Showing 75001 words to 78000 words out of 350584 words

Chapter 26 - Tubali Book 1 Hausa Novel Complete

duk kan maza nata shirin zuwa sallan jumma'a tako ina.

Sha biyu da rabi dai-dai haka take a gidansu Dr Rayyern Mai-nasara ma.

Yayinda hakama Barrister Kabir kasan cewar duk a Nassarawa G.R.A suke yasa gaba ɗaya masallacin Al'furƙan suke da niyar zuwa.


A hankali ya kalli Mamy dake ce mishi.
“Toh Rayyern me kake so in dafa maka ne? Ni bana son zamanka da yunwar nan fa”?.
Yana mai haurawa saman yace.
“Mamy yanzu lokacin jumma'a ya ƙara to, bari inje inyi shirin salla in na dawo zanci abincin”.
Da ido kawai ta bishi ganin tuni ma ya haura sama.

A hankali ya ɗan juyo ya kalli ƙofar Bedroom din Ramadan jiyo muryarsa shida Riyyam-nsra alamun suma shirin tafiya jumma'a sukeyi.
Dan yana jiyo muryar Riyyam-nsra na cewa.
"Nima fa mai gare zaka bani in saka Hamma Ramadan”.
Kai kawai ya jinjina ya wuce Bedroom ɗinsa.
Kai tsaye Bathroom ya wuce.

Bayan 15mn ya fito ɗaure da towel.
Gaban dreesing mirror'nsa ya nufa cikin yanayin sauri-sauri ya busar da sumar kanshi tare da shafa mai kana ya miƙe ya nufi gaban ƴar ƙaramar Driver'n'shi na glass dake gefen babban durowar.

A hankali ya buɗe, ido ya ɗan zubawa ƙananan kayanshi dake kimtse a ciki.
Wata tattausan boxer and single ya zaro masu ɗan karen taushi.
A hankali ya meda marfin ya rufe, sauri-sauri yasasu kana ya zare towel din ya cilla gefe ganin ɗaya ta kusa cika.

Babbar durowar ya buɗe,
Wasu kayan ya zaro Getzner fara ƙal mai masifar kyau da sheƙin maiƙo.
Riga da wondo.
Sauri-sauri ya saka su.
Kana ya koma gaban Driver'n'shi na glass din hula damanga ya zaro Royal blue kalan zaren surfanin da akayi wa Getzner aikin rigar.
Sunkuyowa ya ɗanyi toms masu masifar kyau samfarin Italy ya zaro suma Royal blue.
Kana ya dawo gaban dreesing mirror'nsa.
Kafa hular yayi irin kafin nan da matasa ke cewa.
Babu ruwanka da duniya.
Wato ya ɗan ture hular ta koma baya kaɗan hakan yasa tattausar sumarshi ta fito tana zuba sheƙi sajenshi ya kwanta lib sai sheƙi yake siraran lips dinsa suma suna sheƙin taushi.
Sai kuma ya sunkuyo yasa fararen sawunsa cikin takalman.

Agogon Daimond dake kan mirror'n ya saka.
Turarensa Oud Zauji mai masifar daɗin shaƙa ya fesa.
Kana ya zari car key ɗinsa Dan lokacin ya ɗan so ƙure mishi.

Da sassarfa ya sauƙo kan steps din har yana takawa bibbiyu.

Ba kowa a falon yasa da sauri yasa kai ya fita, ko su Baba Mauɗo duk sun tafi sai Ari.


Haka yasa ya buɗe mishi gate kana Suka tafi tare haka nan yake ta jin tsinkewan zuciya da faduwan gaba.

Numfashi ya ɗan fesar lokacin daya shiga cikin masalacin sabida har yanzu huduba akeyi.

Inda ake hudubar akan illar cin riba.

Sosai aka nitsu, bayan an ida hudubar ne kuma aka kabbarta sallan...

