Showing 183001 words to 186000 words out of 350584 words

Chapter 62 - Tubali Book 1 Hausa Novel Complete

na, bani da numbernsa na k’asar Mascow.”

Riyyam din ya tambaya cike da kewa.

Mamy kuwa fuska asake tace masa duk suna lafiya,
Haka dai suka d’an tab’a hira kafun daga bisani sukayi sallama.


Acan Mascow kuwa, kamar dai jiya yau d’inma sai k’arfe biyar, su Rayyern suka tashi ataron nasu.


Ahanyarsa ta dawowa ne kuma ya biya, Halal Mascow on top restaurant ya saya musu abinci.

Koda ya dawo wanka yayi tare da dawowa, falon ya zauna, tashar CNN yake kallo, Ahankali kuma yake d’an cin abincin dake gabansa, wanda kwata-kwata shi yanzu ba wani dadin abincin yakeji sosai ba.

Bayan ya kammala cin abincinne kuma ya wuce masallaci.

Jannart din kuwa kamar jiya haka yau d’inma ta fito taci abinci, saidai bata wani ci sosai ba, drinks din kawai tasha ta koma ta kwanta.

Taso yin k’ira amma kuma tasan layinta, bazai yi amfani awannan k’asar ba sabida bata da kati ko asi, shiyasa ta hakura, gashi shi kuma tun ranan da suka zo ba ganinsa ma takeyi ba.

Wannan dalilin yasa kawai ta soma buga game, tana cikin yin game dinne kuma bacci ya d’auketa.

*Ethiopia.*

Riyyam-nsra ne zaune akan sofan, dake cikin katafaren falon Mammynsa, daga can gefensa kuwa Mammyn nasa ce, sai Kuma Zaytoon itama dake gefe.

Kakarsu Didi kuwa kwance take akan kujera.

Riyyam-nsra din ne kuma ya d’ago kansa, tare da jingina da jikin Mammynsa, cikin farinciki da kulawa yace.

“Mammy duk wani abun da muke zato da tunani ya tabbata, Mammy Nigeria tsatson mune, kuma jigonmu ce acan tushen farin cikinmu suke, wallahi Mamy ni harma naji na gaji da k’asar nan, inason komawa k’asata ta Haihuwa kuma k’asar mahaifina.”

Ya k’are maganan cikin wani irin bege me karfi dake fusgarsa.

Zaytoon dake zaune agefensa ne ta d’an langwabar dakai, kana Cikin sanyi tace.

“Har gwara kaima Riyyam kaje kaga k’asar, kaje ka ga abunda ni idanuna suka kasa ganemin kaje ka ƙamshin ƙasarmu ka shaƙi iskar ƙarmu.”

Idanunsa ya d’an lumshe kana cikin son bawa y’ar uwartasa k’arfin guiwa yace.

“Insha Allah kema zakije Zaytoon, auren Hamma Ramadan na tashi, Mamy zata je kema kuma zakiji harma da Didi, nikam naji dadin zama cikin ahalina, nayi farinciki sosai Ina kuma fatan kasancewa dasu har abada.”

Idanu Mammy ta d’an lumshe cikin kuma yanayin sanyi tace.

“Insha Allah Riyyam komai zaiyi dai-dai, watarana komai zai wuce mubi komai ahankali.”

Fuska Riyyam din ya d’an kwab’e, kana cikin salon shagwab’a yace.

“Mamy wani irin ahankali tsawon shekaru fa muna zaune ahaka, ayanzu kuma gaba d’aya komai ya tabbata.”

Gyara zama Mammyn tayi kana cikin kulawa tace.

“Riyyam nima inaji ajikina cewar watarana zanje, zuciyata ta zak’u akan naje din, saidai bansan meye zuwan nawa zai haifar ba Riyyam, duk wani abu da kake tunani ya wuce nan, har yanzu akwai k’ullin da bai gama warwarewa ba, amma nasa araina cewa Insha Allah zanje watarana, saidai kuma akwai buk’atar muyita addu’a, saboda Allah ya sauk’ak’a mana duk wani tsanani.”

Da “Ameen.” Duk suka amsa, kana daga nan kuma suka ci gaba da hirarsu.


Ahaka rayuwa taci gaba, aduniyar Rayyern da kuma Jannart, babu wanda yaga d’an uwansa tun zuwansu Mascow’n, wanda ak’alla yau kwanansu shida suna neman na bakwai kenan.

Ko yanzun kuwa Jannart dince ke zaune acikin falon, zaman nan tayi irin na tankwashe kafafu.

Yayinda take sanye da wani pencil jeans pink colour, da kuma wani t-shirt sai jacket mai nauyi da ta d’aura akan shigar tata.

