ya?e ta sakar mashi"mungode dr, Allah Ya saka da alkhairi, agaida gida" ya amsa mata da toh, harya fuce daga dakin Yana mai mamakin Hajiya layla, abun ya daure masa kai yadda ta fito daga toilet a haukace anya kuwa tana da lafiya"?



Komawa cikin toilet din tayi, sam babu nutsuwa atare da ita, shaf shaf ta ?arasa alwalar ta fito da sauri ta nufi closet din dakin ta dauko darduma ta shimfiWa tare da kabbara sallah.

Da zarar taji motsi adakin sai gabanta Ya faWi, bayan ta ida sallar, ta zauna tayi addu'o'i ta kai kukanta wurin Allah,

Kafin ta mike ta koma kan chair din dake fuskantar gadon benazir ta zauna tana kallon ta, patient gown din dake ajikinta launin light blue tayi mata kyau, A hankali ta kai hannu ta shafa gefen fuskarta, tuni taji ?walla sun cika idanunta.



Idan muka koma bangaren su Aneelerh, bayan komawarsu gida, A falo suka zauna kowa Yana jimamin halin da Benazir take a ciki, Ummi ta fito daga daki hannunta dauke da Baby junaid bawan Allah tunda Mahboob ya dauko shi daga makaranta, Ya dinga kuka Yana ambaton mommynsa, dakyar mami ta samu ta shawo kanshi Har yaci abinci tayi mashi wanka, har bacci Yayi, sauke shi ummi tayi da gudu Ya nufi Aneelerh ya faWa jikinta Yana kuka, Ta rungune shi tana lallashin shi, dakyar ta shawo kanshi har suka sasanta junansu...



Lokacin da hajiya sara ta shiga falon gidan, kasa yin sallama tayi saboda fargaban hukuncin da Alhaji musa zaiyi mata, Cikin sanWa ta nufi bedroom din su ko sallama batayi ba, ta shiga ciki,



A kwance ta same shi kan shimfiWeWan gadon shi, Ya tada kanshi bisa pillow, zeenatu na arungume da shi, ta daura kanta bisa kirjinsa, daga ita har shi kayan bacci ne a jikin su




Tayi tsammani bacci suke Yi, ajiyar zuciya ta sauke, ta lalla6e ta nufi cikin dakin, ta daura key dinta akan mirror, ta nufi toilet ta shiga, alwala tayo tana kokarin fitowa daga toilet din suka ci karo da shi, wani irin bugu kirjin ta yayi, tuni gumi ya lullu6e fuskarta, la66anta na kerma tace"yanzu na shigo, nayi tunanin bacci kake Yi, fatan na same ka lafiya..." tsare ta da idanunsa yayi masu matukar gigitata, gaba daya yayi mata kwarjini



"Ki faWa min wani hukunci Ya dace Inyi maki"! Rass taji gabanta Ya fadi, marairaice mashi fuska tayi"am sorry bazan ?ara ba, wallahi bansan na Waga maka murya ba, dan Allah Ka yafe min.."

Fuskarshi babu annuri Ya furta"cewa nayi ki fada min wani hukun ci Ya dace nayi maki"?

Shiru tayi batare da ta furta kalma ba, duk tasha jinin jikinta....fargabanta kada Yace zai turata U.s

Saboda bata son duk wani abu da zai rabata da shi, shiyasa take yi mashi biyayya sau da kafa, duk wani abu da tasan zai bata masa rai, tana kokarin ganin tayi takatsantsan da shi

"Daddy kayi mata hakuri tun da ta gane kuskuranta," muryar zeenatu ce ta ratsa kunnuwansu,

"Kinci sa'a, da yau sai kin yaba ma aya zakin ta" nauyayyar ajiyar zuciya ta sauke, har zata wuce ya sake shan gabanta, a rude ta kalle shi

"Ya jikin benazir din?

"Jikin nata yayi tsauri, kwata kwata bata a hayyacin ta, baiwar Allah tana jin jiki"



"Allah Ya bata lafiya, in sha Allah gobe da safe zanje dubata" har cikin ranta taji dadin jin zaije dubata,

"Allah ya kaimu lafiya.."

"Kije kiyi sallar, kafin kin kammala zan kira tani ta shirya maki dinner dinki, nasan kina jin yunwa, kin wuni baki ciki komai ba" ya fada tare dakai hannu Ya shafa flat tommy dinta, aruWe hajiya sarah take kallon shi, kamar ba Alhaji musa ba,yadda kasan badaga bakinshi kalaman suke fitowa ba,

Kamar sakarya haka ta kura mashi ido tana kallon shi, murmushin gefen fuska ya sakar mata, gaba daya ya nemi zautar da ita, dakyar ta samu nutsuwar sanya hijabi ta


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login