Showing 105001 words to 108000 words out of 350584 words

Chapter 36 - Tubali Book 1 Hausa Novel Complete

watarana Jannart sai ta zamo wani sashi na jikinsa.”

Murmushi Aunty Dijat tayi, saboda ta fahimci kalaman da mijinnata ke nufi.

Acan gidan su Rayyern kuwa, Koda Abba ya dawo cikin falon, anan ya sameta zaune ita da Jannart din, da har yanzu ta kasa daina zubda hawaye.

Zama Abban yayi
Tare da tausasa muryarsa cikin aminci yace.

“Jannart”.
Wani irin sanyi taji muryar Abba ya sakar mata.
Shi kuwa a mutunce yace.
“Jannart d’ago kanki ki kalleni.”

Jannart dake sakin shesshekan kuka, sake Jin Muryar Babban mutum acikin kunnuwanta ne yasa ta d’ago kanta Ahankali, da kuma Idanunta wanda sukayi luhu-luhu ta kalleshi.

Kai Abban ya girgiza, kana cikin lallashi da ban baki yace.

“Kada kiyi mini wani kallo na daban Jannart, inaso ki kalleni amatsayin mahaifinki, ni Babanki ne, kada ki ajiyeni amatsayin suruki kawai, saboda na daukeki ne amatsayin y’a, wanda har abada kuma bazan tab’a bari kunci yayi tasiri acikin zuciyarki ba, wannan gidan kada ki daukeshi amatsayin gidan aurenki kawai, ki daukeshi amatsayin gidanku, kafun yanzu bamu sanki ba, amma ayanzu kedin tamuce, kin zama daya daga cikin iyalinmu, munzama iyayenki ke kuma kinzama y’armu, Ramadan ya zama shak’ik’in d’an uwa agareki, dama kuma duk wani wanda yake tare damu, duk wani damuwa da ya dameki kuwa ki sanar mana.
Insha Allah zamu magance miki ita, saboda haka ki daina kuka kinji, kisa aranki cewa muna tare dake, kuma Allah Ma yana tare dake.”

Kanta ta d’an jinjina, saboda yanda kalaman Abban sukayi tasiri a zuciyarta, duk da cewar ta kasa tsaida hawayen dake zuba acikin Idanunta.

Cikin sanyi hadi da muryarta wacce bata fita sosai tace.

“Nagode Abba, nagode da karamcin da kukayi min Allah ya kara girma.”

Murmushi Abban yayi, kana cikin jin dadin biyayyar yarinyar yace.

“Ba komai Jannart, Insha Allah zamu zame miki iyaye na gari, Mamyn Rayyern Ina Rayyern din kuma ya tafi.”
Ya ƙare mgnar yana kallon Mamy.

“Rayyern ya haura sama.” Mamy ta fad’a tana murmushi.

Kai Abban ya jinjina, kana cikin kulawa yace.

“To dare na tayi, ki Kai Jannart masaukinta ta kwanta.”
Ya ƙare mgnar yana nuna mata side din da zata kai Jannart ɗin.
To Mamyn tace, tare kuma da kama Hannun Jannart din suka nufi, wata had’add’Iyar k’ofa dake nan cikin falon, kusa da side din kitchine da kuma dining area.

Ahankali Mamy ta tura k’ofar d’akin.

“Ki shigo da bismillah.”
Mamyn ta fad’awa Jannart Cikin kulawa, hakan kuwa akayi da bismillah Jannart ta jefa k’afarta ta dama acikin falon.

Falo ne mai kyaun gaske wanda aka k’awata cikinsa, da wasu had’add’un royal cushions masu kyau, sai kuma labulayen da aka k’awata jikin window dana bedroom door dashi, atsakiyar falon kuwa, wani lallausan carpet ne maikyau da girma, sai kuma babban tv’ plasma’n da aka daurasa akan wani babban tv stand.

Sosai falon yayi kyau, duk da cewar babu wasu tarkace masu yawa acikinsa, amma komai da komai mai tsada ne.

