Showing 66001 words to 69000 words out of 350584 words
matuk’ar d’agamin hankali sama da ciwon Rayyern.
Ciwon Rayyern yana damuna, musamman ciwon cikinsa da Idan ya tashi masa, yakeyin kamar zai rabamu dashi, Tabbas Ina matuk’ar tsoron ranan da ciwon nasa zai tashi, Ina fargaban hakan akoda yaushe, Ina mai kuma addu’a da fatan, Allah ya yayemishi wannan ciwon kai da ciwon cikin, Domin kuwa aduk sanda d’aya daga cikinsu ya tashi, shi kad’ai yasan wani irin zafi da yakeji tunda har yake fidda shi hayyacinsa.”
Abban ya kai k’arshen maganan nasa, cikin raunatacciyar murya, Yayinda idanunsa kuma suka cicciko da hawaye.
Ganin hawaye a idanun Abban ne kuma, yasa Mamy, Ramadan, Riyyam duk sukaji jikinsu yayi sanyi, take kuma idanun Mamayn ma duk suka cicciko da hawaye, kasancewar ta Mace ne kuma, yasa ta kasa controlling hawayen nata, harsaida suka sauk’o kan fuskarta, batare kuma da ta bari kowa yaga hawayen nata ba, ta share da sauri.
Dai-dai lokacin kuwa Baba Maud’o dake tsaye abakin k’ofar shigowa falon, ya d’an d’aga muryarsa wajen yin sallama.
Jin muryar Baba Maud’o dinne kuma yasa, Ramadan mikewa ya k’arasa tare da bud’e kofar, Cikin kulawa yace.
“Baba Maud’o bismillah ka shigo mana.”
Kai Baba Maud’on ya girgiza, tare da cewa.
“A’a basai na shigo ba Ramadan, dama nazo ne na tambaya naji ya jikin Rayyanu.”
Ajiyar zuciya Ramadan ya sauk’e, cikin kuma son kwantarwa da Baba Maud’on hankali yace.
“Jikinsa da sauki sosai Baba Maud’o, yasha magani kuma yanzu haka ma bacci yake, Insha Allah kuma Idan ya tashi daga baccin, zai ji saukin ciwon kan.”
Kai Baba Maud’on ya jinjina, cike kuma da gamsuwa yace.
“Masha Allah! Allah Ubangiji ya k’ara masa lafiya da Nisan kwana mai amfani.”
Da “Ameen.” Ramadan ya amsa, ganin Baba Maud’on ya juya ya tafi ne kuma, yasa shima komawa cikin falon.
Baba Maud’o kuwa Koda ya nufi dakinsa dake cikin gidan, hannayensa yasanya ahankali ya share hawayen da suka gangaro daga Cikin idanunsa, wanda kuma yayi imani cewa, da ace bai bar wajen Ramadan din da wuri ba, To da akan idanun Ramadan hawayen nasa zasu zubo.
_Littafin TUBALI na kuɗine ki biya ki karanta cikin salama special Group 1k ƙaramin group 500 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU sai ki turo min shaidar biyanki ta whatsApp number na 09097853276 ko ki sayi katin MTN ki copy number's din ki turo min ta WhatsApp_
Acan b’angaren su Barrister Kabir kuwa, da wani irin speed suka shiga cikin asibitin.
Wanda kuma suna shiga ko gama parking ba suyiba, aka turo wasu nurses da gado irin maitayannan, su dakansu nurses din suka d’aura Jannart akan gadon, tare da kutsawa da ita cikin asibitin, kaitsaye zuwa emergency.
Suna shigar da ita emergency din kuwa, Dr. Sulaiman, da kuma Dr. Imran, kana da Dr. Fatymah, suka shiga emergency din, tare da duk’ufa akanta, cikin sauri suka soma bata taimakon gaggawa.
Yayinda acan waje kuwa, hankali atashe Barrister Kabir ya karasa receiption na, Hospital din dan bud’ewa Jannart din folder.
Koda yaje kuwa baiwani dau lokaci ba layi ya iso kanshi.
Mai bud’e folder dinne ya dago kansa ya kalli Barrister Kabir tare da cewa.
“Sir me sunan patient din?.”
D’anjim Barrister Kabir yayi, natsawon wasu mintuna, kafun ya dago kai, cikin aminta da abunda zuciyarsa ta yanke yace.
“Sunanta *Jannart Abdulkarim Saleh Dakata.”*
Kai mai bud’e folder’n ya jinjina, tare da maida kansa k’asa ya rubuta abunda yaji mutumin ya fad’a masa.
