Showing 156001 words to 159000 words out of 350584 words
tausayinsa da taji, sanin kuma halin marassa lafiya da kin son cin abinci ne yasa, cikin tausasawa da kuma kwantar da murya tace.
“Bazaka sha ba?”
Kansa ya kuma jinjina mata, alaman “Eh.”
“To Meyasa?” Ta tambayeshi da wata irin murya, kana kuma cikin yanayin da ita kanta batasan tayi ba.
Fararen hakwaransa yasa ya dan danne lipsl d’insa, cikin wata iriyar fitinenneyar murya yace.
“Banaso!! Bsnaso! banassso!!!”.
Idanu ta zuba mishi tana mai jin yadda tsikar jikinta ke zubawa sabida yadda yayi mata mgnar like ɗan yaye mai shogoba.
Kai ta ɗan kwantar kana cikin murya da bata san ta yaya ya ziyarci harcentaba tace.
“Bakason me?”.
Kwaɓe fuskarsa tayi tamkar zaiyi kuka yace.
“Banason tea me madara empty zaki baneeee.”
Yayi maganar cikin sake yin kasa da murya, saboda gaba daya baya wani jin dadin jikinsa, ga kuma rashin karfi dake damunsa, wanda hakan yasa maganan ma wahala yake basa.
Jannart kuwa jin abunda ya fad’ane yasa, ta d’an kwantar da kanta gefe, tare kuma da Kallon kayan tea din da ta shigo dashi.
Ajiyar zuciya ta d’an sauk’e, kana cikin sanyi tace.
“To bari naje na d’auko wani cup, saina had’a maka empty din.”
Ta k’are maganan tana me mik’ewa tsaye,batare kuma da ta jira wani abuba kaitsaye ta fice daga Cikin d’akin.
Direct falon nasa ta dawo, harta kawo bakin kofar fita daga falonne kuma sai ta hango, kofar dake gefe da dining area d’insa, da dukkan alama kuma nanne kofar kitchine din dake Cikin falon nasa.
Ahankali ta k’arasa jikin kofar tare da turawa ta kutsa kanta ciki.
Idanunta tad’an ware saboda ganin yanda kitchine din nasan ya tsaru, da komai na zamani, domin wani irin kitchine carbinet akayi na musamman acikinsa, ga kuma plates da cups hadi da sauran kayan aiki masu kyau kana Kitchen din nada girma ga kuma kofar store ta ciki.
Jinjina kanta tayi saboda yanda ta yaba da kyawun kitchine din.
Wani cup ta d’auka tare da k’arasawa gaban sink ta wankesa.
Juyowa tayi Anutse ta dawo cikin d’akin.
Yana nan zaune a inda ta barsa dan ko motsawa baiyi ba, saidai idanunsa daya sake lumshewa.
A ranta tace.
“Ga kafiya faɗa ga kuma raki da sakalci”.
D’an durk’usawa tayi, agaban stull din tare da d’aukan lipton ta saka acikin cup din, sai kuma k’wayan shugar guda hud’u da ta d’auka acikin k’wali, bayan ta saka shugar’n ne kuma ta saka ganyen lemongrass leaves wanda already dama tazo dashi akan tray din, murfin flask ta bud’e tare da zuba ruwan zafi acikin cup din, kana tasa cokali tadan jujjuya.
Ganin sugar din ya narke ne kuma yasa ta, d’ago cup din tare da mik’a masa cikin kulawa tace.
“Gashi.”
“Ki ajiye.”
Yafad’a agajarce tare kuma da gyara zamansa, wanda kuma daga yanayin maganarsa kad’ai zaka fahimci cewar bayajin dadin komai.
Ajiye cup din tayi agefensa kamar yanda ya fad’a. Cikin nutsuwa kuma ta mik’e tsaye, tare da d’aukan tray din.
Ahankali batare kuma da ta sake ce masa komai ba, ta juya ta fice daga cikin dakin, tare da mayar masa da kofar ta rufe.
Kaitsaye k’asa ta nufa.
Shikuwa Rayyern jin alamun fitanta ne yasa shi sake lumshe idanunsa.
