Showing 303001 words to 306000 words out of 350584 words

Chapter 102 - Tubali Book 1 Hausa Novel Complete

MARUBUTA*




*Albishirinku! Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA*

NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA.
Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.

Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke taimakawa (sex hormones 😍) dinki.
Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!?
Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu.
Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki?
Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu,
Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ki zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan.
Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya.


Akwai daya bangaren wato *KAMSHI*
Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, sayan na gari maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia.

Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.

🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA
*(GARKUWAR MA'AURATA)*


Cikin tsananin tashin hankali da ruɗani ya iso garesu.
Tare dasa hannunsa ya jawota jikinsa yana mai cewa.
“innalillahi wa innailaihi raji'un Janna Meya sameki?”.
Karkarwa jikinta yakeyi kamar zata zube ƙasa, kana ga yunƙurin yaƙi tsayawa, wata iriyar fitinenneyar zuface mai ƙarfi ta keto mata.

Har yanzu kakarin takeyi amman aman yaƙi zuwa.
Da sauri ya ruggume ta a jikinsa, bayanta ya fara shafawa tare da cewa.
“Yah Salam Janna meke damunki gaya min”.

Narkewa tayi a jikinsa dan gaba ɗaya ƙarfinta ya tafi ji takeyi kamar zata faɗi.
Ramadan ne ya ja musu kujera tare da cewa.
“Hamma zaunar da ita”.
Cikin tarin damuwa yace.
“Ramadan zata faɗi kaga bafa yadda takeyi, Please ka duba min ita, Abba zo kaga yadda takeyi fa innalillahi wa innailaihi raji'un Jannaaaaaaaaaa”.
Yayi mgnar cikin raunatacciya kuma gigitacciyar Muryar da tasa Abba zuwa da sauri.

Gaba ɗaya ya gigice ita kuwa har yanzu yunƙuri da kakarin aman takeyi gwanin ban tausayi.
Cikin damuwa Abba yace.
“Subahallahi, Rayyern ajiye ta. Jannart meke damunki? Ramadan maza ɗauki akwatin taimakon gaggawa”.
Da gudu Ramadan ya nufi side ɗinsu.

Mamy kuwa da sauri ta kamo hannun Jannart ɗin tare da cewa.
“Ya ilahi Jannart kiyi mgn meke damunki gayamin”.
Cikin azabebben kakari da yunƙurin da takeyi ta nunawa Mamy miyar kasen daketa tururi har yanzu tace.
“Mamy a rufe miyar nan wari yakeyi”.
Cikin tsananin mamaki Mamy ta rufe kular tare da cewa.
“Jannart wari kuma?”.
Wani dogon numfashi ta fara ja mai tsawo jin an rufe miyar ta fara jin sauƙin tururin dake shiga hancinta, cikin sauƙe numfashi ta manna bayanta da jikin Rayyern ɗin tana mai maida numfashin.

Kai Mamy ta jinjina tare da sauƙe numfashi a hankali tace.
“Ayyah Jannart sannu Rayyern yanzu haka take fama da amai?".
Kanshi ya jujjuya mata yana mai sharce mata zufan dake goshinta yace.
“A'a Mamy ni ban taɓa ganin tana amai ba”.
Gyara zamanta tayi still dai hannunta na kan hancinta.

Dawowar Ramadan ne yasa Abba ɗan ja baya tare da cewa.
“To gsky muje asibiti kawai zaifi”.
Cikin sauƙe numfashi tace.
“Abba aman ya tsaya ai, ba matsala”.
Tayi mgnar cikin rauni da kasala.
Cikin kulawa Abba yace.
“Anya kuwa Jannart”.

“Da gaske bana jin komai Abba”.
Shi kuwa Rayyern juya kujerar yayi ta fuskanci washing hand baby ɗin cikin yanayin mai cike da tsantsar kulawa, ya wonke mata hannunta.
Da bakinta, sai kuma ya tare ruwa yasa mata a baki, kuskure bakinta tayi, kana ya wonke cikin wurin.
Sannan ya juyo kujerar, kan table ɗin.
Ganin abin nasa azimun ne yasa Abba juyawa ya koma falo.

