Showing 159001 words to 162000 words out of 350584 words

Chapter 54 - Tubali Book 1 Hausa Novel Complete

tace.

“Masha Allah Jannart har kin kammala, Allah Dai yayi miki albarka, ki kai masa nasan yana nan yana jira.”

Murmushi Jannart din tayi, tare kuma da dan sunkuyar da kanta, cikin nutsuwa ta nufi saman.

Tafiya take Ahankali, Yayinda tayi kyau cikin riga da wandon pallazon dake jikinta, wanda ta yafa mayafi. Dan babba akan shigar nata, saidai duk da hakan ga wanda yayi mata Kallon k’urulla, tsab zai iya hango tsararren cikakken hips dinta.

Ga kuma rigar shirt din da yayi mata cibcib ajikinta, cikin tan nan alafe yake, tamkar babu hanji acikinsa.

Karasowa bakin kofar falon nasa da tayi ne kuma yasa ta, tura kofar ahankali, bakinta dauke da sallama ta kutsa kanta ciki.

Babu kowa acikin falon hakane yasa ta nufi, Bedroom nashi,
a hankali ta tura ƙofar tare da sallama a bakinta.
Still nan ɗin ma babu shi,
Cikin mamaki ta ɗan ware idanunta tare da jujjuya kanta, tana mai kasa kunne wai ko zata jiyo mostinsa a Bathroom,
jin shirune ba motsin komai, harta nufi kofar dakin dan fitowa falon nasa ne kuma, saita hangosa zaune acikin wani balcony wanda labulayensa keta kaduwa saboda iska.

Kaitsaye wajen ta nufa tana isa wajen kuwa, idanunta suka sauka akansa.
Da sauri tayi kasa da kanta, saboda ganinsa ahaka da tayi, domin yau dinma ba wani kayan kirki bane ajikinsa, singlet ne da kuma gajeren wando.

Shikuwa Rayyern jin sallamanta ne yasashi dago kansa, ya sauke idanunsa akanta.

Tashin farko kuwa idanunsa suka sauka, akan lafaffen cikinta, wanda ta daure kasansa da adon igiyan wandon dake jikinta.

Janye idanunsa yayi daga Kallon nata, tare da maida kallonsa gefe.

Anutse ta karasa isowa inda yake, tare da Dan dukawa ta ajiye tray din dake hannunta.

Cup ta d’auka tare da zuba masa kunun, kana ta saka masa madara da zuma aciki.

D’an d’agowa da kanta tayi, hade da mik’a masa cup din.

Cikin sanyi tace.

“Gashi.”

Tayi maganan tana me sauke idanunta, akan lallausan beard d’insa. Wanda yake matukar yi mata kyau.

Ahankali ya juyo da kallonsa zuwa gareta, lokaci daya kuma ya sauke idanunsa akan kyakkyawar fuskarta, da kuma dan karamin lips dinta, dake shining din lipgloss.

Hannunsa yasa ya karb’i cup din, Ahankali kuma ya dan motsa lips d’insa, saidai kuma ita kanta bataji mai ya fad’a ba.

Kan Wani had’add’en rug dake gefensa ta zauna, tare kuma da rike flask din ahannunta.

Saurin kallonta yayi, saboda baiyi tunanin zama zatayi ba, kamar zaice wani abu kuma sai ya fasa,Ahankali kuma ya janye idanunsa da suka sauka akan waist dinta.

Cikin nutsuwa ya soma sipping kunun, yana me lumshe idanunsa saboda yanda yakejin dadin kunun.

Itakuwa Jannart gaba daya kallonta ta mayar k’asa, inda take hango Riyyam-nsra da Baba Maud’o wayanda suke zaune abakin gate.

Kallonsu takeyi sosai, musamman ayanzu da taga Riyyam din na waya, ba tare da taga ya jima yana wayan ba kuma ya mikawa Baba Maud’o.

Hannayenta duka biyu ta had’e tana kallonsu.

Yayinda acan kasan kuwa.

Mammy ce takira tana tambayan Riyyam din jikin Rayyern .

Nan Riyyam din yake shaida mata cewar jikin da sauki, Koda ta nemi ta gaisa da Rayyern dinne kuma, Riyyam yake sanar mata cewa, baya kusa da Hamma Rayyern din, ananne kuma Riyyam din yace.

