Showing 33001 words to 36000 words out of 350584 words
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
*FREE PAGE ne*
*Littafin TUBALI na kuɗine ki biya ki karanta cikin salama, special Group 1k ne kana akwai karamin group 500 kacal ne 0661110179 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU sai ki turo min shaidar biyanki ta whatsApp number na 09097853276, ko kuma ki sayi katin MTN ki turo ta whatsApp ɗin*
Hakanne kuwa yasa suka bishi da kallo dukansu harsaida ya b’acewa ganinsu.
Ahankali Rayyern da Ramadan suka dawo da kallonsu ga Mamy wacce itama tayi zugum, da dukkan alama kuma bata da abuncewa.
Naseer kuwa mik’ewa tsaye yayi, kana jikinsa amatuk’ar sanyaye ya kalli Mamy, cikin bayyana godiyarsa agaresu yace.
“Zan tafi Mamy, mungode sosai da karramawarku agaremu nida abokina Riyyam.”
Jin abunda Naseer din ya fad’ane kuma yasa Riyyam ma saurin mik’ewa, tare da cewa.
“Naseer jirani mu tafi asibitin tare.”
Kai Naseer din ya girgiza tare da kama kafadun Riyyam, cikin sanyi yace.
“A’a Riyyam ka zauna, kada kace zaka bini, saboda asibitin Mai-nasara bak’aramin asibiti bane, ko ni da zanje yanzu sainasha tambaya kafun zan iya gano ward d’in da suke, kayi hakuri kaji duk yanda ake ciki zan kiraka awaya Insha Allah ina dai zaka gane hotel ɗin da ka sauka?.”
Kai Riyyam yadan jinjina batare kuma daya soba, haka yabar Naseer ya tafi shi kad’ai.
Ganin fitan Naseer dinne kuma yasa, Rayyern mikewa ahankali, cikin kuma takin dake bayyana nutsuwarsa, ya nufi dakin Abban nasu kai tsaye.
Ajikin k’ofar ya tsaya tare da daura hannunsa akai ya d’anyi knocking.
Daga ciki Abba dake zaune akan wata kujera ya jingina kanshi ya rumtse idanunshi ya bada izinin shigowa.
Ahankali Rayyern ya tura kofar dakin ya shiga, bakinsa dauke da sallama.
Amsa masa sallamar nasa Abban yayi, tare kuma da kafesa da ido.
Shikuwa Rayyern anutse ya karaso ya zauna agaban Abban nasa.
Rank’wafar da kansa k’asa yayi, sannan aladabce yace.
“Kayi hakuri Abba, duk da bansan manufarka ta aikata hakan ba, amma Ina mai rokonka daka bani daman zuwa duba lafiyar Malam Mai-nasara, yau akaron farko yazo hospital dinmu, yana kuma cikin halin buk’atar wanda zai kula da lafiyarsa, dan Allah Abbana kayimin wannan alfarmar, domin kuwa hakkina ne na kula da duk wani marar lafiyar da yazo asibitin mu, aiki na ne hakan, nabawa duk wani marar lafiya kulawa, Dan Allah Abba karkace a’a, domin yin akasin hakan tamkar wulakanta marar lafiya ne.”
Idanu Abba ya lumshe, tare da sakin ajiyar zuciya, domin kuwa Tabbas yasan cewar shi ya d’aura Rayyern din, akan turban da duk yanda abu yake, idan aka rokeka da Allah da Manzon sa to zaka aiwatar.
Yasani kwarai ya gina ƴaƴan nasa, akan tubalin tausayawa duk wani mai neman taimakonsu.
Ajiyar zuciya ya kuma saukewa akaro na biyu, kana cikin tausasa murya yace.
“Shikenan tunda ka had’ani da Allah Rayyern, kaje ka dubashi, amma iya taimakon daya kamata kawai zakayi mishi, da zaran yaji sauki kuma, ayau nakeso ka sallameshi banason ya kwana acikin asibitin.”