Ramadan kuwa da yanzu ya iso, cikin kulawa yace.
“Aman ya tsaya?”.
Murmushi Jannart tayi tare da cewa.
“Eh ya tsaya zo kaci abinci.”
Cike da mamaki duk suka zauna suka sata a tsakiya.
Suna kallon yadda take sauƙe numfashi.
Cikin kulawa Mamy ta jawo filas cup ta ɗauka mai ɗan girma, kunun gombawa ta tsiyaya cikinsa kana ta miƙa mata.
Da sauri ta amsa tare da kai cup ɗin bakinta dan wani irin masifeffen kwaɗayin kunun taji wanda a take yawun bakinta ya tsinke, lumshe idanunta tayi sabida jin dadinsa.
Da sauri Ramadan ya ɓalle maganin amai kwara ɗaya, ya miƙa mata, ba musu ta amsa ta haɗiyeshi sabida taji azabar kakarin yasata yin laushi.

Shi kuwa Rayyern gaba ɗaya ya gaza yin komai sai kallonta yake cike da mamaki, shi kansa sai yanzu yake ganin wani irin matsanancin farin da tayi har wani yellow-yellow tayi, ko dan acan yana ganin turawane yasa baiga tsananin farintaba, ko kuma dan yanzu Mamy dake ba fara sosai bace na kusa da ita koma dai menene farinta yayi yawa yayi kamada dana masu ɗanyen jiki.

Ita kuwa Mamy plate ta ɗauka pepper chicken ɗin ta zuba masa tare da soyyam arish kaɗan. Sai kuma ta haɗa masa tea mai zafi.
Jan plate ɗin yayi gabanshi jin Mamy na cewa.
“Ungo maza kaci kuje ka dubata a asibitin”.
Fork ya ɗan ɗauka tare da soka tattausan tsoka da arish kana ya nufi bakinta dashi.
Da sauri ta jujjuya mishi kai kana tace.
“A'a nifa kunun nan ya isheni”.
Ta kare mgnar tana toshe hancinta.
Haka kuwa akayi duk abinda aka ce mata gashi sam taƙi.

Ramadan kuwa juyawa yayi ya dawo falo don maida kaya aikinsa.
Abba ne ya nuna masa jakkunan da sunan Rayyern ke liƙe a kai yace.
“Kai masa su ɗakinsa”.
Ba musu ya ɗaukasu.

Yana sauƙowa kuma Abba ya nuna masa na Jannart ɗin tare da. Nuna mishi ɗakinta, haka ko akayi ya ɗauka ya kaisu kana ya wuce dinning area.

Sukaci abinci,

Suna fitowa falon Mamy ta kalli Jannart tare da cewa. “ Shiga side ɗinki, ki samu ki ɗan watsa ruwa zakiji ƙarfin jikinki”. Ta ƙare mgnar tana nuna mata ƙofar ɗakin nata, haka yasa Jannart ta
nufi inda tasan nanne ɗakinta.

Shi kuwa Rayyern ido ya zubawa Mamy.
“Kai me kake kallonta haka?”.
Abba ya faɗa cikin tsare gida.

Shi kuwa Rayyern cikin kwaɓe fuska yace.
“Babu”. Yayi mgnar kamar wani abun tausayi.

Ita kuwa Jannart a hankali ta fito Bathroom ɗinta, cikin yanayin kasala.
Tana mamakin abinda yasata amai, da kuma sauyin da ta samu a jikinta tunda tayi aman take jinta wata iriya a haka dai tayi ta ɗan shafa mai, kana ta sauya kaya sannan ta kuma fitowa. duk suna falon sai Abba dake can waje wurin Baba Mauɗo.

Hira sukeyi cike da kewar juna.
Ɗikunan bikin da akayi musu.
Mamy ta fito musu dashi.
Suna kallo, cikin jin daɗi Jannart tace.
“Masha Allah Mamyna mun gode”.
Sai kuma suka kalli Rayyern da ya amsa kiran da Riyyam-nsra ke tayi masa.
“Barka da isa lfy Hamma Rayyern”.