Yan cike cike yayi cikin abunda bai wuce 5mn ba kuwa, ya bud’ewa Jannart folder acikin Hospital din.
Barrister Kabir kuwa ganin komai ya kammala ne, yasa shi komawa bakin emergency room din ya zauna, tare da sanya hannayensa akan fuskarsa ya zuba tagumi, Tabbas a yanzun abubuwa da yawa ne ke damunsa, amma babban burinsa shine farfadowar Jannart da kuma dawowa cikin hayyacinta.
Acan cikin Emergency room din kuwa, sosai su Dr. Sulaiman suka duk’ufa akan Jannart don ceto rayuwarta, saidai kuma duk yanda suka dauki abun ya wuce nan.
Dr. Sulaiman daya shaida fuskar yarinyar ne ya sharce gumin dake goshinsa, tare da d’auko wani abu mai kaman dutsin guga guda biyu ya manna akan kirjin Jannart din, ganin da yayi batayi motsi bane kuma, yasa shi jin wani irin fad’uwar gaba, saboda sanin da yayiwa abun, sau uku kawai ake dannashi ak’irjin mutum, Idan aka dannawa mutum sau daya, ya farfado ya koma, aka kuma na biyu still bayan ya farfado ya sake komawa, To Idan akayi na uku mutum baiko motsa ba, Lallai alamace dake nuna cewar bashi da rai.
Sake danna mata abun Dr. Sulaiman yayi akan kirjinta, cikin sa’a kuwa yaji taja wani irin numfashi, saidai kuma kafun su ankara numfashin harya koma.
Kallon-kallo sukayiwa junansu, kafun Dr. Sulaiman ya sakeyin shahadan danna mata abun da karfi akan kirjinta.
Wani irin dogon numfashi maikama da shak’uwa taja, tare da mimmik’e jikinta, lokaci daya kuma bugun zuciyarta ya...!
*littafin TUBALI na kuɗine, 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU*
*Albishirinku! Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA*
NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA.
Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.
Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke taimakawa (sex hormones 😍) dinki.
Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!?
Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu.
Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki?
Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu,
Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ki zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan.
Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya.
Akwai daya bangaren wato *KAMSHI*
Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, sayan na gari maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia.
Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki ta karkashi D.H.L. in dai kin cika jakarki baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.
🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA
*(GARKUWAR MA'AURATA)*
By
*GARKUWAR FULANI*
11/15/21, 7:20 PM - Auntyna: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*TUBALI*
PAGE 17
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
*FREE PAGE NE*
*LITTAFIN TUBALI NA KUƊI NE, KI SAYA KI KARANTA BA TARE DA HAKKIN WAHALATA A KANKIBA, SPECIAL GROUP 1K AKWAI KUMA KARAMIN GROUP 500 KACAL A YAWAN POSTING NE BABBANCINSU YAKE, 0661110170 GTBank AYSHA GARKUWA ALIYU, sai ki turo min shaidar biyanki ta whatsApp number na 09097853276, in Kuma baki da halin turawa ta banki to ki sayi katin MTN! MTN!! Mtn!!! Ki copy number's din sai ki turo min ta whatsApp 09097853276. 🙏🏻🙏🏻🙏🏻😭😭😭 Na rokeku da girman Allah da Manzonsa da darajar iyayenku tsarkin al'ƙur'ani mai girma, kada ki karan littafina in baki SAYABA! In kuma kin saya dan soyyarki da Nabiyi rahamati kada ki rink’a fitarmin da littafina, mutanen dake karanta Audio books da masu posting a wasu wuraren kamar Facebook wattpad da kuyiwa girman Allah da isar mulkinsa da soyeyyarku da manzo mu Muhammad Rasulullah, kada ku taɓa min book har sai da izinina ga number wayata 09097853276, ka/kiyi min mgn ta whatsApp in mun dai-dai ta na lamunce miki/ka sai ka karanta ko ka saka domin wannan littafin dama kab sauran littattafai na hakkin mallakarsa nawane ɗan Allah kiyiwa Allah ba danniba sabida bana ɗin tashin hankali da fitina bare akai ga babin hatsaniya🤗🤝🏻🙏🏻😭😭😭*
_Special Group 1k ƙaramin group 500 ne kacal 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU_
Ya harba ya fara aiki.
Ajiyar zuciya Dr. Sulaiman Dr Fatymah, da kuma Dr. Imran suka sauk’e, tare kuma dajin wani irin farinciki saboda, taimakon da Allah ya basu iko da dama wajen iya ceto rayuwar Jannart d’in.