Ahankali ta gama sauk’owa daga kan steps din.
Ganin babu kowa acikin main falon ne kuma yasa kaitsaye ta wuce kitchine.
Dan aciki ne takejin motsin Mamy.
Tana shiga kuwa ta samu Mamyn nata aikace aikace.
“Sannu da aiki Mamy.”
Ta fad’a tana me ajiye tray din dake hannunta.
Mamy kuwa jin muryar Jannart abayanta ne yasakata sakin murmushi, cike kuma dajin dadin d’an jimawan da taga Jannart din tayi a sashin Rayyern din tace.
“Yauwa sannu dai Jannart.”
K’asa Jannart din ta d’anyi da kanta, kana anutse tazo kusa da Mamyn tare da k’arb’an aikin da Mamyn keyi ta soma Taya ta.
Hakan yasa cikin yan mintuna suka kammala had’a komai na breakfast.
Bayan sun zuba komai acikin food flask ne kuma, Jannart takai kulolin kan dining Table.
Mamy kuwa na Abba ta d’auka takai masa zuwa part d’insa.
Dai-dai lokacinne kuma Ramadan da Riyyam nsra suka shigo.
Jannart dince ta bawa Riyyam nsra food flask din su Baba Maud’o ya Kai musu.
Koda ya dawo kuwa anan falon suka zauna su dukansu, atare sukayi breakfast, inda suna cin abincin Riyyam-nsra nata zuba musu surutu, wanda kuma bashi da wani labari saina y’an tiktok.
Suna ahaka ne kuma Dr. Sulaiman da kuma Baba Maud’o suka shigo cikin falon.
Fuska d’auke da fara’a suka gaisa, dasu Mamy dai-dai lokacin kuwa Abba ma ya fito daga nan part d’insa.
Bayan Abban sun gaisa da Dr. Sulaiman ne kuma yayi musu jagora zuwa sama.
Ahankali Abba ya tura kofar dakin Rayyern din ya shiga bakinsa dauke da sallama, Yayinda su Baba Maud’o ke biye dashi abaya.
Rayyern dake dan kishingid’e kuwa jin muryar Abban nasa ne, yasa shi dan yunkurawa ya tashi zaune.
Akusa dashi Abba da Baba Maud’o suka zauna, cikin kulawa Baba Maud’o yace.
“Rayyern ya jikin naka?”
Murmushin karfin hali ya d’anyi, tare da gyara zamansa, kana cikin tausasawa yace.
“Alhamdulillah jiki da sauki Baba Maud’o.”
Kai Abba da Baba Maud’o suka jinjina, cikin kuma danjin dadi suka had’a baki wajen cewa.
“Allah ya baka lafiya.”
Da “Ameen.” ya amsa.
Inda Dr. Sulaiman kuwa ya zauna akan bedside drawer, cikin nuna kulawa ga abokin nasa yace.
“Sannu Dr Rayyern ya jikin naka? da Fatan ka d’anji k’arfin jiki.”
Idanunsa ya d’an lumshe kana Ahankali yace.
“Alhamdulillah, nasan komai zai dawo dai-dai soon.”
“Insha Allah, amma fa kasan dole saika dage, musamman wajen cin abinci, domin yanzu ma haka akwai magungunan dana kawo ma, amma dole sai kaci abinci kafun kasha su.”
Cewar Dr. Sulaiman yana me fito da wasu magunguna daga aljihunsa.
Rayyern kuwa Ganin magungunan ne yasa shi d’an yamutse fuska, tare da komar da kansa ya kwanta.
Sanin da sukayi cewa Koda lafiyarsa, bayason yawan surutu, bare kuma yanzu da bashi da cikakken lafiya ne, yasa su mik’ewa tare dayi masa Allah ya sauwake, kana duk suka fice daga cikin dakin, Dan ayanayin da suka gansa kamar ma bacci yakeson yi.
Atare suka sauk’o k’asa dukansu.
Anan cikin falon suka zauna, inda Dr Sulaiman ya d’ago kansa ya kalli Mamy.
Cikin girmamawa yace.