“Barka dai Riyyam-nsra, ina Mammy yaushe zaku taso?”.
Yaya tambayar a jere.
“Mammy na gida ni kuma ina wurin surkarka ne, zan sallameta, in sha Allah gobe uwar haka ai tuni mun iso”.
Cikin kula yace.
“Toh Allah ya kawo mana ku lfy”.
Amin yace kana ya bawa Jannart wayar kamar yadda Riyyam-nsra ɗin ya buƙata cikin jin dadi tace.
“Ga nan ɗikunan ka dana Zaiton hardama Mammy an mata ɗinki Allah yasa dai suyi mata”.
Cikin sauri yace.
“Zasuyi ai Hamma Ramadan ya haɗata da telan sunyi video call ya ganta”.
Cikin zaƙuwa tace.
“To Allah ya kawoku lfy”.
Amin yace kana sukayi sallama.

Su kuwa Anan sukayi ta hirar yadda bikin zai kaya har zuwa wani ɗan lokacin.

Jannart ce zaune gefen.
Mamy data bata cup ɗin kunu ganin yanzuma taƙi cin abinci.
Amsa tayi tare da cewa.
“Nagode”.
Da sauri Mamy tace.
“in akwai abinda kike son ci ki gaya min in dafa miki”.
Da sauri tace.
“Ba komai Mamy yanzu kam na ƙoshi in nasha kunun sai kuma da safe.”
Ta ƙare mgnar tana amsa kiran Barrister Kabeer daya shiga wayarta.
“Masha Allah ɗiyata ta dawo”.
Cikin jin dadi tace.
“Abbana na dawo, a kawo min su Hafeez mana”.
Da sauri yace.
“Kada ki damu in Sha Allah da safe zan kawo miki su”.
Cike da jin daɗi tace.
“Alllah ya kaimu”.

“Amin ɗiyata, ki huta gajiya, zamuzo harda Auntynki”.

Cike da jin daɗi take.
“Kai Alhamdulillah naji daɗi na”.
Daga nan sukayi sallama.

Rayyern kuwa da Ramadan, tuni suka wuce Mai Nasara hospital.

Lungu da saƙo suke zagayawa, yayinda ko ina yake fes-fes haske kamar rana.
Jinjina kai Rayyern yayi tare dafa kaɗan Ramadan kana yace.
“Alhamdulillah Ramadan kayi ƙoƙarin naga dukkan majinyatanmu cikin Kekkyawar kulawa ta musamman komai yana tafiya dai-dai bitsa tsari, naji daɗi haka, nasan ko yanzu na barka da aikin asibitin zakaji da komai”.
Cike da jin dadin ya yaba masa da akayi ya buɗe musu ƙofar Office ɗin Rayyern ɗin kana suka shiga ciki yana cewa.
“Amman dai za'a bani hutun amarci ko”.
Tsaresa da ido yayi hakan ne yasa yayi ƙasa da kansa.
Sai kusan ƙarfe goma harda wasu mituna suka fito.

Daga asibitin kai tsaye gidansu Raihana ya wuce ganin sha ɗaya bata cikaba sabida jarabebben naci.

Shi kuwa Rayyern daga asibitin gidansu Usman PA ya wuce.
Nasir ƙanin Usman ɗin da Mahmoud abokinsa daya fara bawa Jannart bayanai a kan Rayyern ɗin ya samu a ƙofar gidan.
Ganin sa yasa Naseer saurin buɗe masa ɗan madaidacin gate ɗin.
Yana mai cewa.
“Masha Allah Hamma Rayyern Barka da dawowa, mu isa ciki”.
Cikin ɗan sakin fuska yace.
“Umma na nan ko?”.
Ya gyaɗa mishi tare da cewa.
“Harda Yah Usman ɗin ma”.

Suna shiga falon suka samu, Umma da Usman ɗin suna zaune.
Ganin uban gidan nasane yasa Usman miƙewa da sauri tare da cewa.
“Kai Sir mai abin mamaki baka gajiya dayi mana bazata”.
Cikin alamun shaƙuwarsu yace.
“Umma wurinki nazo in gaidaki duk da naga dare yayi”.
Ya ƙare mgnar yana zama gefen Umma, shi cike da jin dadi Umma tace.
“Aiko naji daɗi Rayyanu na, ya hanya ina surkar tamu tana lfy dai ko?”.
“Alhamdulillah Umma”.
Sai kuma ya miƙa wa PA hannu wanda shima hannun ya miƙa masa musabiha sukayi kana sukaci gaba da hira.
Harsu Naseer.
Sai kusan ƙarfe sha ɗaya da kwata kafin ya sallamesu, ya tafi.

