Showing 147001 words to 150000 words out of 350584 words
Ramadan ka kula da aikinka, kasan ganinka zaisa sauran Doctor's din karsashi.”
Cikin gamsuwa Ramadan yace.
“Toh Hamma Rayyern Allah ya kiyaye hanya, Insha Allah kuma zan kula.”
“Amin.” Yace yana mai miƙewa tsaye.
PA kuwa tuni ya fita, yayinda Ramadan da Riyyam-nsra suka mara mishi baya.
Kana shima Rayyern ya bisu a baya.
“Rayyern!!”.
Yaji muryar Abbanshi da sauri ya ɗan juyo.
Ƙofar ɗakin Jannart ya nuna mishi tare da cewa.
“Dan Allah ka shiga ka sallameta, na roƙeka da girman Allah.”
Wani irin abu mai nauyi yaji ya danne masa zuciya.
“Ya salam".
Ya fadi a ransa jin Abban yace ya hadasa da girman Allah wato badon shiba.
Wani rauni, da damuwa ne suka rufesa, sabida ganin da yayi suna gab da sashi a sahun ya'ya marassa biyayya.
A hankali ya juya nufi ƙofar dakin.
Ita kuwa Jannart kasan cewar bakonta (al'ada) ya dawo daren jiya ne, yasa yanzu ta fito daga wonka daga ita sai towel ajikinta, take zaune agaban dreesing mirror'nta.
Rayyern kuwa ahankali ya tura ƙofar falon ya shigo, tare kuma da maida kofar ya rufe.
Ahankali kuma ya tako zuwa tsakiyar falon.
Murya a dakile yace.
“Salamu alaikum.”
Jannart dake zaune kuwa shiru tayi, tare da aje goran man da take shafawa, dan jin kamar mgnar mutum, Jin shiru babu alaman wani motsinne kuma yasa ta cigaba da shafa mai dinta.
Still tana cikin shafa maidin ne kuma tasake jiyo kamar sautin muryar mutum.
Da sauri ta mik’e tsaye tare da nufar kofar fita, ahankali ta bud’e k’ofar tare da d’an lek’o kanta tace.
“Waye?”
Shiru yayi ba tare daya bata amsaba.
Jannart kuwa hakanne yasa ta sake leƙo da kanta, sai dai bata ganshiba.
Jin kaman da gaske ba kowa acikin falonne kuma yasa ta fito gaba ɗayanta.
Inda tayi taku ɗaya ana biyu ta ganshi tsaye.
Cikin wasu irin fitinannun Suit bakake masu masifar kyau da sheƙi.
Da wani irin sauri ta juya ta koma cikin labule.
Shi kuwa Rayyern dauke kansa yayi gefe, kamar bai ganta ba murya a dakile yace.
“Na tafi.”
Da sauri, kuma cikin muryarta dake rawan fargaban ganinsa da tayi, da kuma ganinta da yayi ahaka tace.
“Allah ya tsare ya kiyaye hanya”.
A takaice yace.
“Amin, idan da zuciya ɗaya kika fada”.
Yana faɗin haka ya juya ya fita.
Jin alamun fitansa ne kuma yasa ta fitowa, daga inda ta boye cikin sauri ta koma cikin bedroom din, tana nanata mgnar sa ta karshe, da taji ya fada.
Shi kuwa yana fita, kai tsaye Airport suka wuce.
Su Ramadan kuwa basu dawo ba, saida sukaga jirginsu ya tashi suka dawo tare dasu Hadi.
Su Rayyern din kuwa a Abuja sukayi breakfast.
Kana sai ƙarfe huɗu dai-dai na yamma jirgin da zai kaisu China ya tashi.
Acan gidan kuwa Ramadan na dawowa ya tafi aiki, Yayinda Riyyam-nsra kuma kofar gida ya fita wurin Baba Mauɗo.
Su kuwa su Dr.Rayyern Mai-nasara dare ya fara nisa sosai jirginsu ya sauka a.
Beijing Capital International Airport China.
Suna fitowa a jirgi.
PA yace.