“Mamy akwai wasu magunguna dana kawowa Rayyern, To amma kuma dole akwai buk’atar sai yaci abinci kafun yasha su, saidai kuma na lura kwata kwata Rayyern bayason cin abinci.”
Ajiyar zuciya Mamy ta sauk’e, cikin kuma yanayin sanyi tace.
“To ya zamuyi Sulaiman, kafasan halin Rayyern komai nasa dabanne dana kowa, amma Insha Allah Zamuna kokari akan cin abincinsa.”
Kai Dr Sulaiman din ya jinjina, domin kuwa yasan halin Rayyern din Sarai.
Jannart kuwa dake zaune anan dining table din, ahankali ta ajiye spoon din dake hannunta, tare kuma da d’aukan tissue ta goge bakinta.
Ganin alaman ta kammala cin abincin ne kuma yasa Mamy, kallonta cikin kulawa tace.
“Yauwa Jannart tunda kin kammala cin abincin naki, ga food flask nan d’auka ki kaiwa Rayyern nasa abincin, ki kula dan Allah ki sashi ya d’anci ko kad’anne, sai ki bashi magungunan kinji.”
Mamyn ta k’are maganan cikin sigar kulawan, da tasaka Jannart yin kasa da Kanta.
Ahankali kuma Cikin nutsuwa tace.
“To Mamy.”
Mik’ewa tsaye tayi, tare da gyara mayafin dake jikinta, kana ta d’auki d’an tray ta saka food flask da kuma cups, din da aka gama had’a masa duk breakfast din nasa aciki.
Cikin nutsuwa da kuma d’abi’arta na hankali kaitsaye ta nufi saman.
Ganin tafiyan Jannart dinne kuma, yasa Ramadan d’an gyara zamansa, tare da fuskantar su Abban nasa, cikin tausasawa da kuma yanda yasan zasu fahimcesa yace.
“Alhamdulillah wannan karon ba ayiwa Hamma Rayyern allura ba, saboda likitotin China sun sanja masa magani, wanda iya maganin ya wadatar basai an had’a masa da wannan, alluran mai matukar kashe jikin ba, sun kuma ce typhoid ne ke causing stomach pain din nasa, wanda kuma dama tuntuni munsan cewa akwai cronic typhoid ajikinsa, wanda ayanzu harya fara tab’a masa hanjinsa, shiyasa ma yake yawan sa masa ciwon ciki, amma yanzu likitotin can din sun bamu magunguna wanda, zasu na taimakawa wajen wanke masa hanjin nasa, dama kashe duk wata cuta dake cikinsa,
shiyasa ma suka sallamemu, amma hakan fa bawai yana nufin shikenan bane, sunce akwai yiwuwar dole za’ayi masa aiki, amma Idan anyi dace, magungunan zasu iya wanke duk wani cuta dake damunsa, Insha Allah zai samu sauki, akwai watarana na zuwa da Hamma Rayyern zaiyi bankwana, da wannan ciwon bazai sakeyi ba da Yardar Allah.”
Ajiyar zuciya duk su Abba da Baba Maud’on suka sauk’e, saboda bayanin da Ramadan din yayi musu, yasa sun samu gamsuwa sosai.
Cikin samun nutsuwar zuciya Abba yace.
“Allah yasa Ramadan, Allah Ubangiji ya yayewa Rayyern wannan ciwon, Insha Allah ma basai anyi masa aikin ba nasan zai warke, ai waraka ta Allah ce.”
“Sosai kuwa, da yardar mai duka watarana komai zai wuce, Allah dai ya yaye masa.”
Cewar Baba Maud’o.
Da “Ameen.” Duk suka amsa.
Inda Ramadan kuwa ya gyara zamansa, tare da sake Kallon su Abban nasa murya araunace yace.
“Amma Abba fa Doctors din sun tabbatar mana cewar, harda yawan shan zak’in da yake ma, domin shi zaki kana shansa yana taruwa maka aciki ne, bazai tashi yi maka illa ba kuwa, sai ya samu wani ciwon dazai tashi maka, zai iya had’ewa da wannan ciwon ya cutar dakai, batare da kasan da hakan ba, kuma shi kansa Hamma Rayyern ya sani, amma bansan yaushe ne Hamma Rayyern zai sanja ba, bansan yaushe ne zai daina maida abun zaki abun sonsa ba.”
