Showing 9001 words to 12000 words out of 350584 words

Chapter 4 - Tubali Book 1 Hausa Novel Complete

shafinsa na TIKTOK.
Kun san matsalar su kenan ƴan TIKTOK duk abinda zasuyi ko sukeyi sai sun nunawa duniya, More Especially irin Riyyam-nsra da yayi shuhura yayi zarra da dubban dubatan masoya mabiya, musamman a cikin kwanakin nan da yai mgn da Hausa ya janye mana hankalin matasan Nigeria, domin kuwa ayanzu followers d’insa harsun d’arawa two million.
Gane abin da yayi dinne kuma yasa. Mammy matsoshi da kyau ta kama kunnenshi ta ɗan matse.
Ƙara ya kuma ɗan saki, wanda yasa Zayton tuntsirewa da dariyar jin daɗi tana ɗaga mishi gira.
Ita kuma Mammy cikin ɗan faɗa tace.

“Wato kai Riyyam baza ka taɓa canzawa bako, duk motsinmu sai ka bazamu a duniya? Kai kam inaga kana gab da nuna duniya yadda kake kashi ma ko".
Hannunshi yake ɗan yayyarfawa tare da cewa.
"Afwan Yaah Mammy na tuba, wayyo Hamma Mammy zata tsinke min kunne".
Dariya Zayton tayi tare da cewa.
"Zai aikata fiye da hakama Mammy ja kunnen da kyau".
Hannunshi ya kai ya bugi hannunta tare da cewa.
"Yarinyar nan ki shiga hankalinki fa".
Fuska ta haɗe tare da cewa.
"Waye yarinyar yaro in ka manta in tuna maka nice babba 15 minute nake baka, kaga kuwa dole ace da mijin iya baba, dan 15 minute ba 15 second bane".
Sosai Mammy ta saki murmushi suna matuƙar sata nishaɗi da ɗebe mata kewa, da danne mata duk wani ƙuncin rayuwa, Especially in suna faɗa kan girma.
Zayton son girma kamar gyambo, 15 minute da take bashin nan ji takeyi kamar shekaru goma sha biyar take bashi.
Gefe ta zauna kana suka zo suka sata a tsakiya.
Cikin sakin fuska ta shafa kan Riyyam-nsra tare da cewa.
"Zoh nan autana".
Gwalo yayiwa Zayton tare da ɗaura kanshi bisa cinyarta tuni kuma ya sake haɗa video.
Murmushi yakeyi yana yiwa Zaiton signal tare da cewa.
"Mammy asamin al'barka".
Da sauri itama ta sako kanta tare da cewa.
"Mammy ai nice mace, dan haka ya riƙe girman ya matsa ni in kwanta".
Cikin yin ƙasa da murya Mammy tace.
"Ya isa haka ku bari, Dida na bacci kada ku tada min ita".
Toh sukace dan yadda tayi mgnar ba wasa.
Bayan ya saki wannan video ɗin ne kuma.
Ya gyara zamanshi ya fuskanci Mammy da kyau jin tana cewa.

“Riyyam sam hankali na. baya kwanciya da wannan rawan kan naka! Ina jin tsoron kayi nesa dani, gaba ɗaya ka juye ka zama ɗan nanaye, ka zama tamkar mazari duk inda kake sai rawa, sai waƙa, sai haɗa comedy duk inda kake waya na hannu, kai kaɗai a ganka kana dariya ko kana kuka ko kana haɗa fuska ko layi, kai gasu nan dai barkatai, ka zama ɗan Film a fili ka rubuta lbri ka tsara ka bawa kanka umarni kayi shirin.
Ga ɗan karen yawo yau kace zaka tafi waccar ƙasar, gobe kace zakaje waccar gashi ka zama babu sirri duk inda kake an sani, shiyasa nake jin tsoron zuwanka Nigeria duk inda kaga mata sai ka bisu da ido".

Da sauri ya gyara zamanshi cikin nitsuwa kamar ba shiba yace.
"Mammy babu komai sai al'khairi, ki yarda dani bana wani mugun abu, in ke bakya gani na ai Ubangijin talikai daya busan numfashin yana ganina".

