Showing 120001 words to 123000 words out of 346625 words
Chapter 41 - Jiddatul Khair Book 1 Hausa Novel Complete
Abuturrab yyi shi ma shi yyi, kamar daga gidansu aka kawo mata abincin, komawa yayi ya xauna yana murmushi yace "Nima na ci abincin amarya" Najeeb yace "Kafin ka ci na taka amaryar kenan" Umar yace "Wllh u are missing Khaleel kaji dadin abincin nan kuwa" Tasowa Khaleel yyi shima ya ci spoon daya, sosai suka dinga yabon girkin, shi dai Abuturrab na xaune yana kallonsu, sai da suka cinye abincin duk da ba yunwa suke ji ba, sannan duk suka fita xuwa masallaci, Ahmad ne last din fita, kafin ya fita ya nufi Abuturrab yyi kasa da murya yace "Amma daga gidanmu aka kawo abincin nan ko?" Abuturrab yace "What did u mean?" Ahmad yace "Ba Jiddah bace ta girka" Abuturrab yace "Haka ta ce maka??" Juyawa Ahmad yyi ya bi bayansu Umar, Abuturrab ya mike ya dau tray din abincin ya wuce kitchen, har sannan jiddah na tsaye ta jingina da bango, ya ajiye tray din yana kallonta yace "Wa ya aiko maki da abincin nan?" Ta kallesa, a hankali tace "Abincin ya fi karfin ace ni na dafa ko??" Naxarin maganarta ya shiga yi, ta tattara plates da xata wanke a sink sannan ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fita. Sake kallon pot din miyan yayi ya karasa ya bude sannan ya bude na shinkafar, rufewa yayi ya juya ya fita daga kitchen din xuwa masallaci. Ko da suka dawo mosque sun so Abuturrab ya kira jiddah suyi sallama da ita yace ai sallah take, haka nan ko wannensu ya basa kudi ya bata ladan girki, gefen kujera ya ajiye yace "Ta gode" sannan yayi masu rakiya har bakin mota yana kallon Ahmad yace "Xan shigo da safe in sha Allah" Ahmad ya hararesa yace "Kar ma ka shigo mana" a haka suka wuce a mota, Abuturrab ya juya ya koma cikin gidan, dubu sha biyar ne kudin da ya kirga, bayan kusan minti ashirin ya mike ya wuce sama ya bude kofar dakinta, xaune ya ganta kan darduma, ya nufi gaban mirror dinta ya ajiye kudin yana kallonta ta madubin yace "Gashi nan sun baki, dubu sha biyar, amma ban mance turarena da kika fasa ranan ba" juyawa yyi yana kallonta da kyau yace "Kinsan nawa turaren da kika fasa?" Kallonsa kawai take, yace "Dubu arbain da bakwai kika fasa ranan, don haka xaki ajiye wannan dubu sha biyar din har ki samo dubu 32 ki cika min kudin turarena" Yana fadin haka ya bar kudin gaban madubi ya nufi kofa ta bi sa da kallo, can tace "Toh ka tafi da kudin" Ya juyo yace "Sai kin cika" daga haka ya fita dakin. Karfe tara jiddah na wanke wanke a kitchen ya shigo, bin kitchen din ya shiga yi da kallo, ita dai tunda ta kallesa sau daya ta ci gaba da wanke wankenta, kettle din dafa ruwa ya dauko ya bude fridge ya fiddo goran ruwa daya ya xuba a kettle din sannan ya jona, satan kallonta yayi ganin hankalinta na kan wanke wanken da take, ya kai hannu a hankali ya bude murfin tukunyar shinkafar dake kan gas har lkcn, dai dai nan ta juya yayi saurin sakin murfin tukunyar, dauke kanta tayi ta ci gaba da abinda take, ya sosa kansa, sai kuma ya hade rai yace "Shi kuma sauran shinkafar wa kika bar ma??" Ta kallesa tace "Kai mana" ya kauda kai bayan few seconds yace "Na fara wasa da ke ko??" Bata ce komai ba ta dauraye hannunta bayan ta gama