“Mammy Ina tare da Baba Maud’o bari na bashi ku gaisa.”

“To.” Mammyn tace.

Yayinda Riyyam-nsra kuwa ya mikawa Baba Maud’o wayar.

Karb’an wayan Baba Maud’o yayi tare kuma da karata akan kunnensa, Cikin nutsuwa yace.

“Assalamu Alaikum.”


Acan Ethiopian kuwa Mammy dake zaune akan kujera, Jin amo da kuma sautin muryar daya daki dodon kunnenta ne, yasa taji zuciyarta tayi wani irin bugawa, take kuma tsikar jikinta suka shiga wani irin mimmikewa, cikin wani irin yanayi ta mik’e tsaye, tare da sake sauraran muryar dake kan wayar.


“Assalamu Alaikum.”

Baba Maud’o ya sake maimaita sallaman nasan, saboda Jin shiru da yayi.

Komawa Mamyn tayi ta zauna, tare kuma da sanya hannu ta dafe kirjinta, cikin rawar murya tace.

“Wa’alaikassama.”

Zumbur haka Baba Maud’o ya mik’e tsaye daga zaunen da yake, tare kuma da d’an zazzaro idanunsa waje, lokaci daya wani irin yanayi ya bayyana atattare da Baba Maud’on.

Wanda hakan yasa Riyyam dake zaune kallon Baba Maud’on, Cikin yanayin mamaki yace.

“Baba Maud’o lafiya?”

Kallonsa Baba Maud’on yayi, tare kuma da komawa Ahankali ya zauna, saidai kuma har yanzu jikinsa bai daina tsuma ba.

Daga can b’angaren kuwa cikin rawar murya Mammy tace.

“Ina wuni, ya maijiki?”


Hannu Baba Maud’on ya d’an dunkule cikin wani irin abu dake dukan zuciyarsa yace.

“Lafiya mai jiki kuma Alhamdulillah.”


“Masha Allah Allah ya kara sauki, mungode sosai Baba Maud’o nasan kuna nan kuna fama da rigiman Riyyam, Allah ya bada lada.”

Mammyn ta fad’a cikin sanyin murya.

Baba Maud’o kuwa murmushi ya aro ya sakawa muryarsa, kana shima cikin sanyi yace.

“Ameen summa Ameen, ai Riyyam kam babu wani rigiman da yake yi mana, harma mun saba dashi kwannan yana ta cewa kin matsa ya komo mu kuma bamu son rabuwa dashi.”

Murmushi Mammyn tayi, cikin kuma karfin hali da danne bugun zuciyar da takeji, tace.

“Shikenan to Baba Maud’o ahuta gajiya.”

“Yauwa.”
Baba Maud’on ya amsa, tare da zare wayar akan kunnensa, cikin sanyi da kuma wani irin tunani dake dukan, kwakwalwarsa ya mikawa Riyyam nsra wayan.

Karb’an wayan Riyyam-nsra yayi tare da Karawa akan kunnensa.

Jin muryar Riyyam dinne kuma yasa, Mammy sauke wani irin nannauyar Ajiyar zuciya.

Cikin sanyi tace.

“Riyyam ka had’ani video call da Rayyern, inason naga ya yanayin jikin nasa.”

“To Mammy zan hadaku amma maybe sai gobe, saboda nasan yanzu haka yana sama, kuma Idan magriba ta kusa bayason yawan magana.”
Riyyam din ya fada atausashe.

Daga can b’angaren kuwa Kai Mammy ta jinjina, tare da cewa.

“Shikenan to badamuwa Allah ya kaimu goben.”

“Ameen”
Riyyam din ya amsa kana sukayi sallama da Mamyn.

Duk abunnan da sukeyi kuwa Jannart na kallonsu, saboda gaba daya hankalinta ya tafi garesu ne ma, yasa har yanzun take nan bata tafi ba.

Shikuwa Rayyern tuni ya shanye kunun da ta zuba masa din tas.
Ganin bata da niyan kara masa ne kuma yasa shi, dagowa ya kalleta.

Akaron farko kenan daya tsaya ya k’are mata kallo, idanunsa ya dan tsayar akan fuskarta, saboda yanda yaga hankalinta ya tafi izuwa wani waje na daban.