Uhum tsakanin uwa da ɗa kenan ya gane cewa tana zargin shi ne ko tana tsoron taɓarɓarewar tarbiyarshi.
Cikin sauƙe nannauyan numfashin tace.
"Wlh badon dole ba, bazaka jeba, amman ba komai Allah ya kaika lfy ya dawo da kai lfy.
Sai dai dole ka nitsu ka dena wannan rawan kan".

Hannunshi yasa ya kame kanshi kana yace.
"Toh Mammy na dena".
Murmushi tayi hakama zaitun.

Washe gari ranar Laraba, Kano Nigeria.

Cikin bacci taji numfashin ta, na fita a cushe, kana tana shaƙan zazzafan ƙamshin turaren sa mai masifar ƙarfi da tafiya da numfashin ta.
Idonta ta buɗe cikin wahalar numfashi.
Da sauri ta ida buɗe su duka tare da fisgo numfashin ta a wahalce.
Sabida ganin Yah Junaid da tayi sunkuye a kanta hannunshi na kan ƙirjinta.
Wani irin tsuma da karkarwa jikinta ya farayi, da azaban ƙarfi.
Cikin tsananin tsoro da razanin ta yunƙuro zata tashi, tare da furta "innalillahi wa innalillahi raji'un."
Wani irin azabebben tsoro firgita kaɗuwa da gigitane suka dirar mata lokacin ɗaya jin yadda yasa hannunshi ya matse ta tare da murtuƙe fuskarshi.
Cikin tsananin rawan jiki take zaro ido murya da baki na rawa tace.
"Innalillahi Wa’inna Ilaihirraju’un Y... Ya... Yah... Juna..Junaid, me haka!!”

Wani irin masifeffen kallo ya watsa mata, tare da kai hannunshi duka biyu kan breast ɗinta, yayi musu wani irin masifeffen kamu wanda yasa ta saki wani irin gigitaccen ƙara, lokaci ɗaya kuma numfashin ta ya fara off and Dawn, ciwonta na gab da tashi.
Shi kuwa Junaid wani irin sanyi yakeji a ransa tare da rumtse tafin hannunsa.
Mom kuwa dake ɗakinta, ita da Abdul cikin razanin jin sautin muryar Jannart ta miƙe tsaye jiki na rawa, ta fito falo.
Dai-dai lokacin kuma Jannart ɗin ta fara wani irin fiffizgewa sabida numfashin ta dake shirin barin gangan jikinta.
Wata iriyar fitinenneyar zufa mai cike da zafi, ta fara tsastsafo mata tako wani hudan gashin jikinta.

“Hahhhh! Uhhhhhhhh!! Fuhhhhhhhheeeeyyyy!!! M...Mom!"
Ta fuzgo maganar da ƙarfi lokaci daya kuma numfashin ta ya dena shiga sai fifita.
Jiki na rawa Mom ta kutsa kanta cikin ɗakin nata.
Shi kuwa Junaid wani irin fitinenne abu yakeji yana tsirgar masa.
Hannunshi ya kirjinta. Tare da yiwa breast ɗin ta wani azabebben riƙon da saida yaji.
Gamsuwa shaiɗan cinsa.
Kana ya juya ya nufi ƙofar fita.
A bakin ƙofar sukayi kiciɓis da Mom.

Wani irin mugun kallo ya watsa mata.
Ita kuwa Mom wani irin kallon tuhuma take binshi dashi.
"Mchewww".
Taja wani dogon tsaki ganin bazai bata hanya bane yasa ta matsa gefe.
Wucewa yayi tare da cewa.
"Sai kiyi ai".
Ita dai bata bi ta kanshi ba, ta wuce cikin ɗakin.

A gigice ta nufi kan gadon tana kiran ta.
"Jannart! Jannart!! Jannart!!!".
Ta Ƙarisa kiran sunanta a gigice tare da hawa kan gadon ta jawota jikinta tana cewa.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun. Abdul! Abdul kazo".
Da gudu Abdul ya nufi ɗakin sabida dama yana falo Juinad ne ya hanashi shiga.
Cikin ruɗani tace.
"Abdul kira min Daddynku. Ka gaya mishi jikin Jannart ya tashi".
Da sauri yace.
"Toh Mom amman bari in fara kiran Dr Lukman".
Ya ƙare mgnar yana kara wayarshi a kunne.
Ita kuwa Mom sai jijjiga Jannart daketa kokuma da numfashin ta takeyi.
Cikin rauni Abdul yace.
"Assalamu alaikum. Daddy".
"Na'am Abdul ya akayi ne?".
Alhaji idi sele Dakata dake zaune a Office nashi Barrister Kabir Saleh Dakata na zaune a gabanshi.
Ya amsawa Abdul da kulawa.