“Yah Subahanallahi, tsarki ya tabbata ga Ubangijin talikai mai duniya da ƙiyama.”
Rayyern kuwa limshe idanun sa yayi.
Duk da yazo wurin nan a ƙalla sau biyar.
Amman idanunsa kullum a sabo suke ganin Airport ɗin, sabida masifar kyau da tsananin haɗuwa.
Duk da tsakar dare ne kai kace tsakar ranace, sabida yadda wurin yake da masifar kyau da ƙawatuwa.
Ina in an haɗa Airport's dinmu na Nigeria da nasu tofa ai namu jujine.
Da dan sassarfa suka fito inda zasu samu taxi.
Bayan sun shigane PA yace ya kaisu hotel mafi kusa da Airport ɗin.
Dan campany'n injinun da suke da akalar kasuwancin yana kusa.
Kai PA ya jinjina cikin takaicin Yaren masu idanun kwadin nan wato China sam basu cika gane turanci ba.
Saida Rayyern yayi masa karin bayani da kyau kana ya gane.
Tafiya mai ɗan nisa kaɗan sukayi sai gasu a wani tamfatsetsen hotel.
China world hotel beijing.
Bayan sun sallameshi ne, suka shiga.
Bayan sun kama daki sun, haura wonka sukayi kana sukayi ramuwar sallan magriba da isha'i, kasancewar sunci abinci a jirgi ba yunwa ba kishi ne, yasa kawai suka kwanta dan yin baccin gajiya, saboda tafiya dai ko ya take tafiya ce.
A nan gida kuwa Riyyam-nsra ne zaune gefen Baba Mauɗo yana masa gugan kayanshi.
Yayinda shi kuma yake can gefe,
wayarsa dake kusa da Riyyam-nsra ne ta fara ringing.
Juyowa yayi ya kalli Riyyam-nsra tare da cewa.
“Wake kirana?”
Ido Riyyam-nsra ɗin ya zubawa fuskar wayar cike da mamaki, ya juyo ya kalli Baba Mauɗo kana ya Kuma juyowa ya kalli fuskar wayar.
Hakan yasa Baba Mauɗo yun ƙurowa da sauri, cikin rawan jiki ya jawo wayar tasa.
Da sauri kuma ya juyo ya kalli Riyyam-nsra.
Shi kuwa Riyyam-nsra cikin wani irin kallo mai cike da mamaki yace.
“in...!
*Albishirinku! Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA*
NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA.
Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.
Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke taimakawa (sex hormones 😍) dinki.
Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!?
Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu.
Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki?
Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu,
Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ki zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan.
Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya.
Akwai daya bangaren wato *KAMSHI*
Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, sayan na gari maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia.
Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.
🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA
*(GARKUWAR MA'AURATA)*
By
*GARKUWAR FULANI*
“information”.
Riyyam-nsra ya faɗa yana kallon Baba Mauɗo da ya miƙe tsaye, tare da amsa kiran wayar ya liƙa a kunne.
Ba tare daya kalleshi ba, kuma ya fita parlon.
Yana gab da fitan ne kuma Riyyam-nsra ya kuma zura mishi ido jin yana cewa.
“I always pray for wisdom, domin saida hikima zan iya warware zare da abawan da ake sakawa tsawon shekaru dole saida hiki zan warware, in kuma gano bakin zaren, kana inyiwa ahalin GARKUWA daga ruftawa bisa gadar zaren da magauta ke sakawa.”
Sai kuma ya ɗanyi shiru yana mai jinjina kai.
A ƙalla tsawon daƙiƙu 4 kana cikin yanayin zak’uwa da kaɗuwa yace.
“What are you saying?”
Sai kuma yayi dan jim yana mai gyaɗa kai alamun gamsuwa kana yace.
“You can see me at anytime, saboda mgnar zatafi kyau gani gaka.”
Zare soket ɗin dutsen gugan Riyyam-nsra yayi tare, da juyowa ya fuskanci ƙofar dakin
Kana kuma ya kasa kunnensa da kyau, Yana mai jiyo muryar Baba Maud’on can ƙasa, dan a hankali yake mgnar alamun baya son wani yaji.
