Showing 27001 words to 30000 words out of 350584 words
Kusan atare kuwa suka iso babban company’n, Dakata wanda yakasance kayan masarufi ake sarrafawa aciki, Tabbas company’n yana da girma kuma yana da kyau ba laifi, saboda ank’awata cikinsa da abubuwa masu kyau.
Saidai kuma ga mamakin Rayyern kwata kwata babu wasu ma’aikatan kirki aciki.
Haka dai Dr.Lukman yayi masa jagora harzuwa babban d’akin da sukeyin taro.
Koda ya shiga gaba d’aya mutanen dake wajen basu wuce su 18 ba, wanda kuma dukkaninsu suna zaune ne akan royal chairs.
Yayinda wani babban dogon table, wanda aka cika samansa da kayan drinks yayiwa gabansu k’awanya.
Akan daya daga cikin kujerun wajen Dr. Rayyern Mai-nasara ya zauna, wacce kuma ta kasance itace take facing na Barrister Kabir Saleh Dakata.
Agefensa kuwa Alhaji idi Sale Dakata ne zaune.
A hankali ya juyo ya kalli wani dattijon daya zauna ɗaya gefen nashi, Alhaji Abdu Tababa kenan.
Numfashi ya ɗan fesar tare da ɗan kallon Barrister Kabir Sake Dakata.
Wanda tun shigowar Rayyern d’in ya kasa d’auke idanu daga kansa, domin hakanan yaji idanuwansa nayiwa Dr. Rayyern d’in Kallon sani, yanaji ajikinsa kamar a wasu shekarun baya masu tsayi ya tab’a sanin the same irin fuskar na, saidai kuma to Fuskar waye? Waya sani mai irin fuskar?
Tambayar da bashi da amsarta, bashi kuma damai amsa masa haka yasa ya gaza janye idanunsa kan fuskar Rayyern yayinda yake motsa lips ɗinshi a hakali.
Shi kuwaRayyern ido ya ɗan zuba mishi a fakaice yana nazarto abinda ke zuciyarsa .
Gaggaisawa sukayi amutumce kafun daga bisani Alhaji Idi Sale Dakata.
Ya d’an muskuta ya gyara zamansa. kana yace.
“Toh Alhamdulillah domin kusan gabaki d’ayanmu munsan abunda ya taramu da kuma musabbabin had’uwar mu anan wajen.
Idan kuma akwai wanda zance baisani ba saidai wannan yaron wanda yazo yanzu.”
Ya fad’i maganar yana nuna Rayyern da hannu, cikin isa da gadarar dake bayyana cewar akwai wani abunda keyi masa suya a zuciya.
Wanda hakanne kuma yasa Rayyern dago kai, ya soma bin kowannensu da idanu, yana mai karantar labarin dake zuciyoyinsu akan fuskokin su cikin hikima, da kuma haɗawa da ɗan lbransu da ya sani.
Shikuwa Alhaji Idi Sale Dakata ci gaba yayi da cewa.
“kamar dai yanda kuka sani munzauna ananne saboda mu tattauna akan kasuwancin mu, sannan Rayyern kaida baka sani ba kasani, munyi wannan taronne nagamayyan manya-manyan company’s, saboda akwai buk’atar had’a kawunan mu, domin mu gudu tare mu kuma tsira tare bi ma’ana, mu had’e kasuwanci’n wuri guda mu haɗa hannu ta yadda zamu tsara farashin kayan abinci da sauransu a yadda mukeso..”
Ya dire ayar mgnar yana mai kallon.
Alhaji Abdu Tababa dake jinjina kai.
Kai Rayyern ya d’an girgiza tare da maida fuskarsa ya tsuketa waje d’aya, domin lokaci guda ya dawo asalin Rayyern Mai-nasara dinshi, hazikin matashin da bayajin shakka ko tsoron duk wani magauci’nsa ya rigada ya gama saninsu in and out yasan kowa yana da cikekken bayani kan kowansu.