“Daddy jikin Jannart ne ya tashi, na kira Dr Lukman kuma baya ɗagawa".
Da sauri yace.

“Innalillahi Bari in kirashi yanzu-yanzu".
Ya ƙare mgnar da katse kiran.
Cikin kula Barrister Kabir Dakata yace.
"Yaya lfy kuwa? Jikin Jannart ko?".
Cikin damuwa yace.
"Eh".
Miƙewa tsaye yayi tare da cewa.
Bari inje mu tafi asibiti".

Tuni kafin yayi wata magana ma ƙanin nashi ya fita.
Abdul ya kuma kira tare da cewa.

“Ga Abbanku na zuwa da likita".
Toh yace kana ya katse kiran.
Shiru yayi yana nazartar irin son da Ƙanin nashi keyiwa yaranshi, Especially ma Jannart yana mata wani irin so na musamman.
So na da ban a cikin yaranshi.
Ajiyan zuciya ya sauƙe tare da meda kai ya jingina da kujera.
A hankali yake jujjuyawa, yana mai ƙoƙarin kauda tunanin da zuciyarsa ke kawo mishi.

Shi kuwa Barrister Kabir yana fita kai tsaye.
Asibitin Hamda
Ya wuce. Yana mai kiran babban Dr.
Yana tafe cikin gudu kamar maiyin doguwar tafiya.

Yana isa kai tsaye Office ɗin Dr Sajo ya wuce.
Yana ganinshi ya miƙe tsaye tare da cewa.
"A a Ƙanina! Ka iso, ko ina mara lafiyar?".
Cikin girmamawa da alamun tsohuwar amintaka yace.
"Barka dai Yaya Sajo, dan Allah kayi haƙuri mara lafiyar tana gida.
Ni kuma daga Campany’n Yays Dakata nake, so kafin in koma gida in ɗaukota komai zai iya faruwa, kasan matsalar cutar athsman shiyasa nace bari in biya mu tafi tare. Dan Allah kayi haƙuri".

Murmushi Dr. Sajo yayi tare da fara tattara abin buƙatarsa yana mai tuno amintaka da mutuntakar da ke tsakaninsa dasu a baya.
Cikin kuma kula da amintaka yace.
"Ba komai ƙanina muje, dama na gama yau bani da aiki".
Cikin jin daɗi ya juya ya fita, shi kuwa yana biye dashi a baya.

Motarshi suka shiga, shiyasa yake taka motar da kyau.
Tsoro yakeji yasan yadda ciwon ke wahalar da ita.

A can gida kuwa, gaba ɗaya Mom da Abdul sun rikice.
Ita kuwa Jannart tuni ta gama gigicewa ta fita haiyacinta, fuskarta nan tayi jazir.
Sai fuzgo numfashin takeyi da ƙarfi.

Wayar Abdul ne tai ringing yana ɗagawa yace.
"Abba jikin fa ya tsananta".
"Subahanallahi Abdul gani nan zuwa yanzu".
Toh yace kana ya katse kiran.

Suna isa kai tsaye cikin gidan sukayi.

Abban na gaba Dr Sajo na biye dashi a baya.
Suna shiga Dr. Sajo ya fara aikinsa, allura yayi mata dan samun dai-dai-ta numfashin ta.
Allah cikin ikonsa kuma a take ta fara sauƙe ajiyan zuciya, lokaci ɗaya jikinta ya fara sakewa.
Sai ga wani irin bacci mai nauyi ya kwasheta...

Kusan a tare suka sauƙe ajiyar zuciya baki ɗayansu.
Cikin kuma sauƙe numfashi Abba yace.
"Alhamdulillah".
Hakama Mom.
Abdul kuwa shiru yayi yana mai jin tausayin yar uwar tasa.

