Showing 87001 words to 90000 words out of 350584 words

Chapter 30 - Tubali Book 1 Hausa Novel Complete

da mata kasamu kayi aure, kaga Abba yace bazanyi aure ba harsai kayi, ni kuma Allah yanzu aure nakeso nayi, bana son na rasa Rayhanna please Hamma na.”

ya k’are maganan yana me d’an langwab’ar da kansa gefe.

Shikuwa Rayyern d’ago kansa yayi, da kuma fuskarsa wacce ta sanja kala zuwa yanayin bacin rai.

Wani irin kallo ya watsawa Ramadan din, cikin hade fuska yace.

“Rufe min baki Ramadan kada fa ka tunzura min zuciya Kaine zaka tsaramin yanda zan tafiyar da rayuwata? Ko ka fini sanin abunda nakeyi ne, da har zaka zo kana cewa wai nayi aure! Kai ubana ne!? ko yayana!? kama fini sanin abinda ya dace kenan?.”

Rayyern din ya k’are maganan cikin fad’a.

Wanda hakan yasa Ramadan Dan sunkuyar da kansa, cikin yanayin sanyi kuma yace.

“Ayyah Hamma Rayyern kayi hakuri Insha Allah bazan sake ba kaji kayi haƙuri.”

Kai Rayyern din ya kawar, Yayinda Abba da Mamy kuwa suka kalli junansu.

Ramadan kuma mik’ewa tsaye yayi, tare da kama hannun Riyyam-nsra suka fice daga cikin falon.

Fitansu daga cikin falonne kuma yasa Abba d’ago Kai ya kalli Rayyern din.

Yayinda su Ramadan kuwa suna fita, kaitsaye wajen Baba Maud’o dake zaune abakin gate suka nufa.

Ganin su dinne kuma yasa Baba Maud’o sakin murmushi.

Bayan sun zauna akan dogon bencin da Baba Maud’on ke kaine kuma.

Baba Maud’on Ya kalli Riyyam-nsra tare cewa.

“Riyyam ya mutanen can k’asar taku, da su Mammyn ka da Zaiton.”

Murmushi Riyyam-nsra yayi, tare da gyara zamansa ya kalli Baba Maud’on cikin kuma jin dadi yace.

“Munyi waya dasu dazu kowa da kowa yana nan lafiya, sunma ce na gaishe da kai, saboda na tura musu hotonka, har Zaiton tana cewa wai itama zata zo ka nad’a mata irin abunda kake sawa afuskarka, wai zatana boye fuskarta saboda Samarin dake damunta.”

Yar dariya Baba Maud’o yayi, tare da jinjina kansa.

Cikin jin dadi yace.

“To shikenan Idan tazo zan koya mata yanda ake na dawa, ai rawani ne ba komai ba, nadashi kuma ba wahala.”

“To Baba Maud’o nima dai ai watarana zaka koya min ko, sai naje na koya mata.”

Kai Baba Maud’on ya jinjina alaman.

“Eh.” Daga haka kuma suka ci gaba da hiransu.


Ethiopian.
Adai-dai lokacin ne kuma Mammy dake zaune akan sallaya ta kurawa, hoton dake kan screen din wayar nata idanu, wanda kuma hoton Baba Maud’o ne da Riyyam ya turo mata.

Azahirin gaskia ba kuma tana Kallon hoton da wata manufa ko tunani bane.

Kawai dai tana mamamkin irin shigar da taga mutumin yayi ne, saboda su anan basu tab’a Ganin irin shigar ba.

Ajiye wayar nata tayi tare kuma da watsar da duk wani tunani dake ranta, kaitsaye ta mike daga kan sallayan ta shige kitchine.

Acan falo kuwa Abba dake Kallon Rayyern d’an gyara zamansa yayi.

Tare da fuskantar shi kana cikin yanayi masifa faɗa da kuma umarni yace.

