Showing 165001 words to 168000 words out of 350584 words

Chapter 56 - Tubali Book 1 Hausa Novel Complete

za’a samu, a hospital din nasa, domin zasuje suyi course dinne, akan abunda ya shafi dashan k’oda, dana zuciya aikin ƙwaƙwalwa da juyen jini ga masu cutar sikila uwa uba da safarar tunanin kwakwalwar ɗan Adam, dama dai sauransu, kuma Insha Allah zasu kawowa K’asa cigaba.”

Idanu Dr. Lukman ya d’an zazzaro, cikin bakinciki takaici da kuma kunci yace.

“Wallahi kwata-kwata Barrister bani da wannan labarin, kuma ai wannan plant din nima, najima da tsarashi azuciyata, wanda kuma nakeso na aiwatar acikin hospital dina, amma kuma sai next year nakeson haka, why? Why? Wannan yaron ya shigemin hanci, komai zanyi saiya rigani kafin ma in tuna abu shi yayi, na shiga uku Anya zai barni na ci gaba arayuwata kuwa?”

Dr. Lukman din ya fad’i haka cikin tashin hankali, saboda ya fahimci cewa, duk saurinsa Dr. Rayyern din yana gaba dashi akan komai.

Boyayyen Murmushi Barrister Kabir yayi, tare da maida kansa ya ajiye ajikin kujera, yayi hakanne kuma saboda yanda yaga, hankalin Dr. Lukman din ya tashi sosai.

Alhaji Bala Tambari kuwa, gyara zamansa yayi...!



*Albishirinku! Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA*

NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA.
Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.

Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke taimakawa (sex hormones 😍) dinki.
Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!?
Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu.
Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki?
Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu,
Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ki zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan.
Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya.


Akwai daya bangaren wato *KAMSHI*
Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, sayan na gari maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia.

Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.

🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA
*(GARKUWAR MA'AURATA)*


By
*GARKUWAR FULANI*


Tare da fuskantarsu dukansu, cikin dan nisawa yace.

“Gaba d’aya matsalarmu a kullum akan Dr Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara ne, wanda kuma ni kaina bani da iko, ko wani matsayi da zan iya dakatar dashi akan abunda ya saka agaba, saboda duk wani k’a’ida da dokokin da akebi ya bisu, Idan kuma har nace zan wargaza masa tsari.
To tabbas zai iya Kai k’arata wajen na sama dani, hakan kuma zai iya sawa na rasa aikina, yaron ya wuce duk yanda muke tunani, kowacce hanya da zamu b’ullo masa ya sani, kansa yana ja sosai, babban abunda na lura dashi kuma shine, kwata kwata baya tsoron magautansa yaron yana nan Tamkar a haifeshi ne domin daukan fansa!!!.”

Numfashi mai nauyi duk suka ja, musamman Alhaji Idi Sale Dakata wanda gaba daya abubuwa suka had’e masa.

Ga zafin b’atan Jannart ga kuma, na wannan shegen yaron Dr. Rayyern.
Barrister Kabir kuwa, kalaman Alhaji Bala Tambari na karshe yaketa nanatawa a zuciyarshi don son fahimtar wani abin.

Haka dai taron nasu ya watse gaba d’aya zuciyar Alhaji Idi, da kuma na Dr. Lukman Alhaji Abdu Tababa babu dadi, kowannensu kuma saboda Rayyern.

Dr. Lukman din, da kuma Alhaji Abdu Tababa ne suka had’a hanya wajen tafiya, haka ma Alhaji Bala Tambari shima tafiya yayi.

Hakan yasa falon ya rage daga, Daddy sai Barrister Kabir.

Juyowa Alhaji Idi Sale Dakata’n yayi? Ya fuskanci Barrister Kabir, cikin kuma nuna halin damuwa yace.

“Kabir ayanzu babu abunda yake damuna, kamar b’acewar Jannart, har yanzu babu wani labari, kwata kwata ayanzu ma ba batun companyn Rayyern Mai-nasara bane ke damuna, matsalar b’acewar Jannart itace ke damuna hukuma suna iya yinsu abin yaci tura.”

Afakaice kuma ta k’asan idanu, Barrister Kabir ya kalli Yayan nasa, tare da d’an ya mutsa fuskarsa.

Wanda kuma daga wajen Alhaji Idi Sale Dakata’n ma hakan yake, domin kuwa bayan yayi maganar shima, ta k’asan idanu, ya kalli K’anin nasa, tare da sakin wani Shu’umin murmushin, da shi kad’ai yasan ma’anar yinsa.

Barrister Kabir kuwa, mur yasha tare da saka fuskar tsare gida, irin tasu ta lawyoyi, saboda shima akwai wani abu daya gano amatsayinsa na lawyer.