Dr. fatymah ce ta soma treating duk inda Jannart din taji ciwo, bayan ta kammala ne kuma, Dr. Imran yayiwa Jannart din wasu allurai, wanda zasu taimaka mata wajen samun ingantaccen bacci, da kuma k’warin jiki idan ta farka.
Bayan sun kammala yi mata duk wani abunda ya dace ne kuma, Dr. Sulaiman da kansa ya turo gadon da Jannart din ke kwance, zuwa wani d’aki dake gefen Emergency’n na musamman.
Fitowarsu daga Cikin Emergency room dinne kuma, yasa Barrister Kabir ta sowa, cikin sauri ya nufesu, hankalinsa amatukar tashe yace.
“Dr. Yaya ya jikin Jannart din? Dan Allah ku fadamin halin da take ciki, kada ku b’oyemin.”
Ya kare maganan yana me hade hannayensa biyu, waje daya alaman roko.
Dr. Sulaiman ne ya dan matso tare da cewa.
“Calm down jikinta da sauki sosai, Domin da taimakon Allah munyi nasaran samo numfashinta, yanzu dai haka tana dakin hutu.”
Wani irin kakkarfan ajiyar zuciya Barrister ya sauk’e, tare da d’aga hannunsa sama cikin matsanancin farinciki yace.
“Alhamdulillah Allah Nagode ma, Yah Allah ina rokonka da ka cigaba da bawa Jannart kariyarka akoda yaushe.”
Dr. sulaiman kuwa kallon Barrister din yayi, cikin kuma tausasa murya yace.
“Idan babu damuwa zan iya ganinka a office dina, saboda akwai maganar da nakeso muyi.”
Kai Barrister Kabir din ya jinjina, tare da cewa babu wata damuwa.
“Dr muje.”
Hakan kuwa akayi inda Dr. Sulaiman ya shige gaba, shi kuwa Barrister Kabir ya take masa baya.
*Alhaji Idi Saleh Dakata House.*
Dr. Lukman ne ya d’ago da kansa ya kalli Alhaji Idi Sale Dakata dake tsaye, fuskarsa dauke da bacin rai da kuma zallan rashin jin dadin abunda ya faru yace.
“Alhaji Idi Saleh Dakata, kana ga abunda k’aninka yayimin yau, ya hanani duba Jannart, bayan yafi kowa sanin cewar nine likitan da yake dubata tun tana yarinya, kana ga fa har tsawa yayimin wai kada nayi kuskuren tab’a ta, har yana cewa wai yasan abunda nake shiryawa takarkashin k’asa.
To Meya sani kenan? Yanaso yace ban iya aikina bane?”
Dr. Lukman din ya tambaya yana sakin hucin iska.
Shikuwa Daddy hannu ya d’agawa Dr. Lukman di, Domin ayanzu kwata kwata baya bukatar jin korafin kowa, abun dake cikin zuciyarsa kawai ya ishesa.
Wani irin numfashi mai zafi ya fesar, tare da d’agowa ya kalli Alhaji Abdu Tababa, da kuma Dr Lukman din.
“Kuje zan ne meku daga baya.”
Yana gama fad’in haka ya juya, zuciyarsa amatukar hasale ya nufi cikin falonsa.
Ganin hakanne kuma yasa Alhaji Abdu Tababa kama hannun Dr Lukman suka shiga mota, bayan maigadi ya wangale musu gate ne kuma, kaitsaye suka fice daga cikin gidan.
Daddy kuwa Koda ya karasa cikin falon nasa, Sam kasa zama yayi, shi d’ayansa yake ta safa da marwa atsakiyan falon, Yayinda ya had’e hannayensa duka biyu awaje d’aya.
Lallai Tabbas akwai aiki babba a gabansa, wanda kuma dole saiya tashi tsaye.
Babban abunda yake tambayar kansa kuma shine, Tayaya akayi Dr. Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara yagane cewar, shine wanda yasa ake bibiyansa?.
Ya akayi ma yasan gidansa, har tsaurin ido irin na yaron ya kawosa?
Tayaya akayi ya yi wannan saken?
“Wani irin shegen yaro ne wannan? Mai tsaurin ido da taurin kai da rashin tsoro?”
Yayiwa kansa tambayar, yana me sharce gumin daya keto masa.
Dai-dai lokacinne kuma Mom ta shigo, cikin falon, hankalinta amatuk’ar tashe, batare kuma da fahimci din da Daddyn yake ciki ba tace.