Ahankali ta dan daga kanta sama, tare da kwantar da kannata ajikin kujera.

Yanayin zaman da tayi dinne kuma yasa, gaba daya duk wani shati na halittar jikinta ya bayyana, more especially breast dinta, wanda ko bra bata saka ba, gashi kuma rigar sanyin nata ya Dan bud’e kad’an.

Idan ka kalleta azahirance zakayi tunanin cewar bacci ne ya d’auketa ahaka, saidai kuma azahirin gaskiya bawai hakan bane, domin gaba daya tunaninta ya tafi ne izuwa Gida.

Ayanzu tunanin halin da Dadynta dasu Abdull suke ciki take, domin tasan koma yaya basa cikin yanayi mai dadi, gashi kuma tunda tazo k’asar batayi waya da Abba Kabir dinta ba ko su Mamy da Ramadan batayi mgn dasuba gaba ɗaya kewarsu ya dabaibayeta.

Ahankali ya turo k’ofar falon ya shigo, hannunsa rike da ledan restaurant da kuma suit d’insa.

Shigowarsa cikin falon kuwa shiya saka shi sauk’e idanunsa akanta.

D’an tsayawa yayi yana me kallonta, tun daga k’afafunta dake tankwashe, har zuwa kan lafaffen cikinta, da kuma kirjinta zuwa dogon wuyanta.

Idanunsa ya d’an k’urawa soft neck din nata, wanda yake dauke da dan siririn chain, sosai wuyan nata ke da kyau ga wani layi layi, Ahankali ya kuma dawo da kallonsa ga kirjinta.

Lokaci daya kuma cikin sauri ya janye, idanunsa daga kallonta.

Ledan dake hannunsa ya ajiye, tare da ci gaba da takowa ya k’arasa shigowa cikin falon.

Jannart kuwa jin alamun takunsa ne yasa ta saurin d’ago Kanta, karab kuwa Idanunsu suka sark’e acikin na juna.

Wanda hakan yasa taji zuciyarta tayi wani irin bugawa, lokaci d’aya kuma taji wani irin rauni ya lullub’e zuciyarta.

Ahankali tayi k’asa da kanta, tare da da hannu ta gyara zaman rigar sanyin ta.

Cikin wata irin sanyin murya mai dauke da shagwab’a tace.

“Sannu da dawowa.”

Idanunsa ya d’an lumshe
tare kuma da kawar da kansa, murya akasalance da kuma gajiya yace.

“Uhummm.”

Yanayin yanda ya amsa da Uhummm dinne kuma ya sata lumshe ido, saboda hakanan taji yanayin nasa na kasala, ya tada mata da tsikar jiki.

Ahankali Rayyern din ya soma tafiya, har yakai bakin k’ofarsa kuma saiya juyo, ya kalleta, wani abu yakeson ce mata, amma hakanan sai yaji bakinsa yayi nauyi kana shi kansa bai san me yake son ce matanba, hakan kuwa shiyasa kawai ya wuce daki.

Jannart kuw najin alamun ya shige bedroom ne, yasa Itama ta tashi ta wuce nata dakin, yau ko abincin daren ma bata ci ba.

Shikuwa Rayyern Bayan yayi wankane ya dawo falon, abinci yaci tare da komawa dakinsa ya kwanta.

Washegari kuwa kamar yanda ya saba haka ya fita bayan ya ajiye mata breakfast.

After 2weeks.

Ahaka sukeyin rayuwarsu ita dashi, daga wannan ranan kuwa babu wanda ya sake Ganin d’an uwansa, saidai kullum yana ajiye mata breakfast da kuma dinner, da rana kuwa saidai ta ci ragowar breakfast.

Gaba d’aya duk kad’aici ya dame ta, duk da ta saba da hakan amma yanzu batajin dadin hakan.

Shikuwa Rayyern gaba daya yanzu ya zama busy, domin course din da sukeyi din ya fara nisawa, shi yasa always he’s busy.

Daya dawo kuma ya gaji sosai, daga ya d’an tab’a system d’insa sai bacci.

Yau din kuma tunda ya fita da safe baidawo ba, domin Koda suka tashi ataron nasu, still meeting ya shiga da wasu manyan Doctors na k’asar.

Koda lokacin sallan magriba yayi, bayan yayi sallan meeting din ya sake komawa haka ma sallan Isha.

Basune suka tashi a meeting dinba kuwa sai 1:00 pm.

Agajiye yake sosai yau din, dan ko dak’yar ya iya biyawa ta restaurant ya saya abinci, da wasu chocolates d’insa, tun acikin mota kuwa yake cin chocolates din ahaka harya iso gida.