Ajiye cup din dake hannun nasa yayi, Karan ajiye cup dinnasa ne kuma yasa hankalinta dawowa garesa.

Ahankali ta juyo da kanta zuwa garesa, karab kuwa idanunsu suka sarke acikin na juna.

Sunkuyar da kanta k’asa tayi, tare da sauke numfashi, cikin silent voice dinta tace.

“Nak’ara maka ne?”

Kansa ya d’an girgiza mata, tare da lumshe idanunsa, cikin wani irin yanayin daya saka zuciyarta harbawa yace.

“Um um nakoshi.” yayi mgnar yana jin dadi bakinsa yayi masa wasai yawunsa ya sinke alamar dandanon bakinsa zai dawo.

Kallonsa tayi, haka kuma shid’inma.

Kasa tayi da Idanunta tare da matsowa ta durk’usa, tray din ta ke kokarin dauka.

Dan kusancin da sukayi ne kuma yasa, daddad’an kamshin turarenta ratsa cikin hancinsa.

Idanunsa ya dan lumshe, Yayinda itakuwa tray din ta dauka Anutse ta juya ta tafi.


Kaitsaye kasa ta sauka, bayan takai kayan kitchine ne kuma ta wuce dakinta.

Shikuwa Rayyern kiran Sallan magriba ne ya tadashi awajen.

Washegari.

Yau dinma kunun da Jannart din tayi masa jiya ya kuma sha, sai kuma abu mai romo da Mamy tasa ta dafa masa, babu laifi kuma yaci sosai.


After 3days.

Mamy ce tsaye agefensa, Yayinda shikuwa ke zaune akan daya daga cikin kujerun falon.

Murmushi Mamyn tayi tare da dubansa cikin danjin dadi.

Tace.

“Masha Allah Babana Lallai jiki yayi sauki, tunda har ka iya fitowa falo.”

Murmushi ya d’anyi tare da Kallon Mamyn nasa, cikin sanyi yace.

“Mamy yunwa nakeji sosai, kuma nafison abu mai dan tsami, please Mamy roasted fish da ruwan lemon tsami nakeso, ko kuma miyan da akayi ranan nan pls Mamy.”

Murmushi Mamyn tayi tare da cewa.

“To Rayyern amma ni bansan yanda akeyin miyan ba, rannan ma bani nayi ba Jannart ce tayi, amma bari na turo maka ita saikayi mata bayani.”

Fuskarsa yadan kwabe cikin shagwaba yace.


“Eyyah Mamy kifada mata mana, dole sai ni?”

“Eh mana bakaine kakeso ba.”

Mamyn ta fad’a tana me nufar dakin Jannart.

Ramadan dake zaune agefe kuwa, Kallon Hamman nasa yayi, tare da mik’o masa magungunan daya b’are.

Cikin kulawa yace.

“Please Hamma Rayyern karb’a maganinka kasha.”

Fuskarsa yadan yamutsa, kamar zaice a’a sai kuma ya karba yasha.

Bayan yasha maganin ne kuma Ramadan ya Mike ya tafi, domin dama hospital zai tafi, ya tsaya bawa Hamman nasa maganine.

Already Abba kuma dama ya tafi company, Riyyam-nsra kuwa yana waje .


Jannart kuwa dake falon ta zaune take, inda tayi kyau cikin wani fitted gown na maroon lace dake jikinta, sosai rigar tabi jikinta ta zauna, saboda yanda dinkin ya fita sosai.

Bak’aramin kyau yau Jannart din tayi ba, musamman da ta watsa jelan gashinta haka bata kitseshiba, tare dasa dan siririn mayafi daga kanta zuwa kirjinta.

Shigowar Mamy ne kuma yasa ta d’agowa, fuskarta dauke da murmushi.

Itama Mamyn murmushi tayi, tare kuma da Kallon Jannart din Cikin kulawa tace.

“Jannart kije mijinki yana kiranki.”

Kai Jannart din ta d’an sunkuyar kasa, cikin sanyi kuma tace.

“To.”

Juyawa Mamyn tayi ta tafi, Ganin hakanne kuma yasa Jannart din mikewa, Cikin yanayin nutsuwarta ta nufi part din nasa.


Ahankali ta murd’a handle din kofar ta shiga, bakinta dauke da sallama.