Shi yanayiwa Barrister Kabir kallon biri, shi kuwa Barrister Kabir yanayiwa yayan nasa kallon Ayaba.

Koda suka fito daga d’akin taron Alhaji Idi Sale Dakata’n, main falon gidan suka dawo, inda suka samu Momy ta gama had’a abinci.

Sama sama haka Barrister Kabir yaci abincin, bayan sun kammala ne kuma yayiwa Yayan nasa sallama, kaitsaye kuma daga gidan Alhaji Idi Sale Dakata’n, gidansa ya nufa.

Koda ya isa gidan afalo ya samu Dijat.

Hira kadan suka tab’a kana kaitsaye ya wuce bedroom d’insa.
Key ya sawa kofar bedroom din, tare da komawa ya zauna, bayan ya d’auko wasu takardu.

Anutse yake wargaza takardun, tare da Ware wasu daga ciki yana duddubawa.
D’ago wata takarda da yayi ne kuma, ya sashi tsurawa rubutu, da kuma hoton passport din dake jiki idanu.

*** ***

Almost 4weeks kenan yanzu da, dawowar Rayyern daga China, Alhamdulillah kuma jikinsa ya warware.

Bisa taimakon Ramadan da kuma Jannart, way’anda suke kula da shan maganinsa.

Hakan yasa ciwon cikin nasa yayi sauki, ya kuma gama samun karfin jikinsa, duk da cewar time to time ya kanji, ciwon cikin na tashi masa, amma da yasha magani yake jin sauki.

Ahankali yake sauk’owa daga kan matattakalan falon, inda yayi kyau cikin shigar Ash colour suit dake jikinsa.

Yayinda hannunsa ke rik’e da briefcase, da alama kuma aiki zaije.
Ya dawo asalin Rayyern d’insa, big man wanda bai wani cika son wasa ba, wani Rama da yawan kasalan da yakeji ada, duk sun kama gabansu.

Mamy dake tsaye akan dining table, jin alaman takun takalmansa ne yasa, ta d’ago kanta ta kalleshi.

Ganin yanda yayi kyau ne kuma, yasa Mamyn sakin murmushi, Cikin kulawa tace.

“Babana yadai, yau na ganka cikin shiri haka fita zakayi ne?”

Kansa ya jinjina, adaidai lokacin da yake gama sauk’owa daga kan steps din yace.

“Eh Mamy yau zanje company.”

Murmushin dake kan fuskar Mamy ne ya fad’ad’a, cikin jin dadi tace.

“Ah Lallai Masha Allah Babana ya samu sauk’i, amma Ina fatan kanajin karfin jikinka sosai.”

Idanunsa ya d’an lumshe tare da jinjina mata kai alaman. “Eh.”

“To kayi breakfast tukun kafun ka tafi.”

Mamyn ta fad’a tana me nuna masa kujera, tare dayi masa alama akan ya zauna.

Fuskarsa ya d’an shagwab’e, kamar zaice a’a kuma saiya zauna.

Dai-dai lokacin kuwa Jannart ta shigo cikin falon, sanye take da riga da wando ajikinta, saidai wandon irin mai fad’in nan ne, haka ma rigar Wacce take da igiyan d’aurewa, hakan ne kuma yasa lafaffen cikinta bayyana, saboda yanda ta d’aureshi da igiyan, haka ma shape din cikin nata ya bayyana sosai.

Kasancewar kuma kayan nada kalan baki, shiyasa ta yafa siririn mayafi daga kanta zuwa wuyanta.

Sassanyan kamshi take bazawa, shigowarta cikin falonne kuma yasa shi sauk’e idanunsa akanta.

Mamy kuwa Ganin Jannart dinne yasa Cikin kulawa tace.

“Yauwa Jannart yi saving din mijinki mana, yana sauri zai tafi wajen aiki ne.”

Kai Jannart din ta d’an sunkuyar k’asa, cikin yanayin nutsuwa tace.

“To Mamy.”

Kaitsaye dining table din da yake zaune ta nufa, saidai koda wasa bata bari sun had’a idanu ba.

Koda ta k’arasa inda yake, plate ta d’auka tare da bud’e food flask, cikin sanyin muryar dake bayyana nutsuwarta tace.

“Ina kwana.”

“Lafiya.”
Ya amsa mata atak’aice, tare da zubawa kyawawan fararen yatsunta idanu.

Abincin ta zuba masa, bayan ta kammala ne kuma ta turo masa plate din gabansa.

Tare da saka masa apple juice din da ta had’a, acikin wani d’an glass cup.

Ahankali ya soma cin abincin, tare kuma da dan lullumshe idanunsa, saboda yanda yake jin kamshinta na shiga hancinsa.

Jannart kuwa Ganin ya fara cin Abincin ne, yasa ta wucewa kaitsaye ta nufi sama, Dan d’auko maganinsa.