Sai dai mamaki mai tarin yawa ne ya rufe Riyyam-nsra, sabida jin yadda Baba Mauɗo yake sarrafa harshensa da ingantaccen turancin da bai taɓa zaton yanajin koda kawo min wuƙa in yanka kabane sabida yanayin shigarsa harcensa suturarsa.
Kana ya gaza gane ina manufar mgnanganun da yake jiyowa, domin daga kan sunan da ya sawa mai kiran ma ya sashi a tunani sannan kuma a take ya tuno hirar da suka tabayi da Ramadan akan Baba Mauɗon.
Shi kuwa Baba Mauɗo, sosai yake mangantuwa.
Har kusan rabin awa yana mgn kana daga bisani ya katse kiran.
Yana shigowa dakin ya kalli Riyyam-nsra da ya ƙarasa gugan yanzu ya tattare wurin.
Cikin yanayin tsare fuska kada yaron yayi mishi wata tambayar, dan ya sanshi surataccen yarone na ƙarshe fuska a ɗan tsare yace.
“Sannu ko Riyyam-nsra Allah yayi maka al'barka.”
Juyawa Riyyam nsra din yayi ya ɗan kalleshi kana yace.
“Amin Baba Mauɗo.”
Ya ida mgnar yana miƙewa da kayan a hannunsa, cikin ɗan madaidacin wordrobe ya shirya mishi su kana ya juyo yana mai cewa.
“Bari inje inyi wonka.”
“Toh sai ka fito ngd ko”
Cewar Baba Maud’o.
Shikuwa Riyyam kai ya gyaɗa kana ya juya ya fita.
Washe gari da dare suna kwance bisa gado shida Ramadan.
Juyowa yayi ya fuskanci Ramadan da kyau.
Tsaki ya ɗan ja ganin har yanzu Ramadan na ruggume da waya, yayi tsit ya nitsu alamun yana jin abinda Rayhanarsa ke zanta mishi.
Ganin hakane ya miƙe ya fita.
A falon ya zauna kana ya danddanan wayarsa, ya kira Mammy tana ɗagawa tace.
“Riyyam lfy kuwa?”
Riyyam-nsra kuwa jin muryarta da alamun bacci takeyi ne, yasa ya ɗan kwaɓe fuska kana a hankali yace.
“Mammy kaina yana kullewafa da lamarin ahlin na.
Akwai fa abinda ke ɓoye fa,
ina son Baba Mauɗo kuma, ina ganin wasu abubuwa daga gareshi, shin baki da wani ƙarin bayani a kan makusantan baya ne!? naji ina mamaki amman fa babu mummunan zatoa kanshi.”
Cikin sauƙe numfashi tace.
“Ka haɗani video call dashi.”
Da sauri yace.
“Toh Mammy zan hadaku in ya yarda.”
Har zata katse kiran kuma yace.
“Ina Zayton?”
“Gata tana bacci”.
Mammy Ta fadi a takaice tare da katse kiran.
Da safe zaune suke a Dinning area,
Jannart na kusa da Mamy suna karyawa.
“Ramadan kayi waya da Rayyern kuwa tunda suka tafi?”.
Mamy ta tambaya.
Tea ya dan kurba kana yace.
“Eh tun ranar da sukaje washe gari, mukayi waya dashi, dazuma kuma muna dawowa masallaci ya kira Abba.”
Kai Mamyn ta gyaɗa tare da cewa.
“Eh haka yace min, Amman ni bai kirani ba yayi kyau ai.”
Riyyam-nsra ne ya ɗan kalli Jannart da tayi kamar bata wurin.
“My Aunty idan kunyi waya kice masa, Allah yasa mutuwa ta manta dani da Mamy, fiye da yanda ya mance damu, tunda mu bazai kiramuba.”
Dariya sukayi baki ɗayansu hatta Jannart, saida ta dara tare da cewa.
“Uhum kishi ko Riyyam-nsra".
A ranta kuma cewa tayi.
“Waya san dani nima”.
A zahiri kuwa ido ta zuba Riyyam.