Bayan sunyi raka'a biyun, an zauna zaman tahita.
Sun ida zasuyi sallama sunyi gefen dama sun juyo hagu.
Kenan Barrister Kabir ne dake gefen daman Rayyern ɗin ne ya ɗan leƙo fuskar Dr Rayyern bayan ya sallame.

Wata iriyar sassayar ajiyar zuciya mai nauyi ya sauƙe tare da ɗaga hannunshi sama ya fara yiwa ubangiji kirari cikin zuciyarsa yana ƙara neman zaɓin Allah kan manufarsa da addu'a in al'khairi ne Allah ya nufeshi da ida nufinsa a wannan lokacin.
Yayinda shima Rayyern da mafi akasarin mutane hakan sukeyi.
Bayan an idar da salla ne, Dr Rayyern na fita yaji an riƙo hannunsa tare da ce masa.
“Assalamu alaikum”.
Da sauri ya juyo tare da cewa.
“Wa alaikassalam”. Fuskarshi ya ɗan yamutsa alamun tunani kana a hankali yace.
“Lfy”.
“Lfy lau Alhamdulillah Dakta”.
Barrister Kabir ya faɗa yana mai jawo hannun Dr Rayyern ya nufi can kan titi wurin motarsa.

Ba tare da ya ƙara mgna ba yabi bayansh.
Suna zuwa ya buɗe suka shiga....!

Anan asibitin kuwa, da Yamma Dr Sulaiman ya bawa Barrister Kabir takardar sallama, sabida sosai jikin Jannart yayi sauƙin.

Ya ƙara da cewa.
“Idan an barku kun ƙara kwana tofa sai ranar Monday za'a sallameku. Toh kuma tunda jikin da sauƙi gwara kuje gida zaifi”.
Dr Sulaiman yayi mgnar bisa bin umarnin da Dr Rayyern ya kidanya mishi a waya.

Cikin jin daɗin samun lafiyar nata Barrister Kabir yace.
“Toh Alhamdulillah Dr Sulaiman mun gode matuƙa Allah ya bar zumunci”.
Amin Amin yace tare da juyawa ya fita.

Su kuwa biyar dai-dai Barrister Kabir ɗin ya ɗauki Jannart da Mom ya nufi gida dasu.
Suna kan hanya ne Daddy ya kirasu yazo bai samezu ba.
Nan yake ce mishi ai an sallamesu gasu a hanyar gida.

Nan dai suka koma gida Barrister Kabir ya bawa Mom magungunan tare da cewa ta kula da Jannart da shan mgnin.
Ba tare da yayiwa yayan nasa mgnar Junaid ba ya sallamesu ya tafi.


Toh a hankali dai abubuwa ke juyawa suna wakana.
Yau Monday kwana biyu kenan da sallamo Jannart Alhamdulillah kuma jiki yayi sauƙi sosai.
Junaid kuma har yau bai zo gidaba.

Barrister Kabir kuwa duk cikin kwanakin nan bashi da zama yana yawan zirga-zirgan da Aunty Dijat ta gaza gane na menene.



Yau Monday misalin biyar na yamma.
Dr Rayyern Mai-nasara ne dake zaune a yar barandarsa balcony dake sama can jikin Bedroom ɗin sa.
Sanye yake da wasu tattausan riga da wondon iya guiwa rigar kuma irin mara hannun nance.

System ɗinshi ne bisa stoll ɗin dake gabansa sai plate da chocolate sai Bootle water a gefenshi.
Sosai ya dugufa kan aikin da yakeyi.

A hankali ya ɗago kansa cikin tarin gajiya ya juyo ya kalli farfajiyar gidan nasu can bakin gate.
Wani irin juyowa yaye tare da tashi tsaye da masifar fargaba ya zubawa fuskar Barr....!




*TUBALI na kuɗine ki biya kafin ki karanta cikin salama Da Allah.*



*Albishirinku! Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA*

NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA.
Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.

Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke taimakawa (sex hormones 😍) dinki.
Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!?
Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu.
Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki?
Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu,
Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ki zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan.
Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya.