Dagowa Rayyern yayi fuskarsa dauke da murmushin jin dadi, yace “Insha Allah Abba, idan yaji sauki ayau yau zan sallameshi, nagode sosai da wannan alfarmar!”
Kai Abban ya jinjina, kana shikuma batare da wani b’ata lokaci ba ya tashi ya fice daga cikin dakin.
Direct bedroom d’insa ya nufa, Yayinda ya d’auko wayoyinsa da kuma yan k’ananun abubuwan da yasan dole zai bukata.
Koda ya sauko kasa, haka ya samu Mamy Ramadan Riyyam sunyi zugum.
Kallon Ramadan din yayi, cikin yanayin saurin da yakeyi kuma yace.
“Ramadan zo mu tafi hospital din.”
Ai kuwa jin haka yasa Ramadan mikewa cikin sauri, ya marawa Rayyern din baya, kasancewar tuni harya fara tafiya.
Koda suka fito cikin mota d’aya suka shiga, ak’agauce kuma Hadi drivern yaja motar suka fice daga cikin gidan.
Ak’alla saida sukayi tafiyar 17mn, kafun suka iso babban katafaren Mai-nasara Hospital d’in, wanda aka k’awata gininsa kamar ak’asar turai.
Koda driver yayi parking Rayyern baijirayi komai ba, cikin hanzari ya bude murfin motar ya fita.
Yayinda Ramadan ya take masa baya.
Sulaiman da yanzu fitowarsa daga cikin office dinsa, hango Rayyern din da yayine yasashi k’arasowa da sauri.
Rayyern kuwa ak’agauce, batare ma daya bari sun gaisa da Sulaiman din ba yace.
“Awani ward aka kwantar da Malam Mai-nasara?”
“Emergency ne, amma kuma abisa tunanin ba zai samu ganinka yau ba, yasa Manyan ya'yansa suka daukeshi zuwa wani hospital din na daban.”
Idanu Rayyern din ya kankance tare da dafa kansa, dake sarawa da d’an k’arfi yace.
“Shitt! Why Sulaiman? Meyasa bazaka ce musu sujirani ba?”
Kai Sulaiman yad’an girgiza tare da cewa.
“Nakira duka wayoyinka is not available, gashi jikin nasa yana ta tsananta, kuma kaine wanda ya dace ka dubasa, domin mu munyi iya yinmu, yan uwannasa kuma sun kasa hakurin jiran zuwanka, shiyasa suka daukeshi zuwa wani asibitin daban.”
Idanunsa da suka d’anyi ja ya rumtse, saboda Sam ba haka yaso ba, hakika yaso ace shida kansa ya duba mutumin.
Juyawa yayi ya nufi office d’insa, yana maijin ransa duk a jagule, ga kuma ciwon kansa da a yanzun yake sake karuwa.
Koda ya zauna acikin office din, ji yayi gaba daya zaman asibitin ya ishesa, hakan yasa shi tashi ya fito.
Anan yasamu Ramadan ma na shirin komawa gida, saboda yasan sunbar Riyyam shikad’ai acan.
Kamar yanda suka zo kuwa atare suka koma.
Inda Koda suka shigo cikin falon gidan, azaune suka iske Riyyam-nsra kan lallausan carpet din dake malale a tsakiyar falon, agefensa kuwa Mamy ce, Yayinda shi kuwa yake rik’e da wayarsa yana sana’arsa ta chatting.
Saidai kuma duk da chatting din yake, amma bakinsa baiyi shiru ba, labarai kawai yake ta bawa Mamy kala kala, wanda kuma duk rabin labaran nasa akan Mammynsa da kuma Zaytoon abokiyar tagwaicin sa ne.
Mamy dai itakam zamanta da yaron ya sata nishadi sosai, saboda labarai ne na abun dariya yake bata.
Kallon Riyyam-nsra da Mamyn Rayyern yayi, batare kuma da yace wani abuba kaitsaye ya haura sama, saboda so yake yasha magani ya kwanta, ko zai samu relief na headache din dake damunsa.