Shiru duk su Abban sukayi saboda acikinsu babu wanda baisan halin Rayyern dason zaki ba sai dai sun sani laifinsune sune suka rainesa da zaƙin dan yawan soyyaya.
Saidai Abba ya kud’urtawa ransa cewar.
“Insha Allah zai dage tukuru wajen ganin ya raba Rayyern din, da yawan shan zakin da yakeyi.”
Haka dai suka d’an tattauna, kafun daga bisani Abba da Baba Maud’o suka fice, haka shima Dr Sulaiman.
Acan b’angaren Jannart kuwa ahankali, ta murd’a handle din kofar ta shiga bakinta d’auke da sallama.
Kwance yake akan lallausan gadonsa, Yayinda yayi kwanciyarnan irin ta rub da ciki.
Jin sautin muryarta ne kuma yasa shi, lumshe idanunsa dake bud’e.
Ita kuwa Jannart k’arasa shigowa cikin d’akin tayi, tare da ajiye tray din dake hannunta.
D’an Kallon yanda ya bawa kofar shigowa dakin baya tayi, cikin sanyi da kuma tausasa murya tace.
“Ga abincinka nan.”
“Nak’oshi.”
Ya fad’a atakaice saboda ayanzun Sam bayason takura.
“Katashi kaci abinci inji likita.”
Jannart din ta fad’a tana me bud’e food flask din, tare da d’aukan spoon ta zuba Coastarian breakfast dish din, gyara zaman plate din akan table tayi, tare da d’ago da Kanta ta kalleshi.
“Please ka tashi, Mamy ne tace kaci abinci sai kasha magani kaji ko.”
Tayi maganan cikin sanyin murya, da kuma zallan yanayin shagwab’an da ita kanta batasan tayi sa ba.
Idanunsa ya d’an rumtse ahankali, tare kuma da sa hannayensa duka biyu, ya sake matse pillow’n dake kirjinsa.
Kwata-kwata bayason yawan damuwa, bawai kuma dan bayajin yunwa ba, no kawai dai bayason yaga Jannart din akusa dashi har haka ne, musamman ayanzu daya fahimci wani abu, adangane da ita, shine tana da wani special Mood wanda yafahimci ita kanta batasan tana dashi ba tana kuwa yiwa zuciyarsa raraka.
Sake gyara kwanciyarsa yayi, cikin kuma nuna halin ko inkula yace.
“Kije zanci.”
Idanunta ta d’an zubawa faffadan bayansa, tare da kama waist dinta ta rik’e, dama tasan halinsa, ta kuma san cewar bazai tab’a daina wa ba.
“Nifa bawai na wani damu dakai bane, Dan kawai kaga Ina baka attention dina, saboda baka da lafiya ne kawai Malam, baya ga haka me mazaisa nazo wajenka.”
Ta fad’i hakan acikin zuciyarta, tare kuma da murgud’a bakinta gefe.
“Da kika tsuramin ido haka wani abu ne zaki bani? Ko cinyeni danye zakiyi!?”
Rayyern din ya fad’a, batare daya juyo ba.
Saurin kawar da kanta gefe tayi, tare da turo dan karamin bakinta gaba, cikin yanayin Mood din shagwab’a tace.
“Ni ai ba kallonka nake ba kuma ba kai nake kalloba”.
A hankali yace.
“Toh wa kike kallo”.
Baki ta ɗan turo.
“Ni babu”.
Dan gajeren tsaki yaja tare da cewa.
“Mayya”.
Yayi mgnar a hankali so batajiba.
Sai ta d’an kwab’e fuska tare da cewa.
“Kuma ni Mamy ce ta aikoni, Dan Allah katashi mana katashi ka tashhhhhi....”
Ta kare maganar tana slowdown da muryarta.
Hakan kuwa shiya sanya, Rayyern din d’an juyowa akaron farko ya kalleta.
Karab kuwa kyawawan idanunsu suka had’e acikin na juna, da sauri Jannart din ta kawar da kanta gefe.