Akwai daya bangaren wato *KAMSHI*
Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, sayan na gari maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia.

Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.

🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA
*(GARKUWAR MA'AURATA)*



By
*GARKUWAR FULANI*
11/15/21, 7:21 PM - Auntyna: Da sauri ya miƙe.
Idanunsa ya d’an zazzaro tare da sanya hannu ya dafe forehead d’insa, bakomai ne ya sashi yin hakan ba kuma, face ganin Barrister Kabir da ya shigo cikin gidan.

“Wannan mutumin Again? to me yazoyi? Kardai akan wancan magananne mai kama da tatsuniya ya biyoni har gida? gaskiya Indai hakane bazan iyaba, gwara ma tunda wuri naje na dakatar dashi.”

Ya fad’i maganar cikin sauri, batare kuma daya tsaya wani jinkiri ba kaitsaye ya juya, ya nufi asalin cikin sashinsa, Domin dole saiya sauko kasa, kafun zai iya dakatar da Barrister Kabir din.

Barrister Kabir kuwa Koda ya gama dai-dai-ta parking din motar, budewa yayi ya fito.

Ahankali ya juyo tare da nufo inda Baba Maud’o ke tsaye, idanu Baba Maud’o ya zubawa, fuskar mutumin da yaga yana tunkarosa, babu ko kyaftawa, Yayinda ajikinsa yakejin wani irin yanayi na girgizar kwanya.

“Assalamu Alaikum Barka da aiki.”
Barrister Kabir ya fad’a yana me mik’awa Baba Maud’o hannu, alaman suyi musabaha.

Hakan kuwa shi ya katsewa Baba Maud’o d’an guntun tunanin da yakeyi, hannu ya mik’awa Barrister Kabir din suka gaisa.
Saidai kuma duk yanda Baba Maud’on yaso dauke idanunsa daga Kallon, mutumin dake tsaye agaban nasa ya kasa.

Barrister Kabir kuwa Dan gyara tsayuwarsa yayi, kana cikin sakin fuska yace.

“Ni bak’one kuma nasan baka shaidani ba, amma Dan Allah ko zaka iya yimin sallama da maigidan?”

Still idanu Baba Maud’o ya zuba masa, saidai kuma jin yace Yayi masa sallama da mai gidanne, yasa shi d’an sauk’e ajiyar zuciya.

Kai Baba Maud’on ya jinjina, cikin kuma gamsuwa da yaji acikin zuciyarsa yace.
“To Kajirani anan, ba matsala bari nayi masa magana.”

“To Masha Allah nagode sosai.”

Barrister Kabir ya fad’i hakan, yana murmushi.

Yayinda shi kuwa Baba Maud’o kaitsaye ya nufi cikin gidan.

Aikuwa yana fara tafiyanne hankalin Barrister Kabir gaba d’aya ya tattare ya tafi kanshi, inda ya zubawa bayansa idanu baya ko k’yaftawa.
Musamman tafiyan mutumin, yaso tuna masa da wasu abubuwa.

Saurin girgiza kansa yayi, tare kuma da ture duk wani tunani da yazo cikin k’wak’walwarsa, saboda yasan ma ba hakan bane, maybe yanayi ne kawai yazo d’aya.
Sannan babban abunda yake gabansa ayanzu ma yafi karfin wannan tunanin.

Shikuwa Baba Maud’o Koda ya k’arasa jikin k’ofar babban falon gidan, tsayawa yayi tare da soma dan k’wank’wasa kofar.

Abba kuwa dake zaune acikin falon, Jin ana buga kofarne yasashi, d’an d’ago da kansa, tare kuma da bada izinin shigowa.

Jin anbada izinin shiga ne kuma yasa Baba Maud’o d’an tura k’ofar, ahankali ya saka kansa acikin falon bakinsa d’auke da sallama.

Ganin Baba Maud’o ne kuma yasa Abba dake zaune saurin mik’ewa, lokaci daya kuma ya saki fuskarsa tare da cewa.