Ramadan kuwa zama yayi suka sha hiransu, kafun daga bisani ya kama hannun Riyyam din, suka haura dakinsa dake sama.
Acan b’angaren Jannart kuwa, sunyi waya da Salman.
Inda yake shaida mata cewar.
Ya samu information akan sunan hospital din su Rayyern din, da kuma yanda za ayi su samu ganinsa idan sunje hospital din.
Ajiyar zuciya Jannart ta sauk’e adai-dai lokacin da ta zare wayar daga kunnenta.
Cikin kuma halin Kosawa tace.
“Yah Allah Kataimakeni, ka had’ani da wannan mutumin, da nemansa yafi na kud’i wahala, mutum shiba Diamond ba amma ace wai ganinsa ya zama aiki, yau shine can Gobe shine nan, wai dole saikabi wasu matakai kafun ka iya ganinsa, babban ma abun takaicin shine Kwata-kwata, ko a social media babu wani information akansa, baya Facebook baya Instagram only Twitter kawai, still kuma a Twitter dinma, babu wani information akansa, ko hotonsa babu.”
Yar siririyar tsuka taja, tare kuma da turo dan karamin bakinta gaba, kana ashagwab’e tace.
“Idan ma ba munafurci ba da rashin gaskiya. Meyasa yake boye kansa, da har za’ace kwata-kwata babu wanda ya tab’a ganin fuskarsa? A jaridu ko a TV Maybe ma shidin irin ɗima-ɗiman alhazawan nanne masu tafiya da kyar da kuma katon ciki ne, shi yasa yake boye kansa.”
Momy dake tsaye abayanta ne tace.
“Lafiyarki kuwa Jannart keda wa kike ta tashin k’ananan maganganu?”
Juyowa tayi tare da Kallon Momyn kana ta kwab’e fuskarta.
“Momy aiki aka bani a office, gashi kuma aikin sai wahalar dani yakeyi.”
Ta kare maganar tana me zare earpiece din dake kunnenta.
Dan Murmushi Momy tayi hade da cewa.
“To Allah Ya baki sa’a, amma dai yanzu kam ki ajiye aikin kitchine dinnan haka kije ki huta, zan karasa dafa pepper meat din da kika fara.”
“To Momy.”
Tafad’a a sanyaye tare da ajiye baban spoon din dake hannunta.
Momy kuwa da kallo ta bita harta gama ficewa daga cikin kitchine din, Allah yasani duk da cewar ba itace ta ta haifi yarinyar ba, amma tana matuk’ar so da tausayinta.
Saboda yanda rayuwar yarinyar yake cike da sarkakiya mai daurewar hankali da tunani.
Wanda kuma ita kanta haryau ta kasa gano gaskiyar hakikanin abunda ke boye.
Jannart kuwa Koda ta fito daga cikin kitchine din, anutse take tafiyar ta batare kuma da ta lura da Yah Junaid dake zaune acikin falon yana shan shisha ba, direct ta wuce bedroom dinta.
Dan dauro alwalan sallan Magriba.
Junaid dake zaune kuwa da idanunsa yabi manya manyan hips dinta harsai da ta b’acewa ganinsa,
(Yana ɗaya daga cikin illolin da sa suturun banza suke jawa ɗiya mace, koda kuwa a cikin gidanku ne).
Kafun ya iya rumtse idanunsa, tare da shakawa cikinsa hayakin shisha.
Allah Yasani yana matuk’ar so da buk’atar kanwartasa fiye da komai aduniya.
Domin akanta yakanji kamar ana ingiza sa kowacce rana.
Haka kuma idan dai zai ganta sau dubu da irin shigar data zame mata ɗabi'arta to Tabbas zaiji sha’awarta sau dubu yanayin shigarta ke ingiza lafiyar samartakarsa.
Mikewa tsaye yayi kamar zai bi bayanta kuma sai ya fasa, tare da komawa ya zauna ya cigaba da bankawa cikinsa hayakin shisha, duk da kuwa yanajin ana kiran sallan magriba, amma haka yayi biris tamkar ba yaji.