Shidinma kuma janye kallonsa daga gareta yayi, inda ya sauke ganinsa akan Coastarian breakfast dish din.
Idanunsa ya d’an lumshe akasalance, kuma cikin muryarsa da tayi sanyi yace.
“Give me the water.”
Kallon d’an madaidacin bakinsa dake motsawa tayi, sai kuma Ta kau da kanta, tare da rusunawa ta zuba masa ruwan swan acikin cup.
Mik’a masa ruwan tayi.
Ganin hakanne kuma yasa shi d’an yunk’urowa ya zauna.
Karb’an cup din ruwan yayi, tare dayi masa kurb’i d’aya ya ajiye.
Kyawawan yatsun k’afarta ya zubawa ido, cikin sauk’e numfashi yace.
“Naji zanci amma ki tafi, nima zan iyaci da kaina, banason abunda za’amin wanda baikai zuci ba, dan ni bana son abun zuciya biyu da manufa.”
Ya k’are maganar still yana me Kallon yatsun k’afar nata.
Idanu Jannart din ta d’an tsura masa, saboda har yanzu tana mamakin wasu kalamai da yake yawan jifanta dasu, wanda batasan me hakan suke nufi ba ta dai fahimci tabbas bai yarda da ita bane zarginta yakeyi.
Pink lips dinta ta d’an turo, tare da soma motsasu tana mamul mamul dasu, tamkar dai Wacce takeson fad’an wani abu.
Lips din nata ya kalla, ganin yanda suke motsawa ne kuma yasa shi kauda kansa gefe.
“Da wani k’aramin bakinta kamar na tsuntsu.”
Ya fad’i hakan acikin zuciyarsa, Yayinda afili kuwa idanunsa ya lumshe tare da cewa.
“Zagina kikeyi ko?”.
Da sauri ta zaro ido tare da cewa.
“Ni dai a'a”.
Kana ta juya, tana me wasa da y’an yatsun hannunta ta nufi hanyar fita daga cikin dakin.
Har takai bakin k’ofar d’akin nasa kuma saita tsaya tare da juyowa, cikin sanyi da kuma muryar dake nuna lallashi tace.
“Kaci abincin dan Allah sai kasha magani.”
Batare kuma da ta jira abunda zaice dinba ta fice daga cikin dakin tana mgnar zuci.
“Sherri kayan kolba, wannan ai yafi Yah Junaid neman sababi da hujja wai na zageshi”.
Bayanta yabi da kallo harta fice din.
Idonsa ya lumshe tare da sauke wani irin sassayan numfashi,
Kana a hankali ya buɗe su,
Anutse ya jawo plate din abincin, cikin sanyi da kuma yanayi irin na marassa lafiya, ya soma dan tsakalan abincin.
Baiwani ci sosai ba kuma ya ture plate din gefe, tare da d’aukan tea yasha, bayan yasha tea dinne kuma ya b’alli magungunansa yasha.
Yanasha kuwa ya koma ya kwanta.
Jannart kuwa Koda ta sauk’a k’asa, Bata samu Mamy ba, Riyyam nsra kawai ta samu, da shidinne kuma suka sha hira, kafun daga bisani kowannensu ya tashi ya tafi.
Alhamdulillah yau kwanan su Rayyern, uku da dawowa daga China, Masha Allah kuma ciwon cikin nasa yayi sauki sosai, saidai jikin nasa ne baigama samun karfi ba, har yanzu.
Kulawa kuwa yana samunshi sosai daga wajen ahalin nasa, Abba, Baba Maud’o, Mamy, Ramadan Riyyam, da kuma Dr. Sulaeman harma da Usman P.A duk suna iyaka kokarinsu wajen bashi kulawa, saidai kuma har yanzu bai iyacin abinci sosai.
Wanda kuma hakan al’adarsa ce ta tuntuni.
Yau ne kuma Barrister Kabir da kuma Dr Sajo suka shirya musamman dan zuwa duba Rayyern din.
Koda suka Iso gidan tarba na musamman, Abba da Mamy sukayi musu, bayan sun gaisa dasu Mamy da Jannart ne, Abba yayi musu jagora zuwa part din Rayyern din.