Saidai kuma dan ja baya tayi, ganinsa da tayi yana waya, hakan yasa ta matsawa jikin kujera ta d’an zauna, wanda hakan yasa suka zama suna fuskantar juna.

Ahankali ta dan saci kallonsa, musamman yanda taga yayi kyau cikin shigar riga da wandon DG dake jikinsa.


Ahankali ya ajiye wayar tare da d’ago kansa ya kalleta.

K’asa tayi da Idanunta, cikin sanyi tace.

“Ina kwana.”

Idanunsa ya sauke akan labbanta zuwa kan kirjinta, wanda dinkin jikin nata ya masifar fitar da shape din samansu.

Kauda kansa yayi batare da ya iya amsa mata ba


Itakuwa Jannart jin bai amsa mata dinbane yasa ta cewa.

“Ya jiki.”


“Da sauki.”

Ya amsa mata da wani irin murya, wanda yasa ta dago ta kalleshi.


Ahankali kuma tace.

“Gani Mamy tace kana kira na.”


Idanunsa ya dan marairaice cikin sanyin murya mai hade da zallan shagwab’a yace.

“Yunwa nakeji sosai, kibani abinci, but mai dan tsami kawai kinji....”

Yaja maganar tasa cikin wani irin yanayi, tare dasa hannunsa ya shafa cikinsa.

Hakan kuwa shiya sanya Jannart ta d’ago Kai ta kalleshi, lokaci daya kuma taji wani irin tausayinsa ya cika mata zuciya.

Ahankali Cikin yanayin ta itama dake kama da shagwab’a tace.


“To meye kakeso? Miya ko kuma abinci?.”

Idanunsa dake lumshewa ya rufe, tare da bud’e labb’an sa ahankali yace.


“I don’t know kimin komai kawai, ko miyan da kika tab’ayi ranan mai ɗan sami.”

“To.” Tace asanyaye tare da juyawa ta nufi hanyar fita.


Koda ta fito daga dakin nasa, Anutse ta soma sauka daga kan steps din.

Dai-dai lokacin kuma Riyyam-nsra yake haurowa saman, hannunsa rike da waya.

Ganin Jannart dinne kuma yasa shi sakin murmushi, Cikin kulawa yace.

“Good morning My Aunty ya jikin Hamma Rayyern.”

Murmushi tayi tare da dubansa, cikin sakin fuska tace.

“Jikinsa da sauki Riyyam, yanzu ma na sameshi afalo.”

Murmushi Riyyam din yayi tare da cewa.

“Masha Allah, bari naje na sameshi.”

Riyyam din ya fada, Yayinda ita kuwa Jannart kaitsaye kasa ta wuce, inda ta nufi kitchine Dan fara had’a masa abunda zaici.

Riyyam kuwa direct falon ya wuce, yana zuwa zuwa kuwa ya zauna akusa da Hamman nasa.

Tare da dan rankwafar dakai cikin sanyi, yace.

“Hamma Rayyern Mammy tanason yin magana dakai, tace kuyi video call saboda taga ya jikin naka, na kirata please?”

Idanunsa ya dan lumshe, akasalance kuma ya d’an gyad’awa Riyyam din Kai alaman “Eh.”


Murmushi Riyyam din yayi cikin, Jin dadi kuma ya zaro wayartasa tare da dannawa numbern Mammy kira video call.

Ring kadan kuwa wayar tayi Mammy ta d’aga.

Tana d’agawa kuwa Riyyam yayi murmushi, tare da Kallon Mammyn nasa Cikin kulawa yace.

“Mammyna Barka da safiya, ga Hamma Rayyern dinnan ku gaisa.”

Ya k’are maganan yana me mik’awa Rayyern din wayar.

Kasancewar kuma kan Rayyern din yana dan jingine ne yasa, Riyyam cewa.

“Hamma Rayyern ga wayan.”

Ahankali ya d’an juyo tare da kai dubansa ga fuskar wayar, wani irin bugawa yaji zuciyarsa tayi da karfi, wanda hakan ya sashi zabura tare da yunkurawa ya gyara zamansa, inda ya sauke ganinsa akan fuskar.........!




Littafin TUBALI dai na kuɗine ko kin gansa a wasu group ɗin na satane

By
*GARKUWAR FULANI*

Matar da hoton fuskarta ya cika fuskar wayar.