wanke wanken ta dau plate ta nufi gun tukunyar ta debi shinkafar duk da ta ci, ta ajiye pot din gun wanke wanke, ta bude miyar ta sa d'an dai dai da nama yanka uku sannan ta rufe sauran miyan ta dau wani plate me xurfi ta rufe shinkafar da shi ta dau spoon ta nufi kofa ya bi ta da kallon gefen ido har ta fita, shafa kansa yyi yana tunanin wani eatry xai kira yyi ordering abinci da daddaren nan a kawo masa, shayi ya hada bayan ruwan ya tafasa sannan ya fita kitchen din, yana haurawa sama ya kalli kofar dakinta sannan ya wuce bangarensa, bude kofar parlon yayi ya shiga sannan ya kulle, still yyi yana kallon plate din dake ajiye kan center table, ya karasa ya ajiye shayin hannunsa sannan ya bude plate din yana kallon abincin, ajiye murfin yyi ya mike, can ya kalli kofa, sai kuma ya xauna, kamar me contemplating sai kuma ya dau spoon din ya fara cin abincin. Washegari karfe takwas da yan mintuna Abuturrab ya bar gidan xuwa gidansu Ahmad, Umma bata amsa gaisuwar da yake mata ba, ya shafa kansa ya wuce dakin Ahmad, Ahmad na ganinsa ya mike yace "Let's talk" Kama hannunsa yyi ya fita suka tafi bangaren Abbansa, Abuturrab dai kallonsa kawai yake, Ahmad ya kulle kofar parlon yace "Me yasa ka dauke jiddah daga gidan su Ummi jiya?" Abuturrab ya hade rai yace "Gani nayi she isn't comfortable, sannan Aunty duk ta bi ta takurata duk ba wanda yace komai, shkkn saboda ba matata bace ita sai in xuba ido a cuceta?" Ahmad yace "Har Ummi ma cutarta take kenan?" Abuturrab ya shafa kansa ya xauna yace "Ni bance haka ba, wllh da kaga yanda na ganta shekaranjiya ko kai baxa ka bada shawaran in bar ta ba, ita Ummi bak'i sun mata yawa, babu abinda xata yi noticing, and Aunty sai aikenta take tana fita titi, what for?? I hate it when someone is being maltreated kai ma ka sani" Ahmad yace "Hmm, ka gano wani abu kuwa Abuturrab?" Abuturrab na kallonsa yace "Me kenan?" Ahmad yace "You are starting to develop feelings for Jiddah, na lura da hakan tun ba yanxu ba, wannan ya wuce tausayi da kwatar mata 'yan ci, gashi kayi gaggawar rabuwa da ita, don babu aure tsakaninka da ita believe it or not, ko da kuwa baka saketa ba shelan da ka dinga yi kana sanar ma kowa cewar ka saketa, ta saku babu wani kwaskwarima... Babu wani aure tsakaninku ynxu Captain, sannan kar ka manta babu idda a kanta..." Katse sa Abuturrab yyi yace "Nigerians have a very very poor thinking mentality, me yasa baxa ku yi koyi da wasu kasashen da suka fi ku wayewa ba, Shikenan ba dama mutum ya nuna rashin jin dadin abun da ake yi ma mace sai ace yana sonta? Ohk fine... Yanxu in xuba ido ayi ta cutarta kenan tunda ba sonta nake ba, ina ce ita ma mutum ce kamar kai, kamar ni, kamar kowa ma? To don me baxan kwatar mata right dinta ba, ko ka mance akan kwato mata right din nata yasa har naje na aureta? Sannan still a kan kwatar mata right din nata ne yasa na datse auren dake tsakaninmu, and duk wannan wa'axin da kake min ni na ta6a bude baki nace maka da aure tsakaninmu ne?? Ko kuma idan ma da auren gaya maka aka ce xanyi" Ahmad yyi murmushi yace "You are just confusing and disorganizing ur self, shi lamarin da ya shafi addini babu wayo a ciki dai, anyway Ummi is jet angry at you, gwara