Dr. Sajo kuwa, harhaɗa kayan aikinshi yayi, kana ya kalli Barrister Kabir, gyaran murya yayi tare da cewa.

“Ciwonta yayi zurfi a jikinta, kuma bata bin doka da ƙaidar maganin yadda ya kamata".
Da sauri Mom tace.
"Ai ba'a bata magani Allura kawai akeyi mata duk wata".
Cikin mamaki yace.
"Allura kuma? Toh wacce iriyar Allura ce duk wata kuma!?."
Cikin sanyi Abdul yace.
"Gaskiya bamu san wacce iriyar Allura bace".
Da sauri Dr Sajo ya kalli Barrister tare da cewa.
"Wanne Dr ne yake duba ta?".
Numfashi mai nauyi Barrister ya sauƙe kana a hankali yace.
"Dr. Lukman ne".

Wani irin shiru Dr Sajo yayi tare da alamun nisan nazari.
Kana yace.
"Ok muje ko Barrister".
Toh yace kana suka nufi hanyar fita.
Sai kuma ya ɗan juyo ya kalli Mom dake gyarawa Jannart din kwanciyarta, cikin nitsuwa yace.

“Kada ki damu, zata samu lfy in sha Allah, sannan zamu canza mata Dr da zai na kulawa da ita da kyau".
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
"Mun gode".

A hankali Dr. Sajo ya juyo ya kalli Barrister Kabir dake jan mota, dan medashi asibitin sa.

“Ƙanina akwai buk’atar a canzawa Jannart likitan da zaina dubata.”

Cikin nitsuwa Barrister Kabir ya ɗan juyo ya kalleshi tare da cewa.
"Yaya Sajo meyasa!?".
Kafaɗarshi ya ɗan ɗaga tare da cewa.
"Noh ba komai, kawai dai ciwonta yanada buƙatar gamayyar likitocin zamani bawai a tsaya kan ɗaya ba, a samo wani shima ya gwada kwarewar sa".
Uhum Dr.Sajo bai tuna cewa da babban Lawyer yake mgna ba.
Cikin fahimtar wani abun Barrister Kabir yace.
"Toh ba matsala in sha Allah za'ayi haka. Amman ina zamu samu likitan?".
Da sauri yace.
"A wannan mai sauƙine, akwai wani Babban Doctor yarone matashi mai ƙuruciya da sanaiyar ilimin likitanci na juya da yau, kana harna gobe yana bincika yasan aikinsa, mun gamsu dashi, Dr Rayyern Mai-nasara."
Da sauri Barrister yace.

“Zakayi mana hanyar ganinshi kenan? Dan ance yana da wuyar gani".
Ya ƙare maganar yana yin parking.
Kai ya ɗan juyo ya fuskanceshi tare da cewa.
"Eh to Gaskiya yana da wuyar samu, saboda yawan aiyuka, kuma a wani sashin bashi da wuyar gani, in har kaje Mai-nasara Hospital ɗinsa, muddin dai yana ƙasar, toh zaka ganshi sai dai ko in baya ƙasar, in kuma bakayi sa'a ba, sai a turaka wurin wani Dr ƙaninsa da kuma amininsa ɗin ba shiba, tunda yanzu aikin Company's dinsa sun tasoshi gaba, dole ya samo wasu likitocin bayan shi.
Saɓanin da da shi kaɗai ke jan ragamar asibitin.
Amman idan nasa hannu na baku takarda zuwa gareshi kuna zuwa shi ɗin zaku gani".

Cikin gamsuwa Barrister yace.

“Alhamdulillah nagode matuƙa Yayana".
"Haba ba komai Kabir yiwa kaine. Yauwa sai kuma batun allurar da akeyi matan nan, abar yi matashi akwai buƙatar in santa, sannan ina son sanin sunan allurar".
Ya ƙare zancen yana fita daga cikin motar.
Cikin gamsuwa Barrister yace to.
Kana sukayi sallama.

Ganin lokacin sallan azahar yayine kuma yasa ya nufi masallaci.
Koda aka idar da sallah kuwa.
Gidan yayan nashi ya koma.