Gyara zamanshi yayi tare da maida bayanshi ya jingina da jikin kujera,
Kana ya ɗan juya kanshi hagu da damanshi.
Muskutawa yayi ya maida kujerar baya kaɗan kana ya ɗaura ƙafarsa ɗaya bisa ɗaya sabida zogin da yaji yatsarsa nayi mishi dan toms ɗin dake ƙafarsan ya takure yatsar da Jannart ta fasa mishi, cikin zuba musu ido ya sauƙe sassanyan numfashi, tare da cewa.
"Kuyi haƙuri".
Yayi mgnar cikin mutuntaka da girmama su.
Cikin haɗe fuska Alhaji Yawale yace.
"A kan me? Me kake nufi da muyi haƙuri? Fito fili kayi mgn yadda zamu gane?".
Numfashin mai nauyi ya fesar sabida, sarawar da kansa ya farayi sabida yadda suke mgn da ƙarfi.
Cikin nitsuwa yace.
“Bana buƙatar had’a hannu daku a cikin kasuwanci na!!!".
Ya fad’i hakan in don’t care manner, domin iya gaskiyarsa ya fadi kamar yadda suka nemi ji.
Idanu suka zazzaro gaba dayansu.
Yayinda Dr. Lukman dake gabansa ta gefensa bisa hagu yace.
“Haba Dr.Rayyern ya zaka fad’i haka, agaban mutanen da yawancinsu sun haifeka, at least dai ai ya kamata ka daraja su ko dan sun fika gogewa a harkar tunda tun kan a haifeka suke juya kobo ta zama dubu...”
Wani irin kallo da Rayyern din ya watsawa Dr.Lukman d’inne yasashi saurin rufe bakinsa gum, saboda hatta hantar cikinsa saida yaji ta kad’a.
“Bazan had’a hannu dasu ba, na fad’a na kuma sake maimaitawa Ni DR. RAYYERN BASHEER MUHAMMAD MAI-NASARA bazan had’a hannu dasu ba!!!”
Ya fad’i maganar da muryar dake bayyana iya gaskiya, da kuma zallan rashin tsoro ko shakkar kowa dake wajen.
Gaba dayansu shiru sukayi sai Alhaji Ma’aji wanda yake da company'n Ma’aji and Sons ne ya d’an muskuta, tare da fad’in.
“Meyasa bazaka had’a hannu damu ba?”
Wayarshi ya ɗan zaro cikin aljihunsa kana ya ɗan danna kaɗan sannan ya medata cikin aljunsa tare da cewa.
"Awa ɗaya dana baku cikin ɗaƙiƙun rayuwata da Allah ya aramin, kunci 21mn saura muku 39mn, in kuma kun gamane zan tafi."
Cikin hatsala Alhaji Yawale yace.
"Toh meyasa kace bazaka haɗa hannu da mutane ba".
Juyowa yayi ya ɗan kalleshi kana yace.
“Sabida tafiyata da taku ba iri ɗaya bane.
Muddin muka ce zamu haɗa hannu, dole gefe ɗaya zai rinjayi ɗaya,
ta yiwu ku rinjayeni.
Ku ɓata min kekkyawan TUBALIn da aka ginamin.
Ko kuma Ni in rinjayeni in ruguza muku mummunan TUBALIn da kuka gina tun da daɗewa, in ɗauraku bisa tsarina wanda kuma nasan bazaku lamunci hakaba.
Dan haka muyi tafiyar a rabe shi yafi.
Domin ni dai a atafiyata talaka nake dubawa.
Ku kuma aljihunku kuke dubawa, ni kuma ba haka bace a tawa tafiyar, domin ahar kullum talaka nake dubawa, da rayuwarsu, manoman da suke noma abinci, su yake zuwa ya gagara yafi karfinsu, Yayinda ku kuma kunanan kuna juya abincin da suka noma da wahalarsu, yana zame muku manyan kud’ad’e, Sam baku damu da talakan daya noma abincin ko yaci ya koshi ba, ko bai cika wannan duk ba damuwar ku bace, saboda haka.