“Uhmmm RAYYERN kenan.
Saboda kawai yace maka kayi aure shine kake daka masa irin wannan tsawan? Da ɗaga jijiyoyin wuya.
To shi meyene laifinsa, saboda kawai yace ka cika martabarka, ka kuma raya sunnar Annabi Muhammad SAW shine, yayi laifi?”.
Ya ƙare mgnar tare da tsareshi da idanun
Da dole yasa RAYYERN yayi ƙasa da kansa.
Shi kuwa Abba kwaffa yayi tare daci gaba da cewa.
“Yoh wai kai azatonka da tunaninka haka zaka ta zama babu aure ne, saboda kawai kaga na zuba maka ido tsawon shekaru, kayi tunani da hankalin ka fa Rayyern, ayanzu Kai ba yaro bane, Domin kuwa kabawa shekaru 30 baya, shin kana tunanin banason yin aurenka ne? Ko atunaninka bana da buk’atar Ganin aurenka ne? To kasani duk da cewar nasan tabbas na sakar maka ragaamar komai, na tara maka ayyukan da sukafi karfinka, bawai Ina nufin ka zauna haka babu aure bane ba wurin aiki kawai nake son ganin kamalarka ba harda aure, Tabbas banajin dadi aduk sanda ka nuna cewar babu maganar aure kwata-kwata agabanka, kaine babba akan Ramadan, ya kuma zama dole kayi aure, Domin duk wani Namiji mutumcinsa da Darajarsa bata cika ko a idanun mutane, har sai in yana da aure, komin dukiya da mulkinsa kuwa, aure shine abunda ke maida Rabi ya dawo Guda, ka d’aga mutumci da darajarka ta hanyar yin aure, Allah dakansa zai dubi al’amuranka, amma ace akoda yaushe Kai baka da zance sai na cewar bakason aure...”


*Albishirinku! Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA*

NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA.
Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.

Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke taimakawa (sex hormones 😍) dinki.
Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!?
Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu.
Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki?
Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu,
Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ki zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan.
Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya.


Akwai daya bangaren wato *KAMSHI*
Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, sayan na gari maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia.

Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.

🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA
*(GARKUWAR MA'AURATA)*



By
*GARKUWAR FULANI*
11/15/21, 7:21 PM - Auntyna: TUBALI 23


D’an gyara zamanta tayi, tare da sake fuskantar cameras din dake shooting fuskarta.

Ajiyar zuciya ta d’an sauke tare da nemo jarumtarta dake suɓuce mata,
cikin Taushi da kuma amon muryanta zakin tace.

“Assalamu Alaikum Masu kallonmu, sannunmu da arzikin sake saduwa, acikin shirinmu mai farinjini wanda mukeyi Domin farincikin ku, wato Bak’onmu na Mako, To ayau dai shirin namu ya gam da katar yayi babban kamun gayyato muku wani babban bak’o, wanda nasan idanuwanku suna cike da dokin ganinsa. Wannan bako kuwa ba kowa bane face. Dr...!”.
Sai ta kuma datse sunan tare da sakin murmushi.
Wanda hakan yasa kab masu kallo suka ɗokanta da son jinnwayene baƙon makon.
Mayafin kanta ta ɗan gyara tana mai jin harshen ta bazai iya furta sunansa ba, cikin nitsuwa ta tare da lumshe taci gaba da cewa.
“Sanannen mutumin da sunansa yayi shuhura acikin kasarmu Nigeria dama wajenta baki daya, nasan da yawan masu kallo basu tab’a Ganin wannan bak’on namu ba.
Dan yauce rana ta farko daya amsa gayyatar wata kafar sadarwa ta jarida, da TV. Alhamdulillah sai namu a yau.
Kasancewarsa Babban Doctor kuma babban d’ankasuwa da duniya ke damawa dashi, saboda haka yau dai gamu gashi, zakuma mu haska mukushi, inda zai fayyace mana koshi din waye.”

D’an tsagaitawa da maganan nata, tayi tare da juyowa Ahankali ta fuska ce sa.
Cikin muryarta mai taushi tace.

“Doctor barkanka da zuwa, barkanka kuma da shigowa cikin wannan tasha tamu mai Al'barka, da fari dai munaso ka gabatar da kanka ga masu kallonmu.”

Numfashi ya d’an sauk’e, batare kuma da wani sakin fuska ba, ya dago da kansa ya d’an kalli cameran a fakaice, cikin muryarsa da ako yaushe yake kara bayyana asalin wanene shi yace.

“Dr.Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara.”

Ya k’are maganan atak’aice, Cikin kuma halin nitsuwa.

Kai Jannart din ta jinjina, tare da hade yatsunta awaje daya, cikin tsananin kwarewa da sanin makamar aikinta tace.

“Masha Allah to Dacta, yanzu dai ka gabatar da kanka awajen al’umma, saura kuma mu shiga cikin shirin namu ka'in da na'in,.
Dai-dai lokacin kuma aka ɗan ɗauke fuskokinsu aka sa ɗan sautin tambarin tashar Arewa 24 din.
Kana aka dawo dasu.
Cikin nitsuwa ta ɗan kalleshi a fakaice kana a hankali tace.
“Shin amatsayinka na cikakken Likita, wanda kasa keji dashi, wacce irin shawara zaka bawa al’umma dan kula da lafiyarsu da matakan kariyar riga-kafi?.
Sannan kuma ya kake Ganin irin yanda al’amarin k’asarnan yake, ma’ana irin halin da al’ummar k’asar take ciki, da kuma irin k’alubalen da muke fuskanta more Especially wurin kiwon lafiyar kananan yara da mutanen karkara da tsofaffinmu, Sannan wani irin hanya da kuma mataki zamu bi, Domin mu samu nasara akan yaƙar cututtukan dake addabar al'ummar ƙasar mu?
Then menene matsalarmu aharkar malaman kiwon lafiya?”.