A gida kuwa, hira sosai Mamy keyi da Jannart tana bata labarin rawan kan Ramadan dariya sosai takeyi harda kerkerta.

A can gidansu Raihana kuwa, Daddynta ne ke tsaye jikin window ɗakinsa dake sama, cikin yanayin nazari da zurfin tunani ya zubawa Ramadan dake zaune gefen Raihana yanayi mata wani irin kallo mai kama dana maita, kallone da duk wanda ya gani yasan na cikekkun jarababbune, ya lura gaba ɗaya jikin yaron rawa yake kamar mazari.
Numfashi mai nauyi yaja tare da sake labulen ya koma ya zauna yana kallon time.

Shi kuwa Ramadan sha ɗaya da rabi dai-dai ya sallami Raihana,
har gaban mota ta rakasa, cikin narkewa yace.
“Baby wlh ji nake kamar kada in tafi, gani nake dararen suna yimin tsawo”.
Cikin jin kunya tace.
“Saida safe”.
Tana faɗin haka ta juya ta tafi.

Cike da zumuɗi yaja motar ya tafi.

A falon ya samu Mamy da Jannart suna hira, haka yasa ya zauna akaci gaba da hira Jannart na mishi tsiya.

A hankali Mamy ta sauƙe numfashi ganin Jannart ɗin nata hamma da lumshe idanunta, cikin kulawa tace.
“Jannart jeki kwanta dare yayi naga kina ta hamma. Gashi har sha ɗaya da rabi tayi gota”.
Murmushi tayi tare da lumshe idanunta.
Cikin tsokana Ramadan yace.
“Gsky kam Mamy bare ma masu ƙaramin ciki da bacci”.
Cikeda mamaki ta juyo ta kalleshi sai kuma ta kauda kao ganin dariyar tsiya yake mata.
Shi kuwa miƙawa tsaye yayi tare da cewa.
“Uhmm ni bari inyi ciki in Kira tawa masoyiyar”.
Ya ƙare yana haurawa sama.

Itama Jannart miƙewa tayi a kunyace, dan Ramadan ya kumyatata,
A ranta tace.
“Wa ciki yoh ni ina ni ina ciki? Indai ba'a ruwa ake shansaba.”
A fili kuwa kai a sunjuye tace.
“Mamy sai da safe”.
Cikin jin dadi Mamy da dama tuni kallon mai ciki takeyi mata tace.
“Toh Allah ya bamu al'khairi ɗiyata”.
Amin tace tare da wucewa ɗakinta, kana ta maida ƙofar ta rufe.

Ita kuwa Mamy dake falo da sauri ta juyo ta kalli Abba da ya shigo falon, gefenta ya zauna tare da cewa.
“Kawo min coffee ɗina nan”.

“Toh yau kuma a falo za'a sha kenan”.
Tace tana nufar kitchen tana mamakin hakan.

Dai-dai lokacin kuma Rayyern ya turo ƙofar ta shigo tare da sallama a bakinsa.
Amsawa yayi cikin yanayin tsare gida, gefen Abba nasa ya matso cike da son ganin wulgawar Jannart ɗin ya fara jujjuya idanu kana a hankali yace.
“Abba Barka da dare”.

“Yauwa Barka dai”.

“Uhm Abba yau kuma kai kaɗai inasu Mamy”.

Kanshi ya juyo ya kalli Mamyn dake shigowa.

“Babana ka dawo ne”.
Mamy ta faɗa cikin kulawa.
Kanshi ya ɗan jinjina tare da kallon ƙofar falon Jannart a karo na barkatai yace.
“Eh Mamy ya mai jikin?”.
Cikin kulawa da yanayin da yake ciki tace.
“La Alhamdulillah ba komai bata sake aman Bama, tun ɗazuma hira mukeyi da naga tana jin baccine nace taje ta kwanta”.
Kanshi ya jinjina kana ya kuma kallon Abba daya tsare fuska.

Miƙewa yayi tare da cewa.
“Bari inje in ɗan watsa ruwa”.