Sanyin AC da kuma daddad’an kamshin room freshener dake tashi acikin falonne yasa Jannart lumshe Idanunta.

Inda Mamy kuwa kaitsaye ta wuce jin wata kofa dake cikin falon, still kuma tana rik’e da hannun Jannart ta bud’e kofar suka kutsa ciki.

Bedroom ne madaidaici wanda aka zuba masa furnitures na alfarma, bed, drawer, and dressing mirror with bedside drawer then shoe rug.

Komai dake cikin d’akin kalan pink and white ne, shiyasa haduwarsa yake dajan hankali, kamar dai falon, Domin shima cushions da labulayen cikinsa duk pink and white ne.

K’arasa shigowa cikin dakin sukayi, Yayinda Mamyn ta zaunar da ita bakin gadon daya sha bedsheet na alfarma.

Kallonta Mamyn tayi, kana cikin tausasawa tace.

“Jannart Nan shine masaukinki, zaki zauna ne kuma kafun agama gyara miki asalin inda zaki zauna.
Dan Allah Jannart ki saki jikinki, babu wani wanda zai takura miki, akwai komai na amfani da zaki buk’ata, duk abunda kikeso kuma kiyi min magana, banason kiyi kuka kinji ko Jannart”.
Cikin sharce hawayen ta gyaɗa kai alamun.
Eh taji.
Cikin jin daɗi Mamy tace.
“Kinga ke amanace agaremu, zubar hawayenki kuma zai zamo damuwa azuciyoyin mu, duk wani abunda ya dameki ki sanar dani, kada kiji shakka ko kuma nauyi na.
Domin bana daukanki amatsayin suruka, sannan kada ki bari damuwa tayi nasarar tank’wasar da zuciyarki, kowani bawa yana d’auke da irin salon k’addararsa, saboda haka ki kwantar da hankalinki, ke taki k’addarar ahaka tazo, Insha Allah kuma watarana komai zai wuce, babu wani damuwa dake tabbata, kiyi farinciki aduk wani yanayin da kika samu kanki kinji Jannart.”

Kai Jannart din ta jinjina, tare kuma da kama y’an yatsun hannunta cikin sanyi tace.
“Insha Allahu Mamy zanyi duk abinda kikace.”

Murmushi Mamyn tayi, cikin tsananin jin dadi da farinciki tace.

“Yauwa Jannart, Allah Yayi miki albarka, naji dadin biyayyarki.
Domin duk wani wanda yake daukar maganan na sama dashi, har abada bazai tab’ayin dana sani ba.”

Ta ƙare mgnar tana nufar Bathroom.

Ruwan wanka mai dumi Mamyn ta had’awa Jannart acikin bath, tare kuma dasa mata turaren wanka mai dadin k’amshi.

Koda ta fito daga toilet din, hannun Jannart din ta kamo ta miƙar da ita, tare da cewa.

“Yauwa Jannart kije kiyi wanka ko nasan..”

Sauran maganan Mamyn ne ya mak’ale, saboda yanda taji duk jikin Jannart din ya dau zafi.

“Subahanallah Jannart gashi duk jikinki zafi, nasan kuma hakan bai rasa na saba, da kukan da kikayi, kije kiyi wanka, akwai sabin towels acikin toilet din saikiyi amfani dasu, akwai kuma ruwan dumi dana had’a miki a bathtub.”

“Nagode Mamy.”
Jannart din ta fad’a, Ahankali tare kuma da zare dogon hijab din dake jikinta.

Mamy kuwa murmushi tayi, kana ta juya ta fice daga cikin d’akin.

Koda ta fito nan cikin falon nasu, kaitsaye kitchine ta wuce.

Yar ƙaramar tukunya tasa akan gas, cikin abunda baiwuce.
15mn ba kuwa ta kammala had’a indomie’n da ta dafawa Jannart din, wanda yaji kayan hadi da kifi, bayan ta juye indomie’n a plate ne kuma, ta had’a tea mai kauri acikin mug.

Bayan ta gama kimtsa komai ne kuma, kaitsaye ta haura sama zuwa dakin Rayyern.