Kanshi ya ɗan kauda gefe tare da yamutsa fuska, ɗan gajeren tsaki yaja.
Ji yadda yarinyar nan take zuba babu ƙaƙƙautawa kamar carbi ya tsinke ko numfashin bata ja.
Ta wani jero min tambaya kusan goma, a dungule.
Ni Radio ne ko ni parrot ne da zan iya haka.
Duk yayi tunanin cikin second 5.
Numfashi ya ɗan fesar kana cikin haiba da dakewar murya yace.
“Privet Hospital!!!
Sune matsalan kiwon lafiyar kasarmu.
Domin sune suke dak’ushe asibitocin gwamnati, har suke zama ba masu inganci ba.”

Ya fad’i maganan kai tsaye, batare kuma da wani dar ko shakka ba.

Jannart kuwa Kai ta d’an jinjina, tare da sake rik’on wani farin card dake hannunta, saboda acikine duk wani tsare tsaren tambayoyin da zatayi masa suke.

Kanta ta d’ago daga Kallon takardar da takeyi, still kuma Cikin muryarta da akoda yaushe take fitar da daddad’an sauti tace.

“To Dakta. munji abunda kace. Kuma al'umma zata iya gamsuwa da hakan.
Toh amma kamar wani mataki za’abi, Domin asamar da ingancin asibitocin Gwamnati da kiyaye lfy?.”

Numfashi ya ɗan fesar a hankali kana yace.
“Dole gwamnati ta tsaya ta gyara asibitotin ta, ta ingantasu hade da kawo nagartattun kayan aiki, da kuma kwararrun ma’aikata, baya ga haka kuma ta rika biyan likitotin isassun kudaden da zasu iya biya musu bukatunsu, saboda mafi akasari acikin kasar bawai Nagartattun Doctor’s dinne bamu da suba, kawai dai basa samun yanda suke sone, hakanne kuma yasa suke fita wasu k’asashwn suje su fara aiki Acan, ko kuma kowannensu saiya zaga gefe yaje ya bud’e asibitin kanshi, saboda baisamu yanda yake so a gwamnati ba, wannan dalilin yasa ayanzu asibitocin gwamnati suka lalace suka zama kara zube,, Domin anriga da ancire Tubalin abunda aka gina asibitin akai haka yasa duk mai ƙarfi da yar wadata bazaibi ta kan asibitin gwamnatin ba, wanda kuma da al'ummar ƙasa aka ginasu.
Sannan yana da matukar muhimmanci ga iyayen yara suke kula da tsabtar jikin raya da muhalli da abinda zasuci domin shine babban rigakafi.”
Ya k’are maganan yana me gyara zaman necktie din dake wuyansa.
Sosai yayi masifar kyau yadda yake dan jujjuya fararen yatsunshi

Inda Jannart kuwa ta ci gaba da cewa.

“To Doctor yaya za’ayi agyara matsalar Government Hospitals din domin in ƙantasu ta yadda al'ummar ƙasa zasuje garesu da kekkyawan yaƙini!?.”

Dan muskutawa yayi still kuma cikin rashin tsoro ko fargaba cikin yaƙinin da Kekkyawar manufa yace.

“To Da farko dai asibitotin gwamnati abunda zai gyarasu abu maisauki ne!?”.
Da sauri ta ɗan fuskanceshi tare da cewa.
“Duk da lalacewar da sukayi gyaran mai sauƙin ne? Ta yaya ko kuma ta ina gyaran zai fito da sauki!?”.
Cameras din ya ɗan kalla kana ya gyara zamanshi tare ɗaura kafa ɗaya bisa ɗaya cikin masakaicin amo yace.
“Idan har gyara akeso ta yadda zasu in ƙanta tofa dole daga kan, Shugaban k’asa, Governors, Ministers, senator's har zuwa kan ciyamomin kana kama daga Sarki, Waziri, Galadima, Wambai, Chiroma, Durbi, Garkuwa, Ɗan buram, Majidadi, Ma'aji, dama duk wasu masu fad’a aji, na siyasa da masarautun gargajiya. suyi kokarin daina zuwa asibitotin kudi, ko fita kasashen waje Dan duba lafiyarsu, su tsaya su ingata asibitotin Gwamnati, ta hanyar dasu kansu asibitotin zasuna basu Kekkyawar kulawa,
Ya zama asibitin da Sarki zaije.
To shi fadawan sarki zasuje.
Kana asibitin da shugaban kasa zaije ya zama shine na talakawa, ta hakane zai sa shugabanni su san halin da asibitocinsu suke ciki, da inƙancin likitocin da kayan aikin.
Haka zai sa a kula da in ƙancin asibitocin.
Domin duk wani asibitin gwamnati matukar akwai ingantattun Doctor’s da kayan aiki da watar tsabtacewa.
Toh dai-dai yake da duk wani asibitin kudi, hakanne kuma zaisa asibitotin kudin su dakushe, su durkushe.
saboda yawnacinsu bawai anginasu Dan taimakon al’umma bane, anginasu ne kawai saboda neman kudi irin na yaki haram yaki halal, tayanda talaka bazai tab’a amfana dasu ba sai dai su cika aljihunsu.”
Da sauri Jannart ta juyo ta kalleshi.
Ido cikin ido sukayi da juna,
Bakinshi ya taɓe tare da yimata wani irin munafukin harara, hakane yasa tayi saurin yin ƙasa da kanta
Kai ta jinjina, cike kuma da gamsuwa da kalaman nasa tace.