Da sauri ya kalli Abba da yace mishi.
“Toh saida safe”.
Yi yayi kamar bai jisaba ya haura saman.

Shi kuwa Abba coffee ɗinsa da Mamy ta haɗa masa ya fara sha,
ita kuwa Mamy gefenshi ta zauna tana ɗan mishi hira.

Bayan kamar 30 minute, Abba ne ya juyo kansa a hankali ya kalli steps ɗin sauƙowa, sabida jin takun mutun. Rayyern ya gani cikin wata tattausar jallabiya maroon collor mai shaƙi.
Shima Rayyern Abban ya zubawa idanu cike da mamakin ganinsu a falon har yanzu.
Cikin kauda kai ya ɗan sosa sajensa da bayan hannu kana ya ƙarasa sauƙowa ƙasan.
“Babana bakayi bacci bane?”.
Cewar Mamy. Fuskarsa ya ɗan kwaɓe tare da kallon ƙofar ɗakin Jannart wanda hakan yasa Abba jinjina kai tare da tsareshi da idanu shi kuwa, cikin sanyi yace.
“Eh da..ma”.

“Dama me?”. Abba ya faɗi still idansa na kansa, da sauri yace.
“Uhmm Dam Chocolate na nazo karɓa”.
Yayi mgnar cikin inda-inda da kallon ɗakibta,
Shi kuwa Abba gyara zama yayi tare da cewa.
“Naga ai ɗazu Ramadan yasa wasu a Fridge je ka duba”.

Kwaɓe fuskarsa ya kumayi kamar zaiyi kuka.
Allah ya sani bazai iya bacci ba tare da itaba.
Yana begen ɗumi da ƙamshin jikinta, cikin ransa yace.
“Abba bazaka gane bane”.
Asheko bai san mgnar ta fito fili ba.

“Bazan ganeba kamar yaya? To ai sai ka ganar dani”.
Abba ya faɗa a daƙile.

Da sauri ya nufi kitchen ɗin yana cewa.
“Eh Abba babu irin wanda nake sone a Fridge ɗin shiyasa”.
Sai kuma ya juyo ya haura saman.

Shi kuwa Abba kanshi ya jinjina tare dayin mgnar zuci.
“Mara kunya da bai san kawaici ba, ka kalli tsabar idon mutumin daya baka kyautar mace ba tare da sanin ko kai wayeba kace mishi wai baka son yarsa bazaka kuma taɓa sontaba, harda cewa auren yarjejeniya ne zaka saketa, uhumm ɗan yau”. Ita kuwa Mamy cikin mamakin take kallonsa ganin yayi nisan zangon a tunani.

A can cikin ɗakin kuwa, kasan cewar, Ramadan ya bawa, Jannart mgnin amai tasha, shiyasa tana kwanciya sai bacci.

Shi kuwa Rayyern cikin takaici yake zirya a falonsa,
A karo na uku ya kuma leƙowa, jin falon shirune kuma an kashe wuta yasashi, sauƙowa da sauri.
Yana isa tsakiyar falon ya tsaya.
Ganin an haskashi da hasken waya, da sauri ya juya baya, ganin Abba ne zaune bisa 3 str.
“Yah Salam”. Yace tare da dafe kansa yayi maza ya koma baya.
Yana mgnar zuci haka ya haura sama.

Shi kuwa Abba maida kai yayi ya kwanta.

Shi kam Rayyern ranar jk yayi kamar yayi ta kurma ihu.
Haka yake jinsa duniyar babu daɗi.
Sai kusan ƙarfe uku kafin bacci yayi nasarar ɗaukesa.

Washe gari bayan suna dawo daga masallacin sallan asuba, a jere suka shigo falon, Abba ne a baya ya sasu a gaba.
Juyowa yayi ya ɗan kalli Abba.
Shi kuwa Abba tsaresa da ido yayi, a falon suka zauna.
Suka sha tea kamar yadda suka saba.

Miƙewa Ramadan yayi ya wuce side ɗinsu.
Shi kuwa Naan kan kujera ya hau tare da niyar kwanciya.
“Kai tashi ka tafi ɗakinka, ka fara shiri, bakwai dai-dai zamu


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login