Ethiopia.
Dr Rayyern Mai-nasara ne. Tsaye cikin wasu tattausan Suit masu masifar kyau da taushi tare da sheƙi.
Inda Riga da wondon suit din suka kasance pink color masu dauke da zane-zanen fari, sai kuma neck tie ɗin shi daya kasance fari, yayinda long sleeve dinsa ma ta kasance white, takalmin dake kafansa kuwa pink color ne mai dauke da harafin R-M.
Sai kuma Diamond watch din dake hannunsa mai ɗan karen sheƙi da tsada.

Wayarshi kirar iphone 12pro max ne saƙale a kafaɗarshi yayinda ya mannata a kunne yana magana.
Kana kuma hannunshi ɗaya na riƙe da System ɗin shi. Daya hannunshi kuma na lallatsashi.
Bisa alamu aiki mai muhimmanci yakeyi.

Ga kuma wani irin masifeffen ƙamshi mai ɗan karen daɗin shaƙa da yake fitarwa.
Lallausan Sajenshi nan ya kwanta lib, yayiwa kyakkyawar fuskarsa kawanya sai sheƙi yakeyi.
Haka kuma Ɗan madaidaicin bakinsa mai jajayen lips na motsawa a hankali.

Yayinda siraran idanunshi suka fito ras, cikin ɗan siririn glass mai ruwan garai-garai, irin na Doctor's daya liƙashi cas bisa karan hancinsa.

A hankali ya juyo ya kalli Usman daya shigo cikin alamun shiri.
"Sir gani". Usaman ya fada anutse.

Da idanunshi yayi masa nuni da jakarsa, yana maici gaba da maganar da yakeyi a wayar.
"Uhumm". Yace tare da lumshe idonshi.

A can ɗaya sashin kuwa ba tare da damuwa ba Sulaiman yaci gaba da magana.
Sabida sanin haka Allah ya halicce Rayyern mafi akasarin lokuta maganar Uhumm, ne ko eh ko hmm koko a'a
Bai cika yawan surutu ba, da fari gani suke miskilanci ne, sai daga baya suka fahimci abin da gaskene. Dan muddin za'ayi ta surutu ko hayaniya ko magana da ƙarfi a kanshi ko kukan yaro ko babba, a take idanunshi ke kaɗawa suyi jazir, lokaci ɗaya ciwon kai ke rufeshi larurarsa.
Ido ya ɗan juyo yana kallon Usman dake tsaye gefenshi.
Yayinda kuma yake jin Sulaiman na cewa.
"Wallahi Rayyern ni kamanninku ya daina bani mamaki yanzu sai dai tsoro, Allah ko da yayi magana da hausa ko muryarshi iri ɗaya da Ramadan kuma".
A hankali yace.
"Hmmm Sulaiman social media ka biyewa ko?".
Da sauri yace.
"Dan Allah tsaya kaji, yaushe zaku dawo?".
A taƙaice yace.
"Jibi!".
Cikin fidda numfashi Sulaiman yace.

“Toh gashi kuma shi yaron yau zai taho Nigeria, ni nai zaton yau nema zaku dawo ince Allah yasa ku haɗu a jirgi kaga zahiri, abu kamar an dama kunu an raba har ɗan makolloto yake dashi irin naka fa".

Ɗan gajeren numfashi mai d’auke da gajiya Rayyern ya fesar tare da cewa.
"Uhmm, it’s Okay a gaida Baby".
Yana faɗin haka ya katse kiran.
Sai kuma ga wani kiran ya shigo.
Da sauri ya zauna bisa kujerar bayanshi kana ya amsa kiran.
Cikin tsananin girmamawa hade da ladabi da biyayya da kuma tarin mutuntaka yace.
"Assalamu alaikum".
A can ɗaya sashin kuwa, wani kyakkyawan mutum ne mai cikar haiba kamala ne, zaune.
Alhaji Bashir Muhammad Mai-nasara kenan, sai Mami mai ɗakinshi dake gefenshi.
Kana ɗan matashin ƙaramin ɗansu Dr Ramadan Mai-nasara na zaune gaban Abba'n nasu.

Cikin tarin so kula bege da kuma ƙauna,
Alhaji Bashir ya gyara zamanshi tare da cewa.
"Wa alaikassalam".