Zaune yake akan gadonsa, inda ya sanja shigar jikinsa, zuwa kayan bacci masu taushi.

Yanayin yanda yayi zaman duka k’afafunsa na k’asa, sannan kuma ya dafe kansa da hannayensa duka biyu.

Idanunsa arumtse suke, kana kuma time to time yake fesar da wani irin numfashi mai kama da ajiyan zuciya.

Mamy kuwa isowarta jikin kofar ne yasa ta d’an soma knocking.
Sai-dai har tsawon mintuna 2 tana knocking amma bataji a bud’e k’ofar ko kuma bata izinin shigowa ba.

Hakan kuwa shi yasa ta murd’a handle din kofar a zayonta ko yana bacci ne, ga mamakinta kuwa sai taga kofar ta bud’u.

Ahankali ta tura kanta cikin dakin tare dayin sallama.

Anan zaune ta hangosa, ya dafe Kai, da dukkan alama kuma yayi nisa acikin duniyar tunanin da yakeyi.

Idanu Mamyn ta Dan tsura masa cike da mamaki, saboda wannan ne karo na farko da taga Rayyern din acikin yanayin zallar damuwa.

Rayyen kuwa da yayi nisa acikin duniyar tunaninsa, Sam baisan cewa Mamyn ta shigo ba.

Gaba daya hankalinsa ya tafi, izuwa sabuwar k’addarar daya samu kansa aciki.
Yayinda har yanzu ya kasa tantance wani irin aure ne aka daura masa, Sam ya kasa tantance marabar auren dana dole, shi ya sani bayason lamarin mace acikin rayuwarsa, but why za’a takura masa? Yasan meye aure yasan manufarsa yasan hakkokin mata a kan mijinta.
Yasan bashi da lokacin saukesu da reno da tattalin mace yadda ya kamata shiyasa bai kawo mace a rayuwarsa meyasa zasu liƙa mishi ita a dole su lika mata shi a dole.

“Rayyern! Rayyern!!”



https://chat.whatsapp.com/IM6PrgYNy9s6lP0aXmBkaN


Samun zafafan saukakan kayayyakin zamani na mata tun daga kan leshi, shadda, atamfa, material, jaka da takalmi, hijab..... da dai sauransu akan farashi mai sauki da rahusa sai a kamfanin Garkuwa collection. Bama wannan kadai ba akwai kayan order da muke yi shi ma duk a cikin rahusan da saukin kudi. Ba mu tsaya nan ba ina kuke yan kasar *NIGER* albishirinku kuma kuna iya siyan kayanmu ya isa gareku cikin aminci ba tare da bata lokaci ba. maza yan’uwa ku garzayo ku gane wa kanku wannan rahusar da kuke jin labari. Kayanmu ko a kasuwa ba zaka samu farashinsu ba. gidanmu gidan duniyar leshi, atamfa shadda, material da sauransu. Sai kun zo. Muna maraba da kai a kowanne gari kake.
GARKUWA COLLECTION! Siyan nagari mayar da kudi gida!

By
*GARKUWAR FULANI*
11/15/21, 7:21 PM - Auntyna: https://chat.whatsapp.com/IM6PrgYNy9s6lP0aXmBkaN


Samun zafafan saukakan kayayyakin zamani na mata tun daga kan leshi, shadda, atamfa, material, jaka da takalmi, hijab..... da dai sauransu akan farashi mai sauki da rahusa sai a kamfanin Garkuwa collection. Bama wannan kadai ba akwai kayan order da muke yi shi ma duk a cikin rahusan da saukin kudi. Ba mu tsaya nan ba ina kuke yan kasar *NIGER* albishirinku kuma kuna iya siyan kayanmu ya isa gareku cikin aminci ba tare da bata lokaci ba. maza yan’uwa ku garzayo ku gane wa kanku wannan rahusar da kuke jin labari. Kayanmu ko a kasuwa ba zaka samu farashinsu ba. gidanmu gidan duniyar leshi, atamfa shadda, material da sauransu. Sai kun zo. Muna maraba da kai a kowanne gari kake.
GARKUWA COLLECTION! Siyan nagari mayar da kudi gida!