“Alhaji Ina Jannart d’in, Ina aka kaita wanni hali take ciki dan Allah ku fadamin.”
Amatuk’ar fusace Daddyn ya juyo, cikin tafasan zuciya ya dann wani tsawan daya saka hanjin cikin Momn kad’awa yace.
“Waya baki izinin shigomin falo kai tsaye? Kifita daga harkata fa Maryam, da kike tambayan Jannart kinfini sonta ne? Ba’ayata bace, Ina ruwanki da inda aka kaita? Ko kece kika haifa min ita? Fice min daga falo, tunkafun na aikata abunda zai bata miki rai!!!”
Daddy’n ya fad’a fuskarsa babu alaman annuri asamanta.
Hakan kuwa shiya sanya, gaba d’aya jikin Mom yayi sanyi, kamar kuma yanda ya buk’ata cikin sauri ta juya ta fice daga cikin falon.
Abdull dake tsaye awaje kuwa ganin Mom nasu tafi to jiki asanyaye ne yasashi rufa mata baya.
Bayan sun isa nasu falonne ya kalli mahaifiyar tasa cikin sharce hawaye yace cewa.
“Ki kwantar da hankalinki Mom, Insha Allah Aunty Jannart ako Ina take Allah zai kula da ita, kuma naga Abba Kabir nema da kansa ya d’auketa, nasan kuma asibiti zai kaita.”
Jin abunda Abdull din ya fad’ane kuwa yasa Mom sauke ajiyar zuciya, lokaci guda kuma taji hankalinta ya d’an kwanta.
Wayarta ta dauka tare da lalub’o lamban Barrister Kabir din, saidai kuma amma kwata kwata wayartasa bata shiga, hakanne kuma yasa ta hakura tare da ajiyewa akan anjima zata sake kira.
*Mainasara hospital*
Cikin yanayin tashin hankali Barrister Kabir ya zauna bisa kujerar dake gaban babban table ɗin dake gaba Dr Sulaiman.
Gyara zama Dr Sulaiman yayi tare da d’an sauk’e numfashi, kana ya fuskanci Barrister Kabir, murya a tausashe yace.
“Babanta ne kai?”.
Cikin sauri Barrister Kabir ya gyaɗa mishi kai alamun eh kawai.
Shi kuwa Dr Sulaiman, kai ya jinjina tare da ci gaba da cewa.
“Kuna sane da cewa tana ɗauke da chronic Asthma, wanda yayi worst sosai ajikinta ko kunsan hakan?”
Kai Barrister Kabir ya jinjina, kana cikin bada tabbaci yace.
“K’warai Dr. munsan da hakan.”
Ajiyar zuciya Dr. Sulaiman din yayi, kamar kuma zaice wani abu saiya fasa, rubutu ya danyi ajikin wata takarda.
Bayan ya mikowa Barrister Kabir din takardar ne kuma yace.
“Way’annan sune magungunan da zata sha idan ta farka, sannan kuma Dan Allah ana kiyaye yawan bacin ranta please dan abubuwan sunyiwa zuciyarta yawa, har ta fara samun raunin harbawar jini.”
Kai Barrister Kabir din ya jinjina, tare da cewa.
“Insha Allah Dr. Nagode sosai, amma ya kake gani shin zan iya zuwa na Ganta kuwa.”
“K’warai kuwa saidai kada kayi wata magana mai karfi da zai disturbing nata, saboda akwai alluran da mukayi mata, wanda akwai buk’atar dole saita huta.”
Kai Barrister Kabir din ya jinjina, tare da mikewa tsaye musabaha suka sakeyi da Dr. Sulaiman din.
Bayan kuma ya gaya masa numbern dakin da Jannart din ke ciki ne ya juya yafice daga cikin office din.
_Dan girman Allah da isarsa masu fitar da littafina da masu karanta na sata da masu karanta Audio books da masu sawa a YouTube da masu posting nashi a wani wurin kuyiwa girman zatin ubangiji daya haliccemu kada ku taɓamin. Littafina sai kunmin mgn kun saya na lamunce muku ku, dan kin biya 1k ko 500 bawai kuɗin mallakarsa kika biyaba, kudin samun damar karantawa ne 09097853276, ga number' ta, in Kuma zaki sayane ga ac no dina 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU_
Kaitsaye dakin da aka kwantar da Jannart din ya nufa,
Koda ya shiga tura kofar dakin yayi, inda ya Sameta kwance tana