Showing 132001 words to 135000 words out of 350584 words
tare da cewa.
“Dan Allah Hamma Rayyern kada kace a'a”.
Ya rigada ya gama karya mishi zuciya da hawayensa.
Duk da ko mgnar yayi sai yaji ya gaji shiyasa baya son yawan mgn.
A hankali yasa hannunshin ya amshi wayar.
Cikin nitsuwa ya manna wayar a kunneshi tare dasa kafaɗarsa ya makale wayar.
Murya a sanyaye yace.
“Assalamu alaikum”.
A can ƙasar Ethiopia kuwa.
Wani irin lumshe ido Mamma tayi, tare da jan wani irin dogon numfashi, kana cikin tsananin harbawar da zuciyarta keyi tace.
“Wa alaikassalam Mauɗo am!!!”.
Wani irin rumtse idanu Rayyern yayi da azaban ƙarfi tare dasa hannunshi y...!
*Albishirinku! Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA*
NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA.
Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.
Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke taimakawa (sex hormones 😍) dinki.
Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!?
Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu.
Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki?
Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu,
Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ki zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan.
Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya.
Akwai daya bangaren wato *KAMSHI*
Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, sayan na gari maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia.
Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.
🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA
*(GARKUWAR MA'AURATA)*
By
*GARKUWAR FULANI*
A Jikinta ya manna kanshi da cikinta kana kuma ya cusa fuskarshi acikin jikin nata.
Tare dasa hannunshi na dama ya damƙe mararshi.
Gaba ɗaya jikinshi rawa yakeyi tamkar mazari, wani irin ciwo cikinnasa keyi masa, wanda har hakan yasa numfashinsa, ke kokarin kwacewa.
Hannunshi na hagu yasa abayanta ya zagayeta, tare da riƙe ta gam-gam cikin gigitan ciwo da fitan hayyaci.
Hakan kuwa yayi masifar gigita Jannart, wanda gaba daya jikinta ya d’auki rawa, kamar yadda nashi jikin ke rawa.
Kana ya kwakumeta ya kanainayeta ya hanata ƙwaƙƙwaran motsi.
Jannart kuwa Ganin hakan yasa cikin firgici ta buɗe baki, murya na rawa ta fara cewa.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun Mamy! Mamy!! Mamy!!! Kalli yadda yakeyi fa!!!!”.
Yayinda ita kuwa Mamy cikin tsananin tashin hankali da kidima, ta fara juyawa tsakiyar falon cikin rashin sanin abinyi taketa rabkawa Ramadan kira.
“Ramadan! Ramadan!!! Kazo!!! Rayyern ba lfy”.
Dr. Sulaiman ne wanda shi ya dawo da Rayyern din, ya turo ƙofar da hanzari,
baishigo da wuri bane kuma, saboda ya tsaya fadawa Baba Mauɗo cewar ciwon Rayyern ne ya tashi.
A hanzarce ya faɗo cikin falon,
Baba Mauɗo na biye dashi a baya.
Yayinda sukabar Hadi da Ari mai gadi kuwa tsaye a harabar gidan, sunyi jugum-jugum domin duk mai imani, muddin yasan yadda ciwon Rayyern ke yi in ya tashi tamkar zai tafi da ransa to tabbas zai cika da fargaba.
Hakan ne ma yasa Hadi zaro wayarshi ya kira Abba, yana ɗagawa cikin yanayin tashin hankali yace.
“Alhaji jikin Rayyern fa ya tashi”.
Cikin kidima Abba ya kalli mutanen da yake tare dasu tare da miƙewa tsaye yace.
“Rayyern ba lfy”.
Yana faɗin haka ya fita daga falon da bisa alamu duk mgnar sirri yakeyi.
Yana katse kiran Hadi ya kira Ramadan yana ɗagawa yace.
“Kai Ramadan kana ina”.
Da sauri yace.
“Abba ina Minjibir ne. Lfy kuwa?”.
Cikin bada umarni da tashin hankali yace.
“Maza ka wuce kayi gida yau kuma cikin Rayyern ya tashi”.