Mamy ta kira sunansa da d’an k’arfi, wanda hakan yasa shi dawowa daga duniyar tunanin daya fad’a.

D’ago da kansa yayi Ahankali ya kalli Mamy’n, da ta tsare shi da ido.

“Mamy yaushe kika shigo?”
Ya tambaya da dan mamaki akan fuskarsa.

“Tayaya zaka san lokacin dana shigo, bayan kanason takurawa rayuwarka, dason sawa kanka damuwa akan abunda kasan ya zama wajibi akanka.”

Mamyn ta fad’a.

Longoɓar da kansa yayi, kamar zaice wani abu kuma saiyayi shiru.

Mamy kuwa Ajiyar zuciya ta sauk’e, had’e da cewa.

“Idan akwai magananin zazzab’i awajenka, ko paracetamol ne ka bani, Jannart ce jikinta duk ya d’au zafi.”

Jin abunda Mamyn ta fad’a ne kuma yasashi d’ago kansa ahankali ya kalleta, fuska ya kwab’e kana cikin muryarsa mai kama da shagwab’a yace.

“Ni kam Mamy bani da wani magannin zazzab’i.”

Harara Mamyn ta watsa mishi tare da gyara tsayuwarta tace.
“Taya zaka cemin babu bayan bakaje ka duba ba.”

Sake langwabar da kansa yayi, still yace.

“Mamy nasan fa babunne, kuma yanzu ni bana ajiye magani, saidai ko ki tambayi Ramadan.”

“Katashi Kai kaje ka karb’omin maganin awajen Ramadan.”
Mamyn ta fad’a adake.

Jin hakanne kuma yasa shi mik’ewa jiki asanyaye, ya nufi dakin su Ramadan.

Yana zuwa kuwa ya samu Ramadan da Riyyam-nsra kowannensu na rike da waya ahannu.

Ko Kallon kirki baiyi musu ba, ya tsaya tare da d’age kansa sama, kana yace.

“Ramadan bani paracetamol.”

Da mamaki Ramadan yake kallonsa, kamar zaiyi magana kuma saiya fasa, kaitsaye ya bud’e wani Dan box maganin zazzab’i ya ciro ya mik’awa Rayyern din.

Yana karb’a kuwa ya fice, inda ya samu Mamy abakin k’ofa ya mik’a mata.

Amsan maganin Mamy tayi, batare da tace masa komai ba kuma ta juya ta sauk’a k’asa.

Shikuwa d’akinsa ya koma, zuciyarsa cike da takaici.
Domin shi sai yanzu ne ma yakejin haushin yarinyar da aketa kira da Jannart din.

Mamy kuwa kaitsaye kitchine ta nufa, bayan ta d’auki abincinne kuma ta wuce sashin Jannart.

Jannart kuwa dai-dai lokacin ta fito daga wanka, bayan tayi wankanne kuma ta sake maida doguwar rigar da ta cire.

Tana tsaka da maida hijab dinta ne kuma, Mamy ta shigo hannunta dauke da cup da kuma plate din indomei.

Akan wani Dan stull Mamy ta ajiye cup da plate din, tare da duban Jannart din Cikin kulawa tace.

“Yauwa Jannart kinfito ko, ga abinci nan kici, sai kisha magani saboda naji jikinki akwai zafin zazzab’i.”

Kai Jannart din ta Dan sunkuyar kasa, kana aladabce tace.

“Mamy nakoshi.”

“A’a kam Jannart, saboda kefa na shiga kitchine na dafa abincin nan, saboda haka ki zauna kici, kada kiyimin gardama kinji, koso kikeyi na barki haka, Allah ya kama mu kefa amanace awajen mu, zo maza ki zauna kici.”

Mamyn ta fad’i haka cikin matukar kulawa.

Wanda hakanne kuma yasa Jannart din karasowa, ta zauna akan lallausan sofan dake malale agaban gadon.