Baki ya tura tare da cewa.
“Ba wani kishi fisabilillahi Mamy ya mana adalci kenan, yaufa kwanansa biyu fa ace bai neme mu ba.”
Dariyar tsokana Ramadan yayi tare da cewa.
“Toh ku kirashi mana.”
Ya ida mgnar yana miƙewa tsaye tare da kallon agogon hannunsa.
Ganin lokaci ya tafine yasa ya nufi waje, shi ma Riyyam-nsra da sauri ya miƙe yana cewa.
“Yauwa Hamma Ramadan muje ka sauƙeni, a gidan Malam Mai-nasara mana, munyi da Nasir zamu hadu a can.”
“Toh taho mu tafi.”
Ramadan yace
Daga nan suka fita.
Suna gab da fita agidanne kuma, Ramadan ya ɗan leƙo ta cikin motar ya kalli Ari, tare da cewa.
“Baba Mauɗo fa?”.
Ari yana mai ida buɗe musu gate din yace.
“Yau tun sassafe ya fita har yanzu bai dawo ba.”
Da sauri Ramadan yace.
“Ina yaje, meyasa Hadi bai kaishi ba?”
Da sauri Hadi dake gefe yace.
“Wllh nace zan kaishi yace, a'a in bari ba dadewa zaiba, toh kuma gashi har yanzu bai dawoba.”
“Yayi breakfast ne kafin ya fita.”
Ramadan ya kuma tambaya.
“A'a baiyiba".
Ari ya faɗa.
Kai Ramadan din ya gyaɗa tare dajan motar suka fice daga cikin gidan.
Wayarshi ya miƙa wa Riyyam-nsra tare da cewa.
“Kira min shi.”
Toh yace tare da duba number kana ya kira.
Miƙa masa wayar yayi jin an amsa kiran.
“Assalamu alaimun Barka da safiya Baba Mauɗo.”
“Wa alaikassalam Barka dai Ramadan”.
“Baba ina ka tafine yau shiru ban ganka ba.”
Da sauri Baba Maud’o yace.
“Ah gani nan zuwa nazo nan wurin wani ɗan ƙasarmu ne Niger ne zai je gida Agadaz gobe shine zan aikeshi.”
Yana mai taka motar yace.
“Toh sai ka dawo nima na wuce wurin aiki amman ai da ka gaya min da na kaika.”
“A'a ba komai Allah ya bada sa'a.” Baba Maud’on ya fad’a.
Ramadan kuwa da
“Amin.” Ya amsa kana ya katse kiran.
Shi kuwa Baba Mauɗo juyowa yayi ya fuskanci mutanen da yake mgnar da Allah ne kadai yasan kan me suke tattaunawa cikin killace kai sukaci gaba da mgn.
A cikin gidan kuwa, tattare wurin Jannart ta fara.
Mamy kuwa miƙewa tayi ta koma side ɗinsu dan sanin Abba na tsumayin ta.
Tana gama kimtsa wurin ta wuce Bedroom ɗinta dan, bacci takeji kasan cewar in tana cikin halin larura tana yawan jin kasala da bacci.
Bayan Ramadan ya sauke Riyyam agidan Malam Mai-nasara, bai shigaba ya wuce sabida lokacin ya kure masa.
Zaune suke gaban malam Mai-nasara.
Cikin muryar girma yace.
“Zakariyya ya jikin ya'yan naka?"
Kai Riyyam ya d’aga ya ɗan kallesu tare da cewa.
“Jiki da sauki har yayi tafiya ma, zuwa China.”
Da sauri Uncle Mustapha yace.
“Eh lallai haka akayi ai naje dubasa a asibitinsa, da yake ban san gidan nakuba, nan yake cemin zaiyi tafiya in ya dawo zaizo ya duba ka da jiki Malam.”
“Masha allah. Toh Allah ya dawo dashi lfy.”
Cewar Malam da Amin suka amsa.
Nasir ne ya ɗan miƙe tare da cewa.
“Riyyam mu tafi ko.”
Inna ce ta kalleshi cikin tuhuma tace.