Bazan had’a hannu daku aci gaba da cutan talakawa ba, domin sudinma mutanene kamar kowa!!!”.
Wani irin murmushi mai cike da tarin ma'anoni Barrister Kabir Saleh Dakata yakeyi, yana mai kallon Rayyern ido cikin ido cike da alamun so, da kuma tsoro can ƙasan zuciyarsa.
Su kuwa sauran gaba ɗaya a hatsale suke
Cikin yanayi hasala Alhaji Idi Sale Dakata yace.
“Okay wannan dalilin shi yasa ka zagaya gaba d’aya, kan manyan manoman da ƙanana da suke sayar mana da abinci ka hanasu sayar mana, har sai sun gama sun ware wanda zasu ci kafun su kawo mana mu mu saya?.”
“K’warai kuwa hakane, saboda hakkinsu ne kuma guminsu ne, ya zama lallai tilas cutarwar da kukeyi musu ya isa haka, Manoma bawai bayinku bane, domin da ace babusu yau da dukkanku baku kai wannan matakin ba, har yaushe zaku daina ci gaba da cutan mutanen da suke taimakon ku?.”
Ya kai k’arshen maganan nasa, cikin wata irin Muryar dake bayyana, cewa a shirye yake da yayi fito na fito da kowanne daga cikinsu, Sam babu alaman tsoron acikin zuciyarsa.
Wani irin bak’inciki da kuma k’unci ne suka cika zuciyar Alhaji Idi Sale Dakata, wanda hakan yasa shi hasala, ak’ufule yace.
“Indai wannan k’udurin naka ne basai kana da rai da lafiya zaka cika saba, Lallai Tabbas ayi mugani idan zai yiwu!”
Cikin tsoro Barrister Kabir Saleh Dakata ya juyo ya kalli yayan nashi Alhaji Idi Sale Dakatan har ya buɗe baki zaiyi mgn kuma, sai yayi shiru ya juyo yana kallon Dr Rayyern Mai-nasara da yayi.
Murmushin dake bayyana izzarsa da fito da kwarjininsa, kana ya d’ago ya kalli Alhaji Idi Sale Dakata.
Cikin bayyana rashin tsoronsa yace.
“Kwarai saida rai da lafiya ake komai, amma kuma abun jin dadin shine babu wani mai rayawa ko kashewa sai Allah, babu kuma wani wanda ya isa yin abunda Allah bai nufa ba, koda wayeshi kuwa.”
Sosai Alhaji Ahmed Tambari ya jinjina kanshi, hakama Barrister Kabir Saleh Dakata, fuskarshi suka zubawa idanu.
Suna tuno irin kamarsa da ya ƙalubalancu shekarun baya.
Dr Lukman kuwa rumtse idanunsa yayi sabida murya Rayyern na tuna mishi wata muryar data gabata.
Da ƙarfi ya kuma rumtse idanunshi sabida hatta ɗan maƙolloton wuyan RAYYERN irin na wancan mutumin ne.
Da sauri ya buɗe idanunsa jin Alhaji Abdu Tababa na cewa.
“Tabbas babu mai rayawa ko kashewa sai Allah amma.
Yaro ka san cewa komai akwai sanadi.
Toh Lallai watarana za’ayi sanadin da zuciyarka zata tsaya da bugawa ka kiyayi kanka.”
Alhaji Abdu wanda yake aboki ga Alhaji Idi Sale Dakata ya fad’i hakan cikin hasala.
Shikuwa Rayyern awannan karon dariya yayi harsaida fararen hakoransa suka bayyana, saboda shi gaba d’aya dattijawan ma gani yake kamar basu San mesukeyi ba, domin harya fara tunanin cewa girma ne kawai ya Kamasu.