Cikin tsananin tashin hankali Ramadan ya mike tare, da barin duk wani abu da yakeyi, hankalinsa amatukar tashe yace.
“innalillahi wa innailaihi rajiun! Jikin Hamma Rayyern ya tashi? Yanzu Abba Hamma Rayyern din yana ina?”
Abba dake tsaye, cikin alhini da fargaba yace.
“Yana gida, kayi sauri kaje.”
Yana gama fad’in haka ya katse kiran.
Kana yaci gaba da tuƙin da yakeyi.
Shi kuwa Ramadan a kidime ya kalli Riyyam-nsra dake cewa.
“Hamma Ramadan meya faru”.
Ya ƙare .mgnar yana firfito da idanunsa.
Idanu Ramadan din ya rumtse da karfi, cike da alhinin abunda Abban ya gaya masa, ya kamo hannun Riyyam-nsra tare da jansa, suka nufi parking lot, hankalinsa atashe yace.
“Riyyam mu tafi gida yau kuma ciwon cikin Hamma Rayyern ya tashi,
abunda yafi shekara biyu ya kusa shekara uku bai tashi ba, amma yau gashi ya sake tashi mishi.”
“Innalillahi!”
shine abinda Riyyam-nsra ke ta maimaitawa.
Dai-dai lokacin da suka shiga mota.
A 360 Radaman ya figi motar yana cewa.
“Yah Rabbi, Yah Allah ka bawa Hamma na lfy, gaba ɗaya mun sakankance, da cewar ya worke tunda mukaga yayi shekaru bai tashiba”.
A nan gidan kuwa.
Cikin yanayi tashin hankali Mamy ta kamo hannun Dr Sulaiman, a gigice ta jawoshi zuwa gaban Jannart da Rayyern ke kwance kanta, irin kwanciyar nan ta rubda ciki.
Murya na rawa Mamy tace.
“Sulaiman duba min Rayyern yana raye kuwa duba minshi kaga fa baya motsi”.
Ta ƙare mgnar wasu irin masifaffun hawaye na kwaranyo mata.
Yayinda sai a lokacin kuma Jannart ta sunkuyo da kanta, ta zuba mishi ido tabbas kuwa ya daina motsi, duk rawa da karkarwar da jikinshi keyi ya bari.
Wani irin zaro ido tayi tana kallon Mamy dake cewa.
“Innalillahi wa innailaihi rajiun Sulaiman ka duba min Rayyern, kada ya tafi ya barmu akwai nauyinshi da bamu sauke a kanmu ba."
Shi kuwa Dr Sulaiman kamo hannunta yakeyi, yana son zaunar da ita amman ina, gaba daya ta gama gigicewa, ga hawayen dake ta Kwarara acikin Idanunta.
Baba Mauɗo kuwa da sauri ya matso gaban Jannart ya tsuguna, cikin kuma tashin hankali yasa hannunshi, akan wuyan RAYYERN sabida a kife yake, murya na rawa dattijon ya fara kiran sunanshi.
“Rayyern! Rayyern!! RAYYANU!!! Muhammad Muhammadu tashi.
Buɗe idanunka Mauɗona!!!”.
Ya ƙare mgnar hawaye na kwaranyo mishi.
Wanda ganinsu ne kuma yasa hawayen idanun Jannart tsinkowa.
Tausayin tsohon da Mamy ne sukayi masifar raunata mata zuciya.
A fili zaka gano tsananin tashin hankali da kidimar da suke ciki, kana da tsananin sonshi dake cikin kwayar idanunsu.
Shi kuwa Rayyern da yakejin kansa acikin wata duniya, mai dauke da tsananin azaba gami da radadi, sama-sama haka yake jiyo muryarsu.
Saidai kuma bazai taba iya amsawa ba, duk da yana jiyo kiran sunansa da Baba Mauɗo keyi, saidai baya da hakikanin cewa, ko yan siraran labban bakinsa zai iya motsawa, saboda tsananin ciwon da yakeji.
Dr Sulaiman kuwa cikin samar da kwanciyar hankali wa Mamy, ya samu ya ajiyeta bisa kujera kana a hankali yace.