“Tabbas maganarka tatafi Kan hanya mai kyau, sai-dai kuma amma baka ganin yin hakan zai dakushe mutane da dama, musamman ga masu privet hospital kamar yanda ka fad’a!!!.”

Kansa ya d’an girgiza, sannan kuma akaro na farko da tun zamansa awajen ya dago kansa da nufin ya kalleta da kyau dan tambayar da tayi masa.
Saidai ko secan daya bai dauka yana kallontan ba yakau da kansa gefe.

In don’t care manner yace.

“Hakan ba wata matsala bace ai, Domin bani da yakinin cewa yin hakan zai tauye musu hakkinsu”.
Da sauri ta kuma cewa.
“Toh kuma kake bada shawara a rushe asibitocin?”.
Wani irin kallo ya ɗan watsa mata.
Sabida ta mishi tambayar cikin gajin haƙuri irin nasu na ƴan jaridu.
Dan bata tsaya taji ya dasa Ayaba.
Koda yake haka suke.
Yan jaridun suna jin daɗin jefowa mutun tambaya kamar sauƙawar aradu ko kuma titsiye.

Cikin tsare fuska yace. “Dama meyake sawa su bude nasu asibitotin?”.
Ya mata tayarma tare da tsareta da ido.
Yar-yar haka taji tsikar jikinta na tashi.
Haka yasa da sauri ta kauda kanta gefe.
Shi kuwa kai ya jin jina tare da cewa.
“Baki sani bako?
To bari in gaya miki...”
Ya kare mgnar yana mata hararan ƙasan ido kana yaci gaba da cewa.
“Dama rashin samun isasshen abunda zasu rufawa kawunansu asirine, saboda sometimes acikin asibitotin Gwamnatin, gwamnati bata biyansu al'bashi akan kari, baya ga haka kuma bata basu isassun al'bashin da zasu dauki nauyin iyalansu sabida gwamnatin tayiwa malaman jinya dana makarantu riƙon sakainar kashi Alhamdulillah gwarama wannan gwamnati da muke ciki.
Duk da haka ana buƙatar ƙari.
Domin duk lokacin da Gwamnati ta fara biyansu isassun al'bashi, To ba wani abu da zaisa suje su bude privet Hospital toh ko sunje sun buɗewama wa zai je musu in dai asibitocin gwamnatin nada inkanci , Domin ak’asarnan ba yawan asibiti muke da bukata ba, ingancinsu kawai shine abun buk’atar mu, tayanda talaka da maikudi da fulanin daji zasu samu gamsashshiyar kulawa, batare da nuna wani banbanci ba!!!.”

Ajiyar zuciya Jannart ta sauk’e, kana kuma cikin yanayin nutsuwa tace.

“Mungode sosai Dr. inafatan kuma Gwamnati zataji shawarar daka bada kuma tayi aiki dashi, yanzu kuma zamu shiga babi na biyu. wanda ya shafi b’angaren kasuwanci kafin mu dawo nan a likitance.

Yah Salam shine abinda ya faɗa a ransa.
Sabida ya lura yau bakinshi sai yayi tsami sabida magantuwa da wannan fitinenneyar yarinyar take sashi.
Kamar a tsakiyar kanshi yaji ta kuma cillo mushi tambaya.
“Shin Dakta wacce irin shawara zaka bayar, agame da yanda sha’anin saye da sayarwa ya zama acikin k’asarnan, misali ta yanda ayanzu kayan abinci yayi tsada sosai, akullum wasu daga cikin yan kasuwa k’ara farashin kayansu suke, rayuwa tayiwa talaka tsada, manyan y’an kasuwa da kamfanoni sun had’e kai da baki waje daya, Koda yaushe farashin kaya


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login