Abincin Mamy ta ajiye mata, Ahankali kuma ta soma tsakuran abincin tana kaiwa bakinta.

Kasancewar kuma da gaske bata wani jin yunwa sosai ne, yasa bata wani ci abincin sosai ba, saidai tea din da Tasha har fiye da rabin kofin.

Dan matsar da plate din abincin tayi gefe, tare da yiwa Mamy alama akan ta koshi.

Hakanne ko yasa Mamy b’are maganin ta bata tasha.

“Ki kwanta to ki huta, Dan Allah karki sakeyin kuka kinji Jannart, kinga shine ya haddasa miki wannan zazzab’in.”
Mamy ta fadi haka tana me daukan plate da cup din abincin.

“To Mamy.” Jannart din ta fad’a, tana me mikewa tsaye ta haura saman gadon ta kwanta.

Murmushi Mamy tayi saboda a iya yaudin kawai ta yada da hankali,da kuma biyayyar da yarinyar take dashi.
Cikin kula tace.
“A'a Jannart tashi kiyi addu’a kinji, kada bacci ya daukeki batare da kinyi addu’a ba.”

Aikuwa da d’an hanzari Jannart din ta tashi zaune, hannayenta ta hade waje guda, falaq,suratul nass, da kuma suratul Iqlas, k’afa uku uku, kursiyu da amarasulu sai kuma Hasbiyallahu la’ilaha illahuwa, alaihi tawakkaltu wa huwa rabbul arshil azim, k’afa 7, sai kuma suratul Khafirun kafa uku shima.

Bayan ta shafa ne kuma ta koma ta kwanta.

Mamy kuwa cike da farincikin samun ya kuma surkuwa ta gari, ta ragewa Jannart gaba daya hasken wutan dake dakin.
Bayan sunyiwa juna saida safe ne kuma Mamyn ta juya ta fita.

Bayan ta maida plate and cup din kitchine ne kuma, kaitsaye Mamyn dakin Abba ta nufa.

Koda taje Zaune ta sameshi akan gado.

Zama ita dinma tayi agefensa, kana cikin tausasa murya tace.

“Tabbas Rayyern ya samu mata, yayi dace da yarinyar arziki mai ladabi da biyayya”.
Cikin jin daɗi Abba ya juyi ya fuskanceta yana mai jinjina kai alamun gamsuwa.
Ita kuwa Mamy cikin girmamawa tace.
“Toh amma Alhaji meyasa ka umarceni dana kaita wancan dakin, bayan ganan sashin Rayyern.”

Murmushi Abba yayi, tare da maida kallonsa gareta yace.

“Nace ki kaita wancan part dinne Saboda, sai anyi gyara a b’angaren Rayyern kafun ta koma can.
Kadafa ki manta fa amaryace, Koda cewar auren ba dan shiri bane, amma yana da kyau a inganta mata komai nata”.
Da sauri tace.
“Eh gsky hakane kam”.
Ɗan gyara zamanshi yayi tare da cewa.
“Sannan kuma baki ga dan naki bahagon yaro bane, kwata-kwata na kasa gane inda ya dosa, Sam bai fahimci abunda muke nuna masa ba, atakaicema gani yake kamar takurasa mukeson yi.
Bayan haka kuma ganan Ramadan shima yana saman.
To dole yanzu zai dawo k’asa, kafun adai-dai-ta komai ta koma side din nasu.”
Kai Mamy ta jinjina cike da gamsuwa.
Kasancewar ta gaji ne kuma yasa ta zame ta kwanta gefensa.

Acan b’angaren Rayyern kuwa, akwance kawai yake amma duk zuciyarsa babu dadi.
Ak’alla saida ya kwashe sama da 50mn kafun bacci b’arawo ya iya satan shi.

Jannart kuwa tun fitan Mamy ta lumshe idanunta.
Yayinda tunani kala-kala ke yawo aciki kwakwalwarta, akaro na farko kenan tun tashinta izuwa yanzu, da zata kwana awani gida sab’anin nasu dan ko gidan Barrister Kabir Daddy bai taɓa barin ta ta kwana ba sai kuma asibiti.