“Mamy Rayyern yana numfashi fa, babu abunda ya samesa, Dan Allah ki kwantar da hankalin ki, Insha Allah zai samu lfy, na mishi allura tun a asibiti, yanzu haka ciwon ya fara lafawa, Insha Allah gaba daya zai daina”.
Dr. Sulaiman din ya kare maganar cikin, kwantar da murya da kuma son samawa Mamyn nutsuwa.
Dai-dai lokacin ne kuma Abba ya shigo.
Da sauri ya iso tsakiyar falon.
Sai kuma ya iso gefen Baba Mauɗo a kidime ya fara kiransa.
“Rayyern”.
Sai kuma ya juyo da sauri jin Dr Sulaiman na cewa.
“Abba dan Allah ku kwantar da hankalinku, ku barshi zuwa anjima kaɗan zai iya amsa muku, nayi masa allura Insha Allah zai samu sauki”.
Wani irin dogon numfashi Abba ya sauke, kana ya koma ya zauna bisa kujerar dake gefensa.
Yayinda Mamy kuwa har yanzu ta gaza tsaida hawayenta.
Gaba daya hankalinta yaki kwanciya, tsoro takeji kada wani abu ya samu Rayyern din, badon komai ba kuwa saidan sanin da tayi, cewar ciwon cikin baya tab’a yi masa da sauki idan ya tashi.
Jannart kuwa da tayi k’asa da kanta, tana jin yadda Rayyern din ke kwakume da ita da masifar ƙarfi, yanayin rikon da yayi mata, dinne kuma yasa kugunta ya soma sarawa, saboda ba wai riko ne na wasa yayi mata ba riƙone na neman mafita.
Ramadan da Riyyam-nsra kuwa kusan a jere da sassarfa suka shigo cikin falon, kowannensu hankalinsa amatukar tashe.
More especially Ramadan da yasan irin yanda ciwon, keyiwa Hamman nasu idan ya tashi.
Da sauri suka nufi kanshi, saidai basu k’arasa ba kuma suka tsaya, saboda ganin su Abba duk suna zaune.
Baba Mauɗo na zubda hawaye, Mamy ma haka kana Jannart da yake kwance lib a cinyarta kamar matacce, itama hawayen take tsiyayarwa.
Abba kuwa habarsa ya tallafe, saidai kallo daya zakayi masa, ka karanto tsananin tashin hankalin dake kwance akan fuskarsa.
Ganin hakanne kuma yasa, zuciyar Ramadan wani irin harbawa, lokaci daya kuma gaba ɗaya jikinsa ya fara tsuman tashin hankali, dan su a zatonsu Rayyern din ya rasu ne.
Cikin wani irin tashin hankali rauni gigita da kuma kidima.
Riyyam-nsra ya saki wani irin raunataccen kuka, tare da zamewa ya zauna aƙasa ya kife kansa bisa sawun Rayyern, cikin rauni murya na rawa kuka na danne abinda yake faɗa yake cewa.
“Innallahi wa innailaihi rajiun Mammy mutuwa zata hanani cika miki burinki,
Wayyoooooooo Allah na Mammy na inama kina kusa kizo kiga halin da tsatsonki yake ciki, Mammy wlh shine wlh sune”.
Su Abba kuwa, tsananin tashin hankalin da suke ciki, yasa gaba ɗaya basa iya fahimtar kalaman Riyyam-nsra, asalima basa jin me yake faɗa da kyau.
Sai dai shi kuwa Rayyern da tunaninsa ke kokarin gushewa, a sama sama yake jiyo kukan yaron, da kuma abinda yake faɗi.
Duk da bawai yana fahimtar kalaman sosai bane, amma yaji wasu daga cikin maganganun, wanda ayanzu baya cikin Lfy da kuma hayyacin da zai iya nazari ko hasashen kalaman.
Dr Sulaiman ne ya matso kusa da Riyyam-nsra, ya jawoshi jikinsa ya zaunar dashi tare da cewa.