Mik’ewa tsaye yayi ahankali tare da daukar glasss dinsa dake aje bisa table d’in, taku daya biyu yayi ya tsaya tare da juyowa ya kalli Alhaji Idi Sale Dakata.
Fuskarsa dauke da wani murmushi mai rugurguza zuciyar magauta yace.
“Idan akwai Allah to babu wani wanda ya isa da juyya RAYYERN Mai-nasara dole ya dakatar da Dakata in dai kan sayan k’udiri ne.”
Cikin fushi Alhaji Idi Sale Dakata ya buga table din dake gabansa, tare da fadin.
“Karya kake yaro, wallahi kai karamin al'haƙine, domin kuwa mun munji da wayanda suka fika tauri da tsaurin ido ma, saboda haka kai ba komai bane.”
Still wani irin murmushi yayi Cikin kuma nuna halin ko inkula yace.
“Wai tsoro kuke bani ne?".
A hatsale Abdu Tababa yace.
"Isa muke nuna maka".
Ronƙofawa yayi kanshi kaɗan kana yace.
"Hmmmm nifa RAYYERN Ina da taurin kai, ni nan Rayyern babu wanda ya isa sakani abunda banyi niyya ba, haka kuma babu wanda ya isa sakani yin abunda zai sab’awa addinina, idan kuma kuna ganin wasa ne to Lallai magwaji ya gwada ya gani!!!.”
Ya ƙarashe mgnar da ɗan sauti.
Kana ya D’an rank’wafo bisa kan Alhaji Idi Sale Dakata, cikin hade fuska da kuma zafin zuciya yace.
“Ina raga muku ne kawai saboda waɗannan fararen gemun dake kan fuskokinku, amma akasin haka hmmm nima zan iya take kowa kuma ya taku!!!”
Yana gama fad’in hakan ya juya afusace ya fice daga cikin dakin taron.
Dai-dai lokacin kuwa mota k’irar Black Benz ta faka a farfajiyar wajen, ahankali Jannart ta zuro da kwawayan legs dinta waje, wanda suka sha dogon takalmi na al'farma, sannu ahankali kuma itama ta fito daga cikin motar gaba daya.
Wata irin fitinanniyar gown ce mai masifar kyau ajikinta. Yayinda ta yane kanta da mayafin rigar, wanda hakan ya fallasa asirin kyawunta mai daukar hankali, daga gefen damanta kuwa Abdull ne ya fito, inda hannayensa ke dauke da wasu manyan basket guda biyu.
Domin zuwa sukayi musamman dan kawowa su Daddyn nasu da kuma Barrister Kabir abinci, saboda sun shaida musu cewar suna da taron da zasuyi, shiasa Momy tayi girki na musamman aka kawo musu.
Dai-dai isowar Jannart steps din da zata haura zuwa cikin hall din, shi kuma Dr. Rayyern ya fito daga cikin hall din ransa a matuk’ar b’ace ga wani irin masifeffen ciwon kai wanda ihun dattawan nan suka sakar mishi, ga yatsarsa dake zogi dan baima sha mgnin da safe ba.
Karab idanunsu suka sark’afe acikin na juna, saidai kuma ganinsa da Jannart d’in tayi ne yasa ta saurin janye jikinta baya.
A cikin hall ɗin kuwa gaba ɗaya sun hargitse kowa da abinda ke faɗi.
Haka yasa Barrister Kabir Saleh Dakata miƙewa da sauri ya nufo woje yana mai bin bayan Dr Rayyern Mai-nasara.
Shikuwa Rayyern kasancewar afusace yake shiyasa ko sake kallonta baiyi ba, direct ya nufi wajen motarsa wanda hakan yasa Jannart ta bisa da kallo.
Har saida ya b’acewa ganinta.
Yayinda Barrister Kabir Saleh Dakata ma da yanzu ya fito sai binshi da idon yayi.
Abdull dake tsaye ne ya kalli Jannart tare da cewa.