Tunani ne fal zuciyarta, saidai kuma kamar yanda tayiwa Mamy al'ƙawari, batayi kuka ba, da taimakon maganin zazzabin da tasha ne kuma bacci ya dauketa.

Yayinda acan gidan Alhaji Idi Sale Dakata kuwa, kowa ya kwana sharbar bacci batare da tunanin Jannart bata cikin gidan ba, Domin wasu daga cikin mutanen gidan har da gwartin su, saidai banda Junaid Wanda ya taso sad’ab sad’ab ya nufi d’akin Jannart din, saboda gaba daya ya kasa bacci.
Daya rufe idanunsa Surar Jannart dinne keyi masa gizo, shiyasa yazo domin rage zafin abunda ke damunsa.

Koda ya karasa kofar dakin nata, kaitsaye ya tura kansa ciki.

Saidai kuma rashin ganinta da baiyi acikin dakinba, yasa shi cije labbansa, lokaci daya kuma ya raya cewar ko tana toilet Murmushin mugunta yayi, tare da nufan toilet din kaitsaye.

Tura kofar yayi batare daya jira komai ba kuma ya soma zare belt din wandonsa, saboda ya gama targetting yana ganinta zai Afka mata, amma kuma saidai meye?

Wayam haka yaga toilet din, ba alaman ma anshigesa tsawon sama da 1hour.

Tsuka yaja tare da fitowa, yana kwafa haka ya fice daga cikin dakin, cike da takaicin rasa damar da yayi.

Badan ransa yaso ba haka ya koma sashinsa ya kwanta a tunaninsa ko tana dakin Mom.

*Washegari*

8:00 am dai-dai Mom ta gama kammala musu breakfast, wanda kuma har zuwa tsawon wannan lokacin ba taga Jannart ta fito ba.

Hakanne kuwa yasa bayan ta gama setting dining table, kaitsaye tatafi izuwa dakin Jannart din.

Koda ta isa bakin kofar knocking ta fara yi, har na tsawon mintuna 2 kuwa bataji ko motsin za’a bud’e kofar ba, hakan yasa Ahankali ta tura kofar d’akin, tare da kutsa kanta ciki.

“Jannart! Jannart!!” Momyn ta kira sunan Jannart din, saboda rashin ganinta da tayi adakin.

Jin shiru ne kuma yasa Momyn juyawa ta fita, saboda atunaninta ko Jannart din tana cikin toilet ne.

Kaitsaye dining table ta dawo, tana zuwa kuwa, Daddy da Abdull suma suka fito suka zauna.

Momyn ce tayi saving dinsu, tana cikin saving dinnasu ne kuma, Junaid ya shigo cikin falon, yana fito, daga shi kuma sai t shirt da gajeren Wando.

K’arasowa dining table din yayi, batare daya gaisar da kowanne daga cikinsu ba, cikin iskancinsa irin na wasu masifaffun sojoji yace.

“Ina Jannart?”

D’agowa duk sukayi suka kalleshi.

Sanin halin rashin mutumcinsa ne kuma yasa Mom tace.

“Yanzu na dawo daga dakinta banganta ba, tun safe kuma bata sauko ba, amma Ina tunanin ko tana toilet ne.”

“Bawani bata gidan nanne ma gaba d’aya, y’ar iskar yarinya, jiya ma da dare ai naje dakinta amma bansa meta ba, wallahi Idan na kamata sainaci Uwarta.”

Baki Momy ta tab’e, tare da kallonsa cikin yanayin mamaki tace.

“To kai meya kaika dakinta da dare?.”

“Oho bansani ba, munafurci kawai.”

Junaid din ya fad’a kaitsaye, babu wani shakka ko shayi.

Duk da Abba yana jinsa kuwa, haka yayi shiru bai tanka masa ba, saima Kallon Momyn da yayi, yace.

“Kije ki duba toilet din,


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login