Koda ya dawo gidan kusan 11 ake nema.

Haka ya shigo cikin falon, yana mejin yanayinsa na d’an sanjawa, saboda yanzu Kwata-kwata baya ma shan maganinsa, especially now daya zama busy.

Direct d’akinsa ya wuce, tare da sakarwa kansa ruwa.

Itakuwa Jannart tana can cikin d’aki, duk yunwa ya isheta saboda duk yau bataci abinci ragowar breakfast din nata ba.

Tafito falon nasu kuma bata ga komai ba, wannan dalilin yasa ta koma ta kwanta, saidai duk yanda taso bacci yaki daukanta.

Ganin hakanne kuma yasa ta sha ruwa, tare da komawa ta kwanta, ahaka wani baccin wahala ya dauketa.

Ab’angaren Rayyern kuwa yana fitowa daga wanka, kaya ya sakawa jikinsa, batare daya sake bin takan abincin daya kawo ba, ya haura saman gadonsa, bacci ne sosai a idanunsa, shiyasa yana kwanciya bacci ya d’aukesa.

Washegari.

Saturday.

Bakamar sauran ranakun ba, kasancewar yau din weekend ne yasa, bai fito da wuri ba har sai 9:00pm.

Ahankali ya bud’e k’ofar bedroom din ya fito, maida k’ofar yayi ahankali ya rufe.

Ya juyo ya fuskanci cikin falon, idanunsa ya dan waro lokacin da suka suka sauk’a Akan...!



*Albishirinku! Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA*

NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA.
Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.

Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke taimakawa (sex hormones 😍) dinki.
Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!?
Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu.
Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki?
Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu,
Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ki zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan.
Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya.


Akwai daya bangaren wato *KAMSHI*
Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, sayan na gari maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia.

Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.

🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA
*(GARKUWAR MA'AURATA)*

By
*GARKUWAR FULANI*


Abincin daya kawo jiya da daddaren, idanunsa ya d’an zubawa ledodin, wanda da dukkan alamu babu wanda ya tab’a su, Dan suna nan kamar yanda ya ajiye su.

numfashi ya d’an fesar tare da soma takowa, ya k’araso tsakiyar falon, inda abincin ke ajiye.

Isowarsa wajenne kuma ya sake tabbatar masa da cewar, tabbas babu alamun an tab’a ledodin.

Bakinsa ya d’an tab’e tare kuma da komawa ya zauna, akan d’aya daga Cikin kujerun falon, idanunsa ya d’an lumshe Ahankali, dai-dai lokacin kuma daga can waje aka soma knocking kofar falon.

Ahankali ya d’an bud’e idanunsa, tare da mik’ewa tsaye, saboda already dama yayi musu order’n breakfast, to yanzun ma yasan breakfast din nasu ne ya iso.

K’arasawa yayi ya bud’e k’ofar tare, da karb’an ledodin breakfast din.
Kana ya dawo ya zauna akan sofa.

Duk da cewar baya wani jin yunwa sosai, amma hakan baisa shi kincin abincin ba, bud’e ledan yayi ya somaci, saidai bai wani ci sosai ba ya ture abincin gefe.

Yanda yaji duk baya wani jin dadin cikinsa ne kuma, yasa shi mik’ewa ya koma d’aki, sachet din maganinsa ya d’auko, tare kuma da dawowa falon ya zauna.

K’wayoyin maganin da sukayi saura ya zubawa ido, wanda kwata kwata basu wuce guda 16 ba, kasancewar akowacce rana mutum zaisha guda d’add’aya ne.
To Yanzu dai way’anda suka rage masan, basu wuce na 2weeks ba, banda ma yayi wasa da shan maganin yasan da yanzu basu Kai haka yawa ba.

B’alle maganin yayi ya saka abakinsa, tare da Korawa da ruwa marar sanyi.

Bayan yasha maganin ne kuma ya mik’e tsaye, babban agogon Bangon dake sak’ale acikin d’akin ya kalla, wanda yake nuna masa 12:pm dai-dai kenan na rana.

Ajiyar zuciya ya d’an sauk’e tare da d’aukar wayarsa, hadi da car key d’insa, domin duk da cewar yau din weekend ne, amma suna da test da zasuyi akan, yanda ake dashen k’oda, wanda kuma yau dinne firstly da zasu fara, gwaji akan abunda aka koya musu.