Ahankali ta tura kofar d’akin ta shiga.
Lumshe Idanunta tayi saboda, wani irin kamshi daya bugeta.
Ga kuma sanyin ac dake busa ko ina.

Dan bud’e Idanunta tayi, tare da soma bin ko ina dake cikin dakin da kallo, komai nasa need babu alaman datti, duk da cewar ya kwana acikin dakin, amma saida ya gyara komai kafun ya fita.

Hakanan kawai ta samu kanta da sakin murmushi, kaitsaye kuma cikin nutsuwa, ta wuce ta dauko magungunan nasa.

Koda ta sauk’o k’asa harya kammala cin abincin nasa, saidai juice dinne da bai gama shaba, wanda kuma yake sipping d’insa ahankali.

K’arasowa kan dining table din tayi, Anutse ta b’are magungunan tare kuma da zuba su acikin tafin hannunta.

Kallonsa ta d’anyi, tare da mik’a masa magungunan, alaman ya karb’a.

D’ago idanunsa yayi ya kalleta, cikin yanayinsa daya saba yi mata magana yace.

“Ni yaro ne, da har sai kin b’aremin magani, ni bazan iya dakai na bane akace miki? Sai kiyi ta wani ɗuɗɗuramin magunguna babu ko tausayi”

Idanunta ta d’an janye daga kallonsa, saboda ayanzu babu wani abu nasa da bata sani ba, saikayi masa abu sau goma, amma baya tab’a gani yanzu zai gwatsaleta ta fahimci zarginta yakeyi ma shi.

K’wayoyin idanunta tad’an juya ahankali, sau d’aya kuma cikin sigar lallashi tace.

“Okay I’m sorry take it.”

Hararanta ya d’anyi ta k’asan idanunsa, sanin Mamy na cikin falonne kuma yasa shi, bud’e tafukan hannunsa, Anutse ta zuba masa maganin ahannunsa, gudun kada hannunta da nasa su had’e, tayi hakanne kuma saboda, ita kadai tasan me takeji, aduk sanda ta tuna lokacin da fatar hannunsa ya tab’a nata.

Rayyern kuwa bayan yasha Maganin ne ya mik’e tsaye, tare da d’aukan briefcase d’insa, cikin sauri yace.

“Mamy na tafi saina dawo.”

“A dawo lafiya Allah ya bada sa’a.”

Mamyn ta bashi amsa, Cikin kulawa.

Da “Ameen.”
Ya amsa kana ya sakai ya fice daga cikin falon.

Ganin hakanne kuma yasa Jannart dawowa, kusa da Mamyn ta zauna.

Shikuwa Rayyern yana fita kaitsaye company ya wuce,
Koda yaje kuwa ya samu ma’aikatan nata aiki, kowa na aikinsa kamar yanda ya dace.

Gaba d’aya ma’aikatan sun bada himmansu wajen yin aikin tsakani da Allah.

Domin har anfara har had’a cattoon's din abubuwa, wanda kowanne kwali d’auke yake da sunan tambarin.
MAI-NASARA.

Komai Yayi masa sosai, hakanne ma yasa shi jinjina kansa, kaitsaye kuma ya wuce office d’insa dake nan cikin companyn.

Wasu d’an aikace aikace yayi, bayan ya kammala ne kuma ya fito, kaitsaye hospital d’insa ya wuce.

Bashi ne ya dawo gidan ba kuwa sai k’arfe 10:00 pm dai dai.
Hakan ya faru ne kuma saboda tsayawa da yayi, yiwa wata operation, baya ga haka kuma, ya tarawa kansa aiki sosai, wannan dalilin yasa shi tsayawa, ya d’an rage ayyukan.

K’asa k’asa ya danna Horn din motar tasa, cikin abunda bai wuce mintuna 2 ba kuwa, aka wangale masa gate din gidan.

Anutse ya tura hancin motar ciki, bayan yayi parking motar ne kuma ya fito.

Tare da Kallon Baba Maud’o wanda shine ya bud’e masa gate din.

“Baba Maud’o da kanka, ai daka bari na fito na bud’e, sam banaso naga kana wahalar da kanka, saudayawa Idan naga kana wannan aikin sai naji duk babu dadi, please Baba Maud’o ka bari.”

Rayyern din ya fad’i haka ga Baba Maud’o cikin tausasa harshe.

Baba Maud’o kuwa Murmushi yayi tare da d’an gyara tsayuwarsa, kana Cikin kulawa yace.

“Haba Rayyern meye na damuwa kuma, bayan kasan hakan aikina ne, kuma gashi Ari yayi bacci shiyasa.”

Fuska Rayyern din ya d’an kwab’e, hade da karyar da wuyansa yace.

“Ni dai Baba Maud’o da gaske banason hakan, banajin dadi Idan naga kana bud’e gate inajin wani nauyi a zuciyata.”