ko koma yanxu ka dau jiddah ka kai ta can gidan tunda dinner xa ayi yau, daga wajen dinner din sai ka wuce da ita gida, gobe Saturday ka kawota yini tunda baxa ka iya barinta a gidan ba, amma kasan me? Kawai ina ji a jikina xamanku tare da ita ya kusa xuwa karshe" Da ido Abuturrab ya bi Ahmad har ya fita. Motoci biyu ne lafiyayyu suka yi parking kofar gida, El-Basheer ya juya yana kallon warce ke xaune bayan mota ta sha glass yace "Toh ai sai ki sauka mun iso" Da mamaki tace "In sauka fa kace, a kan titin xan sauka d'an nan, motoci sun daina shiga get din gidan ne xan sauka a bakin titi" Yace "Toh ai babu wajen parking a ciki, ke baki ga mutane bane...." Tace "Toh ina ruwana da mutane, har yanxu dama Najeriyan bata canxa ba, mu ba haka ake yi a Masar ba wllh, idan ana biki ko wani shagali wllh dai daikun mutane ake gayyata da daddare, sai a tarfa ma kowa yar gurasar alkama a gefen faranti, a daura kofin madara a gefe, idan da yar cinyar kaza a saka a gefe shi ma, Allah ba a taro irin haka kamar ana yunwa, shi Kabirun yasan haka mutane xa su cika gidan xai bada mota a kawoni nan salon in gantale? wllh mu bamu saba haka a Masar ba, a gaskiya idan baxai yiwu ba a juyar dani kawai a mayar dani Bauchi, daga baya kada Usman ya kullaceni sai in dawo inyi Allah ya sanya alkhairi, amma wllh baxan sauka bakin titi ba duk k'ura ta kare min abinda babu a Masar, ko shi Usman din bai san ina hanya ba ai Aliyu ya sani tunda na sanar masa ta waya.... Aa gaskiya ba dole Allah ya sanya alkhairi juya mu koma kawai... Mu ba haka ake a Masar ba, komai bisa tsari ake yin sa" Kashe motar El-Basheer yyi yace "Kinga Hajja idan xaki sauka ki sauka ni xan tafi gun daurin aure ne, ga ki ga gate kice baxa ki sauka ba" Bude baki tayi tana kallonsa, can tace "Aa toh gaskiya Najeriya ba wajen xuwa bane, tunda nake a masar ba a ta6a min rashin da'a irin wannan ba, sun san girma da mutuncin tsoho..." Tana kai wa nan ta ciro wayarta fuska tsuke ta mika masa tace "Kira min Kabirun, ai shi na haifa ba kai ba" Bude motar El-Basheer yyi ya sauka yayi wucewarsa cikin gidan, ta bi sa da kallo baki bude, sai kuma ta sauko ita ma ta bi bayansa. Jiddah ce xaune bedroom din Umma kanta a kasa tana wasa da gefen hijab dinta, Umma tace "Jiddahh" dago kai tayi a hankali tana kallon Umma, Umma tace "Ina sauraronki, idan kika min karya kuma kar ki manta Allah na kallonki, kuma nasan kinsan makomar makaryaci" Lkci daya hawaye ya kawo idonta, Umma tace "Ina jin ki"
Those nulls reading my book for free and still commenting nonsense should know that i owe dem 500.... subhanallah!!! It's their gut for me wllh. In ma ku biya in ma kar ku biya babu pardon tsakanin mu. My diehard fans kuma we move.... 💖
Littafin Jiddatul Khair na kudi ne, it's 500 via
3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of payment via 07087865788... Thank you
Fareeskinglow is a last bus stop do u wanna have a fairer skin or u wanna glow up ur skin here is the last bus stop where u can get ur desired results, a dream of having auniform complexion, glowing skin nd getting rid of any skin problems