Kaitsaye ya fice daga cikin falon, direct wajen da ya ajiye motarsa ya nufa, Ahankali ya d’aga kansa yana me Kallon yanayin garin, duk da kasancewar yanzun rana ne, amma sudai awajensu tamkar safiya ne, saboda gaba d’aya yanayin garin babu rana, sai wani irin sanyi mai ratsa cikin k’ashi da bargo, ga kuma dusan k’ank’ara da yake sauk’owa daga sama.
Snow kawai tako ta ina.

Yana shiga cikin motar kuwa yayi mata key, tare da cillata kan titi, kaitsaye ya nufi wani babban asibiti.
*JSC MEDICINA CLINIC MASCOW,* domin acanne zasu yi karatun nasu na yau.

Jin k’aran tashin motar ne, yasa ta bud’e Idanunta dake lumshe.
Ahankali takai dubanta ga jikin window’n dakin nata, wani irin sassanyar numfashi ta fesar, tare kuma da d’an yunk’urawa ta tashi ta zauna, Allah ya sani tana matukar shiga takura, azaman da takeyi ita d’aya acikin gidan, tana buk’atar waya sosai, amma bata da yanda zatayi, saboda tasani layinta ba kudi, shi kuwa gaba d’aga ya shareta, akullum yanayin abu tamkar baisan da zamanta acikin gidan ba.
Gashi tun da suka zo ko fita bata tab’a yi ba ko dan harabar gidan.

D’an k’aramin tsuka taja, saboda gaba daya ta gaji da kwanciyar da takeyi.

Ahankali ta sauk’o daga kan gadon, tare da zubo da k’afafunta k’asa.

Kallon kanta tayi, saboda sanye take da wani dogon wando mai kauri, wanda ya kama jikinta sosai, sai kuma wani top long sleeve, shid’inma dai mai kauri ne sosai, still kuma sai wata riga jacket da ta d’aura akan shigar nata, kanta kuwa sanye yake da hulan sanyi.

D’an kwab’e fuska tayi, domin duk da irin shigar da tayi din, bai hanata jin sanyin da akeyi ba, Sam har yanzu bata saba da sanyin garin ba.

Wayarta dake kan bedside ta d’auka, sanin da tayi cewar Rayyern din ya fita ne, yasa kaitsaye ta nufo falon.

Koda ta fito kuwa tv ta kunna, saidai gaba d’aya babu wasu channels, sai zallan na turawa, ba haka ta soba amma dole ta hakura, zama tayi tare da bud’e ledodin breakfast din da taga ya ajiye.

Chinese dishes ne, da kuma African dishes, kamar dai yanda ya saba yi musu order akoda yaushe.

Fuskarta ta d’an kwab’e tare kuma da turo d’an k’aramin bakinta gaba.
Cikin shagwab’a tace.

“Ni gaskiya I’m tired da way’annan foodies din, always abu d’aya ni nagaji, Nigerian dishes nakeson ci, me zanyi da Chinese dishes niba
mai kananan idanu ba.”

Ta k’are maganar cikin tura baki tamkar Rayyern din yana gabanta.

Haka dai ta d’an tsakali abincin taci, domin kwata kwata bata iyacin chinese dishes din.

Bayan ta kammala cin abincinne kuma, ta haye saman kujera ta kwanta.


*Kano Nigeria*

Abba da Mamy ne ke zaune, acikin katafaren falon nasu, inda Abban ke zaune akan sofa, Mamy kuwa na durk’ushe agabansa tana had’a masa coffee.

Abban ne ya d’ago kansa ya kalli Mamyn, kana cikin kulawa yace.

“Ni kuwa Ruƙayyah ya labarin y’arki Jannart, tunda suka tafi kun gaisa da ita kuwa?.”

D’agowa Mamyn tayi ta kalli Abban, domin dama kamar ya Sosa mata inda yakeyi mata k’aik’ayine.

Numfashi ta d’an fesar, cikin kuma rashin jin dadin abunda zata fadad’in tace.

“A’a ba muyi waya da ita ba har yau, kwata-kwata bansan me yake damun Rayyern ba, domin duk sanda zamuyi waya dashi, Idan nace ya bawa Jannart din wayan, sai yace min baya gida, To amma kuma nasan bazaimin k’arya ba, saboda dama ba zamanne ya kaishi ba, kasan Rayyern da sabgogi.”

Kai Abban ya jinjina, tare da gyara zamansa, cikin sanin halin Rayyern din yace.

“Ni ai banma tambayesa itaba, saboda nasan dole wani uzurin zai kawo, amma yanzu ke kinyarda da uzurin da yake baki, na cewar ko yaushe baya gida? ai tunda yana da lokacin da zai iya dawowa gida yayi bacci yayi wonka ya sauya kaya, To yana da lokacin zama ya bata


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login