Murmushi Baba Maud’o yayi, tare da komawa wajen zamansa ya zauna.

Ganin hakanne kuma yasa Rayyern d’in ma, matsawa ya zauna akusa da Baba Maud’on.

“D’azu Barrister Kabir yazo dubaka da jiki, amma baisame ka ba, saidai yace agaisheka.”

Baba Maud’o ya fad’a yana me Kallon Rayyern din.

Shikuwa Rayyern Ajiyar zuciya ya sauk’e, tare da d’an mammatsa hannunsa.
Cikin kuma taushin murya yace.

“Ina amsawa, bari na shiga ciki Baba Maud’o, yau duk na gaji aikin office ya gajiyar dani.”

“To Rayyern Mukwana lafiya.”

Da “Ameen.”
Rayyern din ya amsa, tare da wucewa ciki kaitsaye.

Koda ya shiga main falon nasu babu kowa, hatta su Ramadan da Riyyam nsra duk suna daki.

Kaitsaye kuma shima d’akin nasa ya nufa.
Yana shiga kuwa ya soma rage kayan jikinsa.

Bayan ya shiga toilet yayi wanka ne kuma, ya shirya kansa cikin lallausun kayan bacci.

Bayan yasha Nutri milk ne kuma ya koma kan gado ya kwanta.

Kasancewar agajiye yake ne kuma, yasa yana kwanciya bacci ya d’aukesa.

Washegari.

Arewa24 tv station.

Aunty Fauziya ce ke tafe cikin d’an sauri, saidai kallo d’aya zaka yiwa Fuskarta, ka fahimci cewa tana cikin yanayin damuwa.

Fitowarta kenan kuma daga dakin yad’a labaransu, sukayi Karo da Salman.

Kallonta Salman din yayi, Ganin damuwa afuskarta ne kuma yasa shi d’an tsayawa, Cikin kulawa yace.

“Aunty yadai naganki haka, wani abu ya faru ne?”

Kai ta d’an girgiza, cike da damuwa tace.

“Salman b’acewar Jannart ke damuna, tayaya za ‘ace mace kamar Jannart ta b’ace b’at kamar kud’i? hankalina yana tashi sosai Salman, ka duba dai irin jami’an tsoron da Babanta ya bawa cikiyar nemo ta, ga kuma mu da kullum sai munsa cikiyarta, amma har yau babu wani wanda yace ya ganta, abun yana min ciwo Salman, ga mahaifinta asanadin haka ko lafiyar kirki bashi dashi, kwanan nan naji har India aka fita dashi, duk kuma akan lamarin b’acewar Jannart, Ina cikin damuwa akan hakan.”

Ajiyar zuciya Salman ya sauk’e.

Dai-dai lokacin kuwa Asiya tazo ta wucesu, saiwani karairaya takeyi tamkar zata b’alle.

Ganin hakanne kuma yasa Aunty Fauziyan wucewa office dinta, take kuwa Salman ya rufa mata baya.

Koda suka isa cikin office din zama, duk sukayi, ananne kuma Salman ya d’ago ya kalli Aunty Fauziyar.

Cikin sanyi ya d’an gyara zamansa tare da cewa.

“Gaskiya da banyi niyan fad’awa kowa ba saboda sirrine, saidai ke naga gaba d’aya hankanlin atashe yake, akan b’atan Jannart, amma Dan Allah duk wata magana da zan fad’a miki inason ta zama sirri.”

Nisawa Aunty Fauziya’n ta d’anyi, tare kuma da fuskantar sa tace.

“Kafad’i duk abunda kakeson fad’a Salman, Insha Allah bazan gayawa kowa ba, kasanni kasan koni wacece zan rik’e duk wani sirri.”

Kai Salman din ya jinjina, tare da dan gyara zamansa kana yace.

“K’warai nasan hakan Aunty Fauziya, nasan ke ta musamman ce shiyasa ma na yanke shawarar sanar dake, danki cire wannan damuwar dake zuciyarki, agaskiya Jannart ba b’ata tayi ba.”

Idanu Aunty Fauziyan ta tsura masa cike da mamakin, Jin abunda ke fitowa daga bakinsa tace.

“Kamar yaya Salman ka warwaremin maganar ta yanda zan fahimta.”

“Jannart ba wai b’acewa tayi ba, K’anin Babanta Barrister Kabir shi yayi mata aure, batare da sanin kowa ba, yace kuma yayi hakanne saboda wani dalili nasa maik’arfi, wanda kuma acewarsa hakanne kad’ai zai tseratar da rayuwarta, daga fad’awa koman magauta masu farautar rayuwarta.”

Wani irin gauron Ajiyar zuciya Aunty Fauziyan ta sauke, duk da cewar taji mamakin maganan k’warai, amma


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login