“Kai Riyyam-nsra kabar kuka bafa rasuwa yayi ba, ciwon ne ya fara lafawa kaga Abbanku ma yayi shiru”.
Sai alokacin Ramadan ya sauke wani irin numfashin daya, sakar masa da wani nannauyan abu mai kama da dutse daya tsaya a ƙirjinsa.
Sabida gaba ɗaya ya fara rasa numfashin sa.
Shi kuwa Riyyam-nsra cikin kasa danne kukan sa yace.
“Yah Sulaiman, da gaske kake Hamma Rayyern dina, yana numfashi?”.
Kai Dr. Sulaiman ya jinjina, kana cikin sauri yace.
“Eh Riyyam-nsra bai rasuba gashi yana numfashi, nanda y’an mintuna zai tashi insha Allah.”
Ajiyan zuciya suka sauƙe baki ɗayansu.
Sai lokacinne kuma Mamy ta iya tsaida hawayenta.
Yayinda Baba Mauɗo Kuwa sam hawayen shi ya gaza tsayuwa.
Hakan kuwa shi yasa Jannart ta gaza tsaida hawayenta, saboda acikin rayuwar ta akwai rauni sosai, matukar zata ga hawayen Babba, To Lallai zuciyarta saita karye, ba kuma zata iya lallashin kanta ba.
Ganin duk sun d’an nutsu ne kuma yasa, cikin sanyi Dr. Sulaiman ya samu ya zauna, tare da d’go kansa ahankali yayi gyaran murya kana anutse yace.
“Kwata kwata abun bai wuce 30mnt da fara mishi ba, domin tun da ya fara mishi na fahimta, saboda naga yana ta haɗa zufa, kasancewar alokacin muna cikin meeting ne da sauran Doctor's din mu,
Akan wani course da muke son wasu daga cikin Doctor's ɗin namu suje suyi a Mascow,
So dana fahimci cewa, ciwon cikin nasa nason tashi ne, sai na bukaci da mu tashi taron, amma sai yaki bani dama, to kafin mu gama ma abin har ya fara tsanan ta.”
Idanu duk suka tsurawa Dr. Sulaiman din, saboda Jin abunda yake fad’a.
Shikuwa Dr. Sulaeman gyara zamansa yayi, tare da fuskantarsu, cike da son sake samar musu nutsuwa yace.
“Insha Allah Rayyern zaiji sauk’i, domin muna fita a meeting din nayi masa allura, saidai kafun nan ma tuni abin ya gama tashi, shiyasa ya ɗan wahal dashi amman Alhamdulillah, bayan 50mn idan alluran ta fara aiki zai dan ji sauƙi, wanda kuma zuwa yanzu inada yakinin, fara aikin allurar Dan shiyasa ma kukaga yayi shiru jikin ya daina bari.”
Cikin gamsuwa Ramadan da Abba suka gyaɗa kai, saboda wannan bayanine da likitocin suka saba yi musu, sudai fatansu shine samun saukin Rayyern din.
Baba Mauɗo dake zaune kuwa, ahankali yasa hannunshi ya shafa kan Rayyern din zuwa wuyansa.
Kana ya miƙe tsaye.
Tare da sharce hawayen sa.
Cikin tausayawa yace.
“Toh Alhamdulillah Allah ya bashi lfy yasa zakkan jikine, Allah ya daga kafadunsa.”
Ya ƙare mgnar yana nufar hanyar fita.
Cikin sauƙe numfashi Riyyam-nsra da Ramadan suka bishi da ido, da kuma wani kallo mai cike da wani irin so na musamman.
Abba da Mamy kuwa.
Numfashi suka fesar tare da cewa.
“Amin ya Allah baba Mauɗo”.
Shi kuwa Baba Mauɗo yana fita
Hadi da Ari sukayi kanshi, cikin girmamawa da kwarjinin dattijon suka hada baki wurin cewa.
“Allah rene ya jikin nasa?”.
A hankali yace.
“Alhamdulillah jiki da sauƙi.”
“Allah ya kara sauki.”
suka had’a baki wajen fad’a.
Shikuwa Baba Maud’o.
“Amin ya Allah”.