To dama sallan bawani damunsa tayi ba.
Acan gidansu Rayyern kuwa har akayi sallan Isha suna tare da Riyyam.
Wanda kusan atare ma sukaje masallaci sukayi sallan magriba dana isha.
Yanzu ma kammala dinner dinsu kenan, Riyyam din ya mike tsaye, tare da duban Abba da Mamy.
Cikin girmamawa yace.
“Abba Mamy zan koma masaukina, na kuma nagode da karramawarku sosai.”
Ramadan dake zaune ne ya rik’o hannunsa tare da fadin.
“Haba Riyyam-nsra a daren nanne zaka koma hotel, please ka kwana anan mana, ai duk munzama daya....”
Sauran maganan dake bakin nasane ta makale amakoshinsa, sakamakon mummunan kallon da yaga Abba ya watsa masa.
Shikuwa Riyyam-nsra da bai lura da Kallon da Abban yayiwa Ramadan dinba, murmushi yayi.
Kana cikin nuna godiyarsa yace.
“Kayi hakuri Hamma Ramadan watarana ai Zan dawo.”
Kai Ramadan din ya jinina, Cikin waskewa kuma yace.
“Shikenan ba matsala To muje na saukeka.”
Saida safe Riyyam din yayiwa Mamy da Abba, inda suka amsa masa amutumce.
Kallon Rayyern dake zaune Riyyam din yayi, kana ya dan rankwafo ya rungumesa, cike da k’aunar Rayyan din da yakeji acikin zuciyarsa yace.
“Saida safe Hamma Rayyan.”
Kai Rayyern din yadan jinjina masa.
Yayinda Ramadan kuwa ya kama hannun Riyyam-nsra din suka fice.
Saida suka hau titi ne kuma Riyyam-nsra din yake fadawa Ramadan hotel din da zai kaisa.
Yayinda acan gidannasu kuwa , bayan tafiyar su Ramadan din Rayyern tashi yayi ya wuce bedroom d’insa.
Wanka yayi bayan ya fito ne kuma ya d’auki system d’insa, ya soma latsawa, Yayinda akai akai yake saka nutella chocolate abakinsa.
Agaban babban Hotel din na Taheer Guest Palace Ramadan ya sauke Riyyam, tare dayin exchanging phone number atsakaninsu.
Bayan kuma Ramadan din yace da Riyyam Gobe yazo suyi breakfast tare ne, suka sakeyin sabuwar sallama, Yayinda Riyyam kaitsaye ya wuce cikin hotel din.
Shikuwa Ramadan juya akalar motarsa yayi zuwa gida.
12:30 am dai-dai Rayyern ya kashe laptop dinnasa, tare da mirginawa ya kwanta akan gadonsa.
Wanda daga zaman nasa awajen zuwa yanzu yashanye fiye da rabin Kwalban Nutella chocolate.
Idanunsa yadan lumshe saboda yanda yakejin bacci na game cikinsu.
Sannu Ahankali kuma ya soma ambaton sunan Allah ahaka har baccin ya daukesa.
Acan sashin Riyyam-nsra kuwa, koda ya shiga dakinsa na hotel din, haka ya tarar da komai nead.
Wanka yayi tare da zuwa ya fada kan gado, hade da jawo wayarsa ya runguma, bayan ya kunna data ne kuma ya shiga whatsapp sama sama yayi chatting acikin whatsapp din, kana daga bisani kuma ya dawo ta inda yafi karfi Wato Tiktok.
Atakaice dai saida yakai kusan 2am yana sheke ayarsa kafun bacci barawo ya daukesa, haka kuwa yayi baccin yabar data d’insa akunne.
Washegari.
Kamar koda yaushe yauma 7:30 am ya gama shirya kansa tsab, cikin royal high quality black suit, tare da white long sleeve wacce tayi masa kyau sosai.
Kasancewarsa mai kyau ne kuma shiyasa komai ya saka saiyayi masa kyau.