Fareeskinglow karshe ne Ina kuke masu son farar fata ko masu son jikin yayi glowing kawai ga dama ta samu fareeskinglow taso muku da kayan gyara jiki fatarki yayi fari tayi sheki duk Wani tabo irin su konewar rana masu zagayen Baki a ido,masu pimples masu fama da combination skin Nan Baki Nan fari Ina mata masu ciki da masu jego wayanda wuyansu ke Baki duk fareeskinglow tazo muku da kayan gyara Wanda zaisa fatarki tayi sulbi da sheki ki komai kamar tarwada
Instagram -fareeskinglow_89
TikTok-fareeskinglow
Facebook page-fareeskinglow
WhatsApp -08031898240
[6/11, 9:05 PM] +234 803 540 6041: Umma takara tambayen ta a wannan lokacin Ahmad yashigo dakin,umma ta Kalli Ahmad tace kasan halin Aliyu fadamin gaskiyan lamarin nan,nan take gaban jidda yafadi ita dai harga Babu dugon soyayyan abu turruab acikin zuciyar ta kawai tarike shi tamkar yayanta,umma takara kallon jidda dake ta hawaye tace fadamin gaskiya nace, hakane umma yasake ni tun ranan da muka tare,Ahmad yyi wani boyayyan ajiyar zuciya,nan take umma tamike, takira ummi tasanar mata duk abinda ke faruwa,nan take Abba ma aka sanar dashi gab da daurin,yaroki alfarman abashi 15 mins,aka kira abu turrab da abokan ango da suke Shirin zuwa daurin aure,Ahmad din ma dama yashigo neh yagaishe da umma ana jiran shi sai ya ,iske wannan lamarin dake Shirin rusa rayuwar abokin sa,jidda dama na tare da umma,sai aka kira abu turrab,dama dadi kam ya,iso tun tuni tareda ummi da anty dake ranta fari Kal ko ba komai ansamu daman Gai gaisuwan aneesah cikin kwanan nan,Abba da ransa yagama Baci ya zabgawa abu turrab Mari har so biyu, yace nagode abu turrab Ashe ban isa dakai bah,ya numfasa sai Kuma yace,katashi kabar min gida na nasallama,jidda Kuma a yau din nan zan auran da ita tun ni, na,isa da,gaban jidda yafadi sosai dake ta kuka,yace wa umma da ummi akan za,a daurawa Ahmad da jidda aure,Kuma a yau din nan Bai San sanda abu turrab ya yanke yafadi ba sumamme
[6/11, 9:05 PM] +234 803 540 6041: Jiddah ta goge idonta still ta ki cewa komai, Umma tace "Baxa ki min magana ba Jiddah?" A hankali Jiddah tace "Umma yace min babu aure tsakanina da shi" Umma tace "Kamar ya babu aure a tsakanin ku?" Jiddah ta gyada kai tace "Eh haka yace, wai shi ba mijina bane" Umma tace "A ina yace hakan?" Jiddah tace "A can gidansa, ya rubuta ne a takarda ya bani" Umma ta dinga kallonta kafin tace "Ina takardan?" Cikin sanyin murya tace "Ya ki bani" Umma tace "Amma ya nuna maki?" Jiddah tace "Ehh" Umma tace "Cewa yayi ya sakeki a takardan?" Nan ma tace "Ehh haka yace, shi ba mijina bane" Umma ta gyada kai bata kuma ce mata komai ba, bayan kusan minti goma ta mike ta fita dakin rike da wayarta, wani dakin daban ta shiga tayi dialing number wata aminiyarta tana dagawa tace "Hajiya karfe nawa xa ki taho?" Hajiya Rukayya tace "Ina hanya yanxu haka" Umma tace "Babu kowa gidanki?" Hajiya Rukayya tace "Toh na bar su dai suna ta shirin tafiya dinner da wani abu ne?" Umma tace "Toh shhkn tunda ba kowa, dama wata yar uwarmu ce aka kawo biki to bata son hayaniya, kinga nan din ma akwai taro shine da nake son ta xauna gidanki har bayan biki" Hajiya Rukayya tace "Ohh Allah sarki, to amma Badiya mai aikina na nan ai, ba sai su xauna tare ba" Umma tace "Yauwa toh, xan sa driver ya kai ta can din kawai, sai ki kira