“A’a Baba Maud’o yau kaine da kanka, shigo daga ciki.”

Murmushi Baba Maud’o yayi, tare kuma da d’an girgiza kansa, kana murya asake yace.
“A'a ai bama sai na shigo ba, yanzuma daliline ya kawoni, wani mutumi ne yazo yananan awaje, ya kuma ce Kai yakeson gani.”

Kai Abban ya d’an jinjina, tare kuma da danyin shiru na.
Dan wasu sakanni, saboda duk a iya saninsa baiyi da wani akan cewar za’azo nemansa ba.

Watsar da tunanin dake zuciyar tasa yayi, cikin kuma sakin fuska yace.
“To Baba Maud’o ace masa ganinan zuwa.”

Abban ya fad’a yana me gyara zaman babbar rigar dake jikinsa.

Kai Baba Maud’o ya jinjina, batare da yace komai ba kuma, ya juya ya fice daga cikin falon.

Dai-dai lokacinne kuma Rayyern ya gama sauk’owa cikin falon.

Ganin da yayi kuma Abban nasa na shirin fita ne yasashi, dan Sosa k’eyansa, cikin yanayin inda-inda yace.

“Abba fita zakayi ne?”

Juyowa Abba yayi ya d’an kalleshi tare da cewa.
“Eh yanzun nan Baba Maud’o yake cemin wai wani mutumi awaje yana son ganina.”

Kansa yad’an shafa still, kana cikin yin k’asa da murya yace.
“No Abba basai kajeba ai, ba bak’on ka bane bak’onane, kuma nasan ni yake nema.”

Idanu Abban yad’an tsura masa, cikin rashin gamsuwa da hakan yace.

“To kuma Idan ba bakona bane yace kuma yana nema na? Bari dai naje naji ko menene.”

Saurin d’ago da kansa yayi ya kalli Abban nasa, lokaci daya kuma ya marairaice fuskarsa tamkar karamin yaro.
“Abba dan Allah ka zauna, Zanje naji ko menene.”
Ya fad’a yana me kokarin fita wajen.

Kallonsa Abba yayi kana cikin rashin bai yarda da hakan ba yace.

“Anya kuwa Rayyern To waye ne, lafiya dai kam ko?”

“Eh Abba Lafiya kalau, bari naje na sameshi.”
Rayyern din ya fad’a cikin d’an sauri, tare da gudun kada Abban nasa yace Lallai shi da kansa zaije.

“Da kata Rayyern, koma dai wajen waye yazo, ai dai yanzu kam ni ya buk’aci gani ko, To barni naje na sameshi.”

Abban ya fad’a cikin serious, wanda hakanne kuma yasa duk jikin Rayyern din yin lak’was, kansa yad’an langwabar gefe, cikin kuma yanayin sanyi yace.
“Shikenan To Abba Dan Allah muje tare.”
Kai Abban ya jinjina masa alaman to.

Inda Abban yayi gaba shi kuma Rayyern ya biyoshi abaya, Yayinda acikin zuciyarsa yakejin babu dadi, saboda baisan da wacce maganan Barrister Kabir din ya kuma zuwa yau ba.
Saidai koma meye yana fatan ace sab’anin waccan magananne da sukayi last Friday acikin mota.

Koda suka fito compound din gidan, Barrister Kabir dake tsaye ajikin motarsa, yana hangosu ya fadada murmushi da kuma fara’ar dake kwance akan fuskarsa.

Bayan sun k’arasone kuma Abba’n ya mik’a masa hannu sukayi musabaha, kana Rayyern ma ya bashi hannu suka gaisa.

D’an Kallon Barrister Kabir din Abba yayi, cikin yanayin sakin fuska yace.

“Sannu bawan Allah saidai kuma gaskiya ban shaida fuskar taka ba.”

Murmushi Barrister Kabir din yayi, tare da gyara tsayuwarsa, still kuma fara’a fad’ad’e akan fuskarsa yace.