“Ku kam baku da aikin yine kullum sai yawo da latse-latsen waya?”
Da sauri Nasir yace.
“Kinfi kowa sanin karatu nakeyi kuma ina gab da hada degree dina, shi kuma Riyyam-nsra yama gama wannan shekarar, kuma aikine yake nema tukun.”
Ya ida mgnar yana haɗe fuska.
Uncle Mustapha kuwa murmushi yayi hakama Malam.
Sukuwa su Riyyam nsra daga nan rijiyar zaki suka nufa gidansu Nasir ɗin.
A falo suka samu babban ya'yan Nasir.
Yah Marwan kasan cewarsa filot ne kwana biyu yana gida.
Marwan yana da sauƙin kai sosai haka yasa suke sakewa dashi,
Bayan Riyyam ya gaida Marwan da Ummansu ne, suka roƙeshi mota.
Miƙawa Riyyam car key din yayi tare da cewa.
“Ku kula da kanku, banda tuƙin ganganci.”
Da sauri suka amsa tare da miƙewa.
Kana suka fita suna cewa.
“Umma sai mun dawo.”
Murmushi tayi tare da cewa.
“Allah ya kiyaye.”
Amin sukace kana suka fice.
Dr.Rayyern Mai-nasara kuwa a ƙasar masu ƙananan idanu, komai yana tafiya bisa tsari yadda yakeso.
Yau kwanansu tara a garin, ya sayi dukkan abun da yake buƙata na campany'nsa.
Sai kuma Engineer bello ya kirashi ya shaida masa suna son wannan karfen 3%, ya zama biyu suka samu domin aje sefiya.
So hakane yasa tashi da shirin zuwa sayansa cikin ingantacen kamfanin kayan ƙarafunan.
Tsaye yake cikin shirin fita PA na tsaye agefensa.
Kiran Mamy ne ya shigo wayarsa da sauri PA yace.
“Mamy ce.”
Yayi mgnar yana miƙo masa wayar.
Amsa yayi tare da karawa a kunne
“Barka da safiya Mamy.”
Ya fad’a cikin kulawa.
A dakile tace.
“Barka dai.”
Ba tare da ta bari yayi mgn ba ta daura da cewa.
“Ka kira Jannart kuwa tunda ka tafi?”
Idonshi ya ɗan jujjuya alamun nazari kana a hankali yace.
“Mamy waye kuma hakan?”
Fuska ta kuma tsukewa kamar yana gabanta tace.
“Ok bari in kaiwa Abbanku wayar sai ya gaya maka waye ita.”
Da sauri yace.
“Dan Allah Mamy ki saki ranki kimin bayani, wlh ban fahimci mgnar kiba,
niba sai kin haɗani da Abba ba, ɗazu ma munyi mgna dashi.”
Murmushi ta ɗanyi a ranta tace.
“Uhum Rayyern halinka sai kai.”
A zahiri kuwa cewa tayi.
“Matarka ce baka saniba yanzu tunda ka tafi sau nawa ka kirata?”
A takaice ba tare da yaja mgnar ba cikin kare kai yace.
“Mamy banda number ta.”
Sai kuma yace.
“Dan Allah Mamy kiyi haƙuri ina zuwa zan kiraki anjima yanzu wani aiki nakeyi.”
Bai jira me zata ceba ya katse kiran wayar, kana ya miƙa wa Usman ita, daga nan suka fito d’aya daga cikin taxi ɗin hotel ɗin, nasu suka shiga kamar koda yaushe.
Kai tsaye Chinese Construction Engineering company suka nufa,
koda suka shiga basu fitoba sai gab da sallan azahar dinsu.
Suna fitowa sukayi salla kana suka shiga taxi ɗin da suka zo dashi dan yana jiransu, tunda batu ne dai na kuɗi daga nan Rayyern yace ya kaisu halal Restaurant.
Tafiyar mai yar tazara sukayi kana suka tsaya, wani babban wuri inda daga can sama aka rubuta HALAL Restaurant's da manyan baki.
Kai RAYYERN ya ɗan juya ya kalli gefen hagunshi kana ya juyo