Ahankali yake saukowa daga kan steps din falon, Yayinda briefcase d’insa ke rike ahannunsa na dama.
Mamy dake tsaye tana shirya dining table ne ta dago ta kalleshi.
Ɗan guntun Murmushin gefen baki yayi, wanda ya ɗan bayyana fararen haƙoransa, kana cikin nitsuwa yace.
“Good morning Mamyna.”
Murmushi itama Mamyn tayi, cike kuma da soyayyarsa tace.
“Morning My beautiful son, kafito a dai-dai maza zokayi breakfast dinka.”
Karyar da wuyansa gefe yayi, tare kuma da duban agogon hannunsa.
Muryarsa adan sanyaye yace.
“I’m sorry Mamyna yau sauri nakeyi, amma idan Ramadan yazo fita ki hada masa breakfast dinnawa a basket ya kaimin office.”
Murmushi Mamy tayi tare da cewa.
“To ba matsala adawo lafiya Allah ya tsare ya kuma bada sa’a.”
Da “Ameen.” Ya amsa kana cikin jin dadi ya Sakai ya fice daga cikin falon.
Dai-dai fitowarsa compound din gidanne kuma, Riyyam da Ramadan suka shigo atare.
Cikin sauri Riyyam ya karaso, tare Da dan rungume Rayyern din, fuskarsa dauke da Murmushi yace.
“Good Morning Hamma Rayyern!”
Idanu Rayyern din yadan lumshe tare dasa hannu ya shafa kan Riyyam din, cikin kuma yanayinsa na rashin sabo dayin magana yace.
“Morning Riyyam, Ina fata kunyi waya da Naseer yau, ya jikin Malam din?”
Kai Riyyam din ya jinjina tare da fadin.
“Eh munyi waya dashi, ya kuma tabbatarmin cewa jikin Malam din da sauki.”
Kai Rayyern din ya jinjina tare da cewa.
“Okay bani numbern Naseer din.”
Yafada yana me mikawa Riyyam wayarsa dan yasa masa numbern Naseer.
Ramadan kuwa kai ya jinjina cike da gamsuwar lallai Hamman nasa ya dauki lamarin malam da matuƙar mahimmanci.
Hakan kuwa akayi domin cikin abunda bai wuce 1mn ba Riyyam ya sakawa Rayyern din numbern.
Ramadan kuwa dake tsaye fuskarsa dauke da dan mamaki yace.
“Hamma Rayyern me zakayi da numbern Naseer kuma?.”
“Zanje na duba Malam Mai-nasara ne, tunda har Abba ya a mince dana dubasa din, tofa Tabbas saina duba sa, zan kira Naseer din idan basa hospital har gidansa zanje na dubasa.”
Rayyern din ya fada in full confidence.
Ramadan kuwa Kai ya jinjina cike da gamsuwa, sai kuma suka hada baki atare shida Riyyam wajen cewa suma zasuje gidan Malam Mai-nasara din.
Kansa kawai ya kad’a, adai-dai kuma lokacin da yake shiga cikin motarsa yace.
“Okay nidai yanzu hospital zan wuce, sai Idan na tashi ne zan biya can gidan nasa, amma idan kuna da chance zaku iya zuwa maybe mu hadu acan .”
Yana gama fadan hakan yaja murfin motar ya rufe, batare kuma daya saurari mai zasu sake cewa ba, yasa Hadi driver yaja motar suka bar wajen.
Su kuwa Ramadan da Riyyam kaitsaye cikin gidan suka wuce.
Koda suka karasa cikin falon Riyyam aladabce ya gaishe da Mamy da kuma Abba wanda yake yanzu fitowarsa daga daki.
Cikin farincikin ganinsa Mamy ta amsa, Yayinda Abba ma ya amsa masa fuska asake.
Anan kan dining table sukayi breakfast.
Bayan kuma sun kammala ne Riyyam da kansa ya gyara wajen, tare da kai plates din da suka bata kitchine ya wanke.