Cikin jin daɗin jin muryar mahaifin nashi yace.
"Abba Barka da safiya".

"Barka dai Rayyanu".

Ido ya lumshe cike da son mahaifin nashi yace.
"Abba kuna lafiya?".

"Lafiya lau Alhamdulillah, ga Mamynku da Ramadan wai in tambaya musu yaushe zaka dawo, suna kewarka".

Murmushin gefen baki daya bayyana fararen kyawawan haƙoransa yayi, cikin kuma sauƙe numfashi yace.
"Nima ina kewarku Abba in Sha Allah yau ina hanya amman Abba kai kaɗai fa".
Murmushi yayi fahimtar cewa.
"Shi kaɗai yasan yau zai dawo kenan."
Ramadan kuwa murmushi yayi sabida jin abinda Hamman nashi ya faɗa.

Mamy kuwa Kekkyawar mace mai cikar haiba, murya ta ɗan ɗaga tare da cewa.
"Toh me zan dafa maka".

Idonshi ya lumshe fahimtar sun jishi kenan.
Cikin sanyi yace.
"Mamy'na komai ma".
Amsar wayar tayi tare da cewa.
"Cin zaƙi zai Barka kaci abinda zan dafa maka ko?".
Cikin fuskar annuri yace.
"Yesssss! Mamy".
"Toh shike nan Babana Allah ya kawo min kai lfy".
"Amin Amin Mamy".
Yace cikin lumshe ido
Daga nan sukayi sallama.
Kana ya juyo ya kalli Usman kana a taƙaice yace.
"Mu je".
Da sauri Usman yace.
"Sir ina muka nufa?".
Cike da mamaki Usman ya ɗago kanshi da sauri ya zuba mishi ido cikin al'ajabin jin yana cewa.
"Nigeria".
Ya buɗe baki zaiyi magana ya ɗaga mishi hannu tare da nuna mishi ƙofar fita.

Haka yasa ya gimtse maganar kana ya ɗauki kayyakin nasu
Suka fita.


Boke International Airport Addis Ababa Ethiopian.Suka nufa kai tsaye

Still Kai tsaye Airport parking suka nufa.
Bayan Driver'n'shi yayi parking.
Da sauri Usman ya fito ya buɗe mishi, marfin motar.
Cikin nitsuwa ya zuro ƙafarsa ta dama waje , tare da sauƙeta ƙasa ahankali, Saidai kuma da sauri ya rumtse idanunshi tare da dafe ƙahon zuciyarshi saboda wani irin m...!





📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*TUBALI*
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

ASSALAMU ALAIKUM, Masoyana ma karantan littattafaina, ina mai farin cikin sanar daku, yau d’in nan MON, 18 OCT 2021 za'a fara biyan kud’in samun damar karanta littafin TUBALI akan farashi mai sauk’i Biya 500 k’aramin farashin na k’aramin group, kana sai *Special people Group* akan farashi mai sauk’i 1k kacal babban group a yawan posting babancinsu yake, zaku biya ta asusuna.

ACCOUNT NO 0661110170.

BANK NAME: AISHA ALIYU GARKUWA

BANK GTBank

sai ki turo min shaidar biyanki ta wannan numben tawa da nakeyin whatsApp da ita 09097853276.

*PLS TAKE NOTE BAND VTU*
kada kiyi min VTU ko transfer'n katin ta wannan numben etisalat d’in idan kuwa kikayi wlh babu ruwana dan na fad’i miki. Please and please in dai da hali kada ki turo min katin, kiyi min transfer'n ruwan kud’i ta bank account na, in kuma babu dama to sayi katin MTN sai ki copy number's ɗin katin ki turo min ta whatsApp.

Gareku mutanen jamhuriyar Niger ku tuntub’i Mommy akan layinta +22790899076, ta wurinta zaku biya, hoton katin zaku d’auka ku tura mata ta wannan numben a whatsApp, Special people group 1k ne (1000) k’aramin group kuma (500) kacal,
Please dan Allah babbar macece mai yara da tarin jikoki da y’ay’an jikoki mu kyautata lafazi da mu'amala gareta dan Allah don in ka girmama iyayen wasu wasu zasu girmama naki🙏🏻...

Littafin TUBALI littafine na musamman mai


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login