Koda sukaje akwance suka iske shi, duk da cewar bayajin karfin jikinsa, amma daya gansu ya d’an sake sunyi hira.
Yanzun kuma saukowarsu k’asa kenan.
Dr Sajo ne ya kalli Abba, cikin kulawa yace.
“Amma Alhaji Bashir me zai hana baza’a sake maida Rayyern din, hospital ba tunda naga har yanzu jikin nasa bawani karfi sosai.”
Mamy dake zaune acikin falonne, ta d’an gyara zamanta, tare da fuskantar Dr Sajon, cikin bayyana damuwarta tace.
“Ai bawai wani abune matsalar ba, bayason cin abinci ne kwata kwata, komai aka basa sai yace a’a, Koda an matsa masa kuwa, bai wuce yayi loma biyu ko uku ba, sai yace ya koshi, bashi da wani abinci sai tea, nan ma yanzu ne yake d’an shan tea din da madara, da bayason ko madaran saidai empty, shiyasa bayi da karfin jiki.”
Kai Dr Sajo ya jinjina, cikin gamsuwa yace.
“Eh to kin san dama duk inda dan adam yayi ciwo abinci yake fara tsana.
Tabbas kuwa bazai samu wadataccen karfin jiki ba, harsai in ya dage da cin abinci, amma ana tambayansa ko yana da buk’atar wani abu, sai anayi masa.”
“To.”
Mamyn tace.
Yayinda Abba kuwa cewa yayi.
“Idan naga abun nasa yaki karewa ai, dolensa na daukesa na maidashi hospital, yasan duk wani illar rashin cin abinci, amatsayinsa na Dr amma baya kiyayewa.”
“Hakane kam sai hakuri da majinyaci, Allah dai ya bashi lafiya.”
Cewar Barrister Kabir.
Da “Ameen.” Duk suka amsa.
Basu wani jima ba kuma, Abba yayi musu rakiya suka tafi.
Bayan suntafi dinne kuma Mamy ta haura saman.
Azaune tasa meshi yasaka Laptop d’insa agaba, yana Dan lallatsata.
“Rayyern.”
Mamy takira sunansa da kulawa.
Jin sautin muryar Mamyn nasa ne kuma yasashi d’ago kansa Ahankali ya kalleta.
“Na’am Mamy.”
Ya amsa adan kasalance.
Karasa shigowa cikin dakin Mamyn tayi, tare da matsowa kusa dashi, cikin kulawa da kuma nuna tausayawa agareshi tace.
“Meyasa ne haka Babana? Meyasa kwata kwata bakason cin abinci? kasani fa bazaka samu isashshen karfi ba, har sai inkana cin abinci, yanzu fad’amin mekakeson ci, ko meye saina dafa maka.”
Fuskarsa yad’an kwabe tare da marairaicewa.
Cikin yanayin sakalci yace.
“Nifa Mamy bana sha’awan komai, kawai dai abincin yanzunne baya min, nafison abu me d’an melting da kuma tsami, like Chinese dishes dai, ko Mamy amin irin kunun ranan.”
Ya k’are maganan yana langwabar da kansa gefe.
Murmushi Mamy tayi tare da cewa.
“To za’ayi maka kunun kaji kada ka damu.”
Mamyn ta fad’a tare da juyawa ta fice daga cikin dakin.
Direct kasa Mamyn ta sauk’o, inda ta samu Jannart ta gaya mata, cewar Rayyern yana son ayi masa irin kunun ranar.
“To.” Jannart din tace, babu musu kuwa ta wuce kitchine, Anutse ta soma had’a kunun kamar yanda ya buk’ata.
Tsab ta gama had’a kunun, da yayi kyau sai tashin kamshi yake, juye kunun acikin flask tayi, tare da daura flask din akan tray ta daura cups agefe, sai kuma madara da zuma wanda suke cikin wani abu mai kaman glass.
Fitowa falo tayi rike da tray din ahannunta.
Mamy dake zaune afalon kuwa Ganin Jannart din harta kammala ne yasa, cikin jin dadi