Wani irin harbawa yaji zuciyarsa tayi da karfi, wanda har saida hakan yasa shi zaro idanunsa waje.

Da matukar mamaki yake Kallon fuskar matar, Wacce bata da wata maraba da fuskar Ramadan, domin kuwa tsananin kaman Ramadan daya hango akan fuskarta ne ma, ya sanyashi jin wani irin bugun zuciya.

Lokaci daya kuma yaji wani irin nauyi, da kuma dattakun matar ya cika idanunsa, Yayinda daga cikin zuciyarsa kuwa, wani irin girma, kima, karamci, martaba da kuma haibar matar ne ke hauhawa cikin duk harbawar da zuciyarsa keyi.

Ganin fuskar matar ne kuma yasa, kowanne kofar gashi dake jikinsa budewa, take yaji wani irin sanyi na ratsa shi tako Ina, Yayinda kuma nutsuwa ke kara saukar masa.

“Mammy Ina kwana!!”
Ya fad’a cikin tausasa murya daga can cikin maƙoshinsa har zuwa kan labbansa.

Daga b’angaren Mammy kuwa da ta tsura masa ido bata ko k’yaftawa, wani irin abu itama takeji acikin zuciya da gangar jikinta, lokaci daya kuma taji zuciyarta tayi rauni sosai, tabbas Kallon fuskar Rayyern din da tayi ayanzu, yana tattare da wasu abubuwa da dama, ciki kuwa harda abunda ke kwance acikin zuciyarta, a mafi rinjayen tsawon shekarun rayuwarta.

“Lafiya Maud’ona ya jikin ka?”

Mammyn ta tambaya cikin boye rauni, da kuma damuwar dake kwance akan fuskarta yace.

“Alhamdulillah jiki na yayi sauki Mammy.”

Rayyern din ya bata amsa, cikin sanyi da kuma sigar tausasawa.

Riyyam-nsra kuwa dake zaune agefe idanu ya zubawa, Hamma Rayyern din nasa.

Mammy kuwa Daga can b’angaren ta, murmushi ne ya dan bayyana akan fuskarta, cikin tsananin kulawa da kuma muryar tausayawa tace.

“Allah Ubangiji ya karamaka lafiya, ya kareka aduk inda kake, ya tsare gabanka da bayanka, ya kuma nisanta ku da duk wani sharrin mutum da aljan, Allah ya baku zaman lafiya kaida iyalinka, ya albarkaci rayuwarku ya cika haske a rayuwarku Allah yayi maka al'barka!!!.”

“Ameen thumma Ameen Mammy nagode sosai.”

Rayyern din ya fada cikin nuna tsananin jin da d’insa, domin kowacce kalma da Mammyn zata fad’a, jinsa yake yana tasiri acikin zuciyarsa, Yayinda kuma yakejin wani irin farinciki na musamman yana lullub’eshi.

Mammyn ma Ganin farinciki kwance akan fuskarsa ne yasa ta jin dadi aranta, cikin kuma sakin fuska tace.

“Ya Ramadan da Mamyn ku?”

“Lafiyansu kalau Mammy, saidai Ramadan ya tafi wajen aiki, Mamy kuma tana k’asa.”

Ya bawa Mammyn amsa asake, yana mejin Karin nutsuwa na saukar masa sabida mgnar da yakeyi da itan.

“Masha Allah Allah ya taimaka, Ina Surukata Jannart, fatan itama tana lafiya.”

Mammyn ta tambaya da kulawa.

Idanunsa ya d’an lumshe tare kuma da bud’e su alokaci guda, cikin kwarin jikin daya samu yace.

“Lafiya yanzu ta sauk’a k’asa.”

Murmushi Mammy tayi, tare da jinjina kai, cikin farincikin dake da d’a mamaye zuciyarta duk bayan minti guda tace.

“To bari na bawa Zaytoon ku gaisa, gatanan duk ta tsareni da ido.”

Murmushi Rayyern din yayi dai-dai lokacin kuma, Mammyn ta mikawa Zaytoon dake gefen ta wayar.

Karb’an wayar Zayton tayi, tare da fadada fari’ar dake kan fuskarta, cikin muryarta mai dan sanyi tace.