“Eh gaskiya bazaka shaidani ba, Domin wannan zuwan nawa, shine zuwana na farko cikin gidanka, sunana *Barrister Kabir Saleh Dakata!!”*

Dammmmm dammmmm haka zuciyar Baba Maud’o tayi wani irin bugawa, a lokacin da yaji sunan mutumin dake tsaye agaban nasa.
A hankali ya lumshe idanunsa sabida jin zuciyarsa na wani irin harbawa da karfi, tamkar zata faso kirjinsa ta fito.

Abba kuma kai ya jinjina nawa Barrister Kabir alamun gamsuwa.

Rayyern dake tsaye agefensu kuwa, Dan lumshe idanunsa yayi, cikin kuma yanayin kosawa yace.

“To Barrister mungode k’warai da ziyara.”
Ya k’arasa maganar tasa atak’aice Domin Sam bayason daga haka mutumin ya sake fad’an wani abu kuma.

Barrister Kabir kuwa fahimtar hakanne yasa shi, sakin murmushi, batare kuma daya lura da shock din da suke ciki ba yace.

“Alhaji wajenka nazo Idan babu damuwa kozan iya samun lokacinka muyi magana.”

Saurin girgiza Kai Rayyern yayi, lokaci daya kuma gaba daya mood d’insa ya sanja.
Kallon Barrister Kabir din yayi, kana cikin dagiya yace.

“Mun gama magana dakai tun a wancan ranan.
To yanzu kuma ai inaganin babu buk’atar kace lallai saika yi magana da Abbana, Dan Allah kaje kawai.”

Dr. Rayyern din ya k’arasa maganan, cikin son kin bawa Barrister Kabir din dama.

Shikuwa Barrister Kabir murmushi yayi, batare kuma daya ce komai ba, ya sake gyara tsayuwarsa.

Abba kuwa wani irin boyayyar ajiyar zuciya ya sauk’e, tare da d’an juyawa ya kalli Rayyern dake bayansa, wanda yayi kicin kicin da fuska.
Tabbas zuciyar Abban ta raya masa wani abu.
Hakanne kuma yasa shi dawo da kallonsa ga Barrister Kabir d’in.

“Shikenan badamuwa Barrister Kabir Saleh Dakata mushiga daga ciki.”
Abban ya fad’a yana me juyawa, kaitsaye, Barrister Kabir kuma ya rufa masa baya.

Rayyern kuwa idanunsa ya rumtse, cikin haushi da takaici ya d’an ciji Labb’an bakinsa, sam kwata kwata ba haka yaso ba, yaso ace Barristern bai samu attention din Abban nasu ba.

Juyawa yayi shima asukwane yabi bayansu.

Yayinda Baba Maud’o dake zaune akan d’an bencinsa kuwa duk yabisu da idanu.

Acan cikin falon kuwa, suna shiga Abba ya nunawa Barrister Kabir din wajen zama.
Bayan duk sun zaunane kuma, Abban ya kalli Rayyern, da yake shigowa yanzu.
Kuma shidinma waje ya samu acikin falon ya zauna, saboda ya fiso duk wani abu da Barrister din zai fada ya jita acikin kunnensa.

Abba da Barrister Kabir din kuwa sake gaisawa sukayi, kafun duk sukayi shiru na d’an wasu sakanni.
Still Abban ne kuma da har yanzu zuciyarsa bata daina bugawa da karfi ba, ya kalli Barrister Kabir din, tare da cewa.
“Barrister inajinka meke tafe dakai?”

K’akk’afar ajiyar zuciya Barrister Kabir ya sauk’e, lokaci daya kuma duk wani mood d’insa ya sanja, tsananin rauni da kuma karyewar zuciya ne suka bayyana akan fuskarsa, Yayinda zallan damuwa ta fito tayiwa fuskarsa kawanya.
Gyara zamansa yayi ahankali, cikin kuma sanyin murya dake bayyana tarin fargaba hadi da damuwarsa yace.

“Tabbas ni mabuk’aci ne awajenku, sannan kuma banzo


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login