ki sanar mata bakuwa na xuwa" Hajiya Rukayya tace "Toh ba damuwa" Umma ta koma dakin da Jiddah ke ciki tace "Kaya kala nawa kika taho da?" jiddah tace "Na yau ne da gobe kawai" Umma tace "Ohk, xaku fita da driver xai kai ki gidan kawata yanxu, tunda naga ke ba son taro kike ba ai" Jiddah ta d'an yi shiru, sai kuma a hankali tace "Umma ai yace xai dawo anjima ya daukeni" Umma tace "Ehh kafin ya dawo din, sai yaje can gidan ka ya daukeki, ki tafi da jakar kayanki kawai" Jiddah tace "Toh" Bayan mota Umma ta sa ta shiga ta ajiye mata jakarta a gefenta, sannan driver ya bar gidan bayan ta sanar masa inda xai kai ta, tafiyar kusan minti ashirin da wani abu suka yi suka isa gidan Hajiya Rukayya, Drivern yayi ma mai gadi maganan cewar yayi leading dinta har entrance din gidan, tana shiga cikin compound din mai gadin ya nuna mata direction da xata bi, ta makale jikin kofar ta kwankwasa a hankali, ta fi minti biyar tsaye sannan aka bude kofa, wata mata ce ta bude kofar ganinta tace "Ke ce bakuwar da Hajiya ta sanar kina xuwa?" Jiddah ta gyada mata kai kawai, Badiya ta amshi jakar hannunta tace "Toh sannu da xuwa, Bismillah" Bin bayanta Jiddah tayi, ta xauna parlor, Badiya ta shiga dakin yan matan Hajiya Rukayya ta ajiye mata jakarta. Karfe biyar saura Abuturrab ya isa gidan Umma, ya fi minti biyar cikin mota sanin da mutane gidan shi kuma ba iya shiga xai yi ba, daga karshe kawai Maman Abdallah da ya gani a compound ya aika ta kira masa Jiddah, ba a dau lkci ba sai ga ta, tace "Wllh yallabai Umma tace suna can gidansu amarya" Da mamaki ya dinga kallonta, can yace "Toh nagode" Tada motar yayi ya bar layin ya dau hanyar gidansu, bayan yayi parking a waje ya dau waya ya kira Siyama tana dagawa yace "Ki ce Jiddah ta fito" Tace "Yaya mu muna wajen make up fa, kuma har muka bar gidan bamu ga ta xo ba" ya d'an yi shiru, kafin ya katse wayar. Tunanin wanda xai kira ya dinga yi a ciki amma ya ga ba kowa kuma don ko hauka yake ya san baxai kira Ummi ba, d'an tsaki yyi ya tada motarsa ya bar wajen. Tun da Abuturrab suka isa wajen da ake dinner tare da Ahmad da sauran abokansu yake xuba ido yaga inda xai hango Jiddah a wajen amma bai ga alama ba, hakan bai wani damesa ba don dama xuwa dinner din ne baya son ta xo ya kaita can gidan Umma, tun sanda Aneesah ta kyallara ido ta gansa take masa zarya a wajen, barin yanda taga yayi wani kyau cikin fararen shaddan da duk abokan Ahmad suka saka, ita a dole sai ta ankarar da jama'a cewar saurayinta ne, Ko mayafi bata daura kan damammen doguwar rigar jikinta ba shi dai sai bin ta yake da kallo, wani abokin Ahmad dake side din Ahmad din Abuturrab ke ta kallo yana son tuna inda ya ta6a ganinsa, he looks familiar amma dai bai ce masa komai ba, karfe goma saura Aneesah ta xo ta samesa tana yauki tace "My captain wai xaka xo ka maida su Mummy gida yanxu" Ya d'an kalleta yace "Toh ai bani na taho da motata ba, ban ma san inda yake yanxu ba, nima abun hawa na samu ya kawo ni nan" Tace "Haba Captain, ko wajen daya daga abokanku baxa ka amshi mota ka maida su gida ba...." Ko rufe baki bata yi ba sai ga aunty ita ma ta sha wani ubansun lace tana goge xufan goshinta da handkicin hannunta tace "Aliyu ka tashi