Yace yana mai wucewa cikin ɗan side ɗinsu.
Kai tsaye Bathroom ya wuce al'wala yayi kana yazo.
Ya dauki Kur'ani ya fara karatu wai ko zaiji sanyin zuciyarshi, da wani nauyi daya danne mishi ƙahon zuciyarshi.
Amma ina hakan ya gagara,
Hawaye kuwa tamkar an bude bakin famfo.
Allah ya sani yana jin wani irin azabebben son yaran a zuciyarshi,
Baya son gani ko jin duk wani abu da zai cutar dasu duk kankantarshi da yanada hali da ko kuda bazata sauka kan Rayyern ba.
Da ya dauka kawai dan kyautata mishi da sukeyi ne, kuma dan kasan cewarsu yaran uban gidansa.
Toh amman zuwan Riyyam-nsra yasa ya fahimci, kawai yana son duk wani abinda ya shafesu ne.
Wasu lokutan yakanyi tunanin ko dan kamar da Riyyam-nsra din, yakeyi da Rayyern ne yasa yake masifar sonshi ma din.
Hannun shi ya daga sama yana mai yiwa yaran addu'a.
A nan cikin falon kuwa.
Shiru Jannart tayi ta sunkuyar da kanta ƙasa.
Yayinda hawayenta keta kwaranya ba ƙaƙƙautawa.
Tana ciwo amman bata taɓa ganin irin wannan tashin hankali a fuskar Daddy, kamar yadda ta gani a fuskar Baba Mauɗo da Abba ba.
Bata taɓa ganin makamancin gigitar da Mamy tayi a fuskar Mom ba.
Duk da tasan mom tana masifar sonta.
Wannan kawai ya isa shaidar son uwa da banne a duniya.
Mamy kuwa numfashi take ta saukewa kawai.
Riyyam-nsra kuwa miƙewa yayi ya haura sama.
Yana shiga kuwa ya kira Mammyn sa.
Abba kuwa cikin sauƙe numfashi ya tallabe haba.
Tare da cewa.
“Ramadan dagashi a kanta.
Sai ka gyara mishi kwanciyarsa”.
Cikin sauri Dr Sulaiman yace.
“A'a Abba barshi shida kanshi zai tashi in allurar ta gama ratsashi.”
Cikin sanyi Mamy tace.
“Ai kuma Jannart din zata gaji”.
Kai ya dan juya tare da cewa.
“Bazai dadeba zai tashi”.
Shiru sukayi.
Kana shi kuma Dr. Sulaiman miƙewa tsaye yayi tare da cewa.
“Toh Abba ni bari in wuce gida anjima zan dawo.”
“Toh mun gode Dakta”.
Abba ya faɗa yana mai gyara zamanshi.
Shi kuwa Dr Sulaiman Ramadan ya kalla tare da cewa.
“Kasan idan ya tashi zai tashi ba ƙarfi illar alurar kenan, shiyasa ba'a cika son yawaita yiwa mutum itaba.
Zaijishi duk ba ƙarfi, so dole sai an taimaka mishi ka sani”.
Kai Ramadan ya jinjina tare da cewa.
“Eh na sani”.
Daga nan ya sallamesu ya tafi.
Su kuwa, shiru sukayi suka zauna jugum-jugum.
Ganin kuma yamma lokacin daura girki yayine, yasa Mamy miƙewa a hankali ta nufi Kitchen.
Bayan ta cire lallenta ne kuma ta fara aiki.
Ita kuwa Jannart gaba ɗaya ta kasa kwakwaran motsi.
Sabida masifar kunya da nauyin Abba da takeji, kana ga kuma nauyin zaratan namiji dake kanta.
Wanda agaba daya rayuwarta bata taɓa fuskantar makamancin hakan ba ga wani irin masifeffen ƙamshin jikinsa dake narkar da jikinta, tattausan sumar kansa da sajensa ta zuwa idanu.
Yanzu kusan 50 minutes kenan suke a hakan.
Yayinda kuma har yanzu hawayenta ked’an disowa kadan-kadan.
Suna mannewa ajikin