Showing 174001 words to 177000 words out of 350584 words

Chapter 59 - Tubali Book 1 Hausa Novel Complete

me matsowa, kusa da bowl din, tare da yagan tissue ya d’auko sandwich din guda d’aya.

Janart kuwa Murmushi tayi, tare da neman waje ta zauna akan sofa.

Ramadan kuwa Koda yakai sandwich din bakinsa idanu, ya lumshe, tare da jinjina kai, bakinsa cike da sandwich din wanda yaji rid’i yace.

“Gaskiya Aunty Jannart you’re the best, komai kin iya domin ban tab’a cin sandwich mai dadin wannan ba da Allah waya koya miki girki haka?.”

Murmushi Jannart tayi tare da cewa.
“Malamai na nada yawa, Mom Aunty Dijat da kuma AYSHA ALIYU GARKUWA marubuciyar littafin GARKUWA dan na koyi abubuwa da yawa a ciki littafin sai kuma shirin Akoshi da rufi na tasharmu”.
Yana mai haɗiye na bakinsa yace.
“Kai Allah yayi musu al'barka ya jikansu suda iyayensu al'farma Annabi da al'ƙur'ani, ai mu sun mana gata Allah kawo Raihana ki koya mata komai”.
Dariya sosai Riyyam-nsra, Jannart, Mamy sukayi suna masu cewa Amin.

Riyyam nsra dake zaune ne ya taso cikin dariya da sauri, tare da cewa.

“