“Ya dai kinsan sane?”
Dan kauda kanta gefe tayi, batare kuma da taja zancen ba tace.
“Eh muje kawai.”
Jin hakan ne kuma yasa Abdull Sakai.
Da sauri suka tsaya ganin ƙanin mahaifin nasu, sai dai hankalinsa baya kansu.
Motar Rayyern Mai-nasara ya zubawa ido.
Yana mai motsa lips ɗinshi a hakali.
Jin muryar Abdul ne ya sashi ɗan juyowa, ya amsa gaisuwar yayi tare da kayan kana yace.
Su tafi gida.
Daga nan suma suka juya gida.
Rayyern kuwa daga Cikin company din direct cewa yayi driver ya dawo dashi gida.
Hakan kuwa akayi suka nufo gida kai tsaye.
A nan Nassarawa G.R.A kusa.
Riyyam-nsra ne ke tsaye ajikin wani tamfatsetsen gate na alfarma.
Wanda garin yawon zafaye anguwar da sukeyi ne da tattaki shida Nasir ɗin shi suka gilma ta gidan.
nan kuwa Nasir yace.
"Riyyam-nsra ya tsaya suyi video a gate ɗin gidan.
A hankali yake shafa tarin sumar dake kwance akansa.
Ahmad dake tsaye agabansa yana rike da, wayar Riyyam dinne yayi dariya tare da cewa.
“Nifa wallahi yanzu kam nagaji da rik’e wayannan, tun d’azun kake cewa zakayi video da waƙar hausa amma ka kasa, sai kace wani bak’o a harkar.”
Dariya shima Riyyam din yayi tare da cewa.
"Kafa san hausar tawa kar inje bin waƙar bai hauba."
Murmushi Nasir yayi tare da cewa.
"No kada ka damu zaiyi."
Murmushi Riyyam-nsra yayi tare da shafa sumar kanshi kana, ya ɗan ware sawunsa.
lokaci d’aya kuma ya nutsu, tare dasa Ahmad yayi start din videon, cikin abubuwansa irin na tiktodians daya saba, ya soma rawa tare da bin wata waka dake tashi acikin wayar, inda yake cewa.
“Niba gida ba niba mota ba,".
Yayi mgnar yana nuna gidan bayan nashi
Kana yaci gaba da cewa.
"Bamai tarin dukiya masu yawa ba, Babana shiga gwamna ba, ba shugaban k’asa ba ba kuma member ba".
Sosai Nasir yake murmushi yana jinjina mishi sabida yayi masifar kyau da bin waƙar hausa.
Cikin karsashin ganin Nasir na jinjina mishi yaci gaba da cewa.
"Banje makaranta maitsada ba, banje Dubai ba kuma banje London ba.
Gidanmu ba a G.R.A ne ba, ban d’auki selfie nasa Instagram ba.
Ko zana zamma saniyar ware wallahi ni baza na zam makaryaci ba!!!”
Sosai yake wani irin rawa mai ƙayatarwa yayi masifar kyau.
Dai dai lokacin kuwa Motar Dr Rayyern Mai-nasara ta kunno kai dai dai wajen gate din, Yayinda motar Ramadan ma ta kunno kai ta b’angaren hagu, saboda shima yanzun nan shigowarsa cikin layin nasu.
Atare suka ci wani irin birki tare da zaro idanu saboda G.....