“Hamma Rayyern.”

Saurin d’ago idanunsa yayi, ya kalli kyakkyawar yarinyar da ke magana acikin wayar, wanda muryarta tayi masa sak da wata muryar da yaji kwanannan , idanunsa ya Dan bud’e da kyau, tare kuma da zaro su waje, badon komai ba kuwa saidan Ganin still kamanin yarinyar sak na Ramadan ga kuma kamannin muryarta da waccar tsohuwar kamar dai yadda kamannin Muryar Ramadan Riyyam-nsra da ita Zayton ɗin a can wani sashin na zuciyarshi kuwa kamarsa da Riyyam-nsra ne ya fado masa “Yah salam”.
Yace a ransa a zahiri kuwa,
Idanu ya dan zubawa yarinyar, har na tsawon minti daya, kafun daga bisani ya fadada fara’ar dake kan fuskarsa, cikin sakewa yace.

“Na’am Zayton.”

Murmushi Zayton din tayi, kana cikin jin dadi tace.

“Sannu Hamma Rayyern ya jikinka, Ina fatan dai kayi sauki sosai, kuma kana cin abinci sosai ko?.”

Wani irin Murmushi Rayyern din yayi, wanda har saida kyawawan hakoransa suka bayyana, tashin farko yaji matashiyar budurwar tashiga ransa sosai.

“Jikina da sauki sosai Zaytoon, amma banason Ina yawan cin abinci saboda kada na zama ɗan lukuti kamarki.”

Dariya sosai Zaytoon ta kwashe dashi, saboda daga jin yanda yayi maganar ma kasan akwai tsokana aciki.

“Haba Hamma Rayyern ni har wani jiki ne dani, kanaga saboda banida jiki ne ma ai, Riyyam ya rainani, Hamma Rayyern Ina Auntyna Jannart take?”

Zaytoon din ta tambaya, cike da kulawa.

Murmushi yayi tare da d’an shafa lallausan sumar kansa, cikin muryar tausasawa yace.

“Tana k’asa.”

Kai Zaytoon din ta jinjina, tare kuma da dan rausayar dakai, cikin nuna kulawarta agaresa tace.

“To ka gaishemin da ita kaji, sannan please Hamma Rayyern kana kulawa da kanka kaji, Allah Ya baka lafiya mai amfani.”

Idanunsa ya d’an lumshe tare kuma da sauke Ajiyar zuciya, saboda sosai yaji dadin addu’ar da yarinyar ta masa kana har cikin ransa yake jin sonta a ransa.

Wanda har hakan yasa shi cewa.

“Ameen nagode Zaytoon.”

Kai Zaytoon din ta jinjina, Yayinda shikuwa Rayyern ya mikawa Riyyam nsra dake zaune agefe wayan.

Da sauri Riyyam da zuciyarsa ke cike da farinciki ya karb’i wayan tare da fuskantar screen din wayar, cikin kula dajin dadi yace.

“Mammyna yau kam kinga Hamma Rayyern dinmu ko.”

Kai Mammyn ta jinjina, cike da jin dadi tace.

“Kwarai kuwa Riyyam yau kam naga Rayyern.”

Tayi maganan cikin kasa da murya, ta yanda Riyyam dinne kadai zai iya Jiyota.

Jin abunda ta fada dinne kuma yasa Riyyam nsra tashi, rike da wayan a hannunsa kaitsaye ya nufi dakin Ramadan.

Shikuwa Rayyern maida kansa jikin kujera yayi, tare da lumshe idanunsa, ahankali yake lumshe idanunsa, yana mejin wani irin nutsuwa na saukar masa.

Mammy da Riyyam kuwa basu wani jima suna magana ba, Mammy ta katse kiran.

Acan Ethiopia kuwa bayan Mammy ta ajiye wayanne, Ta zame daga zaunen da take tare da durk’usawa k’asa tayi sujjada.
Na nunawa Allah tsananin jin dadinta, da kuma godiya agaresa, domin komai da yake faruwa shine ya tsarashi, shine kuma yake bawa ahalinta dama ita kanta kariya akoda yaushe.

Acan b’angaren Jannart kuwa Anutse ta kammala gasa masa roasted fish, tare da matsa masa ruwan lemon tsami aciki,


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login