Mamy kam cike da mamaki take kallonsa, domin kuwa duk da ta hanashi saida yayi, inda yake bata labarin cewa ai yanayiwa Mammynsa ma, saidai watarana dagangan sai yakiyi dole Zaytoon ce zatayi.
Mamy dai itakam dariya kawai takeyi, saboda daga jiya zuwa yau din kawai, zama da yaron ya zame mata sabo.
Abba kuwa ido ya zuba musu da inda yake zaune can tsakiyar falon yana nazartar ƙarfin halin Riyyam-nsra da shisshiginsa garesu anya kuwa!?.
Ya ɗiga ayar tambaya a kan yaron.
Acan hospital kuwa Rayyern bayan yadan duba wasu daga cikin patients dinsa ne, ya d’auki waya ya kira Naseer.
Bayan sungaisa ne kuma yake tambayar Naseer din, jikin Malam Mai-nasara.
Tofa ananne Naseer din yake fada masa cewar.
“Ajiyan ankai Malam din Zanna Hospital, amma kuma an sallamosu Yanzu dai Malam din yana gida, kuma babu laifi jikin da d’an sauki. “
Kai Rayyern din ya jinjina, tare da cewa Naseer din ya turo masa adireshin gidan Malam din zaizo anjima.
“To.” Naseer din ya fada cikin minti kadan kuwa ya turowa Dr Rayyern din, da text message na address din gidan Malam Mai-nasara.
12: am dai-dai Rayyern ya kammala duk wani abu abunda yakeyi acikin hospital din.
Haka ya fito daga cikin office dinnasa yana taku cikin nitsuwa da kuma zarransa dake kara bayyana kwarjininsa da haiba na cikakken da na miji.
Kaitsaye compound din asibitin ya nufa, yana zuwa kuwa ya shige cikin motarsa batare da bata lokaci ba, driver yaja motar suka fice daga cikin asibitin gaba daya.
Bayan sun hau titi ne kuma drivern ya juyo yadan kallasa, kana aladabce yace.
“Ranka ya dad’e Ina muka nufa?.”
“Hausawa sabon titi.” Ya fada atakaice.
Tare da sanya hannu ya zare glass din dake manne a idanunsa.
A dai-dai wannan lokacin kuwa Ramadan Riyyam da kuma Naseer ne, acikin motar Ramadan din kirar Range rover velar 2019, inda suma kaitsaye suka nufi Unguwar ta Hausawa sabon Titi, wanda suna tafiyar ne kuma bisa jagoran Naseer.
After some 20mn suka iso gaban wani gate din makeken gida mai tsananin kyau da girma.
Wanda kuma yake nanne gidan Malam Mai-nasara.
Horn Ramadan dake driving ya danna.
Jin karan horn dinnasa ne kuma yasa maigadi, Dan lekowa ganin dalleliyar motar da yayi ne da kuma Naseer a gaba ne yasashi karasawa da hanzari ya wangale babban farin gate din.
Wanda hakan ya bawa Ramadan daman tura kan motar tasa ciki.
Wanda shigansu cikin gidan kuwa. yayi dai dai da wani irin masifeffen bugawar zuciyoyin Riyyam-nsra da Ramadan.
Kokarin maida gate din maigadin yasomayi saidai kuma ganin wata dakekkiyar motar again BMW ta faso kaine, yasashi wangale gate din.
Inda matukin motar ya tura hancin motar ciki.
Wanda saukan tayoyin motar acikin gidan, yayi dai-dai wani irin azabebben harbawa da zuciyar Dr. Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara yayi.
Cikin wani irin matsanancin faduwar gaban da yakeji, da kuma dukan da zuciyarsa keyi ya bud’e idanunsa inda ya saukesu A...!
Fawal beauty parlor sunai muku albashir da bude gidan Mata wato kigyara da kanki👩🏻🦰 da cewa suna gabatar da aiki na zamani kamar su gyaran jiki, spa kenan gyaran fuska wato facial,gyaran Kai, hair style , gyaran kafa pedicure,gyaran hannaye,