Fawal beauty parlor sunai muku albashir da bude gidan Mata wato kigyara da kanki👩🏻🦰 da cewa suna gabatar da aiki na zamani kamar su gyaran jiki, spa kenan gyaran fuska wato facial,gyaran Kai, hair style , gyaran kafa pedicure,gyaran hannaye, manicure kitso,lalle ja da bakki,ba'a barsu abayaba suna saida kayan gyaran aure, turaruka,man shafawa, suna kwalliya wato makeup,turaren wuta, humrah,kulaccham dama abunda Baku sanshiba wato maida tsohuwa yarinya akankanin lokaci😄iya kudinka iya shagalinka💃kudai ku hanzarta zuwa ga wannan gida na mata zallah (FAWaL BEAUTY PARLOR)
Address: Main gate na fire service jimeta, opp sixty plaza.
kada kubari abaku labari😍 munai muku maraba a koda yaushe Mata yan kwalisa mace sai da gyara , yar uwa bora ba sunanki kizama mowar mai🏨 da taimakon FAWAL BEAUTY PARLOR 👩🏻🦰da kudinki qalilan kifita sab abunki ki baza kamci mai kama jiki.
Gamai buka contact CEO FAWaL BEAUTY PARLOR kan 09033901035 or 08078809930 sai kunzo, our time services from 8:am to 7pm, Monday to Saturday/ Sunday 10am to 6pm🪞🎁🛒🛍️🤝🏻
By
*GARKUWAR FULANI*
11/15/21, 7:20 PM - Auntyna: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*TUBALI*
PAGE 8
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
*FREE PAGE ne*
*Littafin TUBALI na kuɗine hamzarta ki biya kafin a gama free PAGE in saki a Group, ƙaramin group 500 special Group 1k ne, 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU, sai ki turo min shaidar biyanki ta whatsApp number na 09097853276, ko kuma ki sayi katin mtn ki copy number's ɗin katin ki turo min ta whatsApp 09097853276*
Ganin Riyyam Nsra da sukayi, domin daga Rayyern har Ramadan kusan atare idanunsu ya sauk’a akan matashin yaron dake tsaye ajikin gate din gidansu.
Wanda shima kuma Rayyern din d’ago kansa kenan da zaiyi, ya sauk’e idanunsa akan na Rayyern dake zaune agaban motarsa, inda yake zaune akan kujerar mai zaman banza, ya zauna agaba dinne kuma saboda lokacin daya fito daga hall din taro, na Dakatas company ransa a matuk’ar b’ace yake, wannan yasa bai tsaya wani tantance inda zai zauna dinba, kawai sai ya bud’e gaban motar ya shiga ya zauna.
Sam kwata-kwata babu alaman murmushi akan fuskarsa, saima tsananin b’acin ran da yasa fatar fuskartasa tayi jajur, haka ma idanunsa, ga kuma wata yar jijiya da ta bayyana akan goshinsa, sosai yakejin kansa na d’anyi masa ciwo, wanda kuma hakan ya faru ne saboda d’an yawaita magana da yayi yau din, da kuma ihun da way’ancan dattawan suka dingayi masa tsakar aka.
“Laaah Hamma Rayyern!!”
Riyyam-nsra dake tsaye fuskarsa d’auke da tsananin farinciki da kuma mamakin ganin Rayyern d’in ya fad’a, yana mai d’an matsawa daga jikin gate d’in, kaitsaye ya nufo wajen da motar Rayyer’n d’in ke tsaye.
Still fuskarsa dauke da murmushi yace.
“Thank God dama zan sake ganinka anan kusa, jiya kun b’acemin a airport nasha wahala sosai awajen neman ku.”
Idanu Dr Rayyern Mai-nasara ya lumshe duk da cewar, baya iya jiyo abunda Riyyam d’in ke fad’a, amma ya daiga bakin yaron na motsi kuma ya karanto abinda yake faɗin.
Dai-dai lokacin kuwa daga cikin gidan, Baba Mauɗo ya wangale musu makeken gate d’in, wanda hakan yasa direct driver’n Rayyern din ya tura hancin motar ciki.
Wulgawan da motar tazo yine kuma yasa Naseer dake tsaye ya sauke idanunsa akan, wani handsome guy dake zaune acikin motar, wanda yake matuk’ar kama da abokinsa Riyyam-nsra.
Bakinsa ya wangale cike kuma da tarin mamaki yace.
“La Riyyam kalli wani maikama da kai.”
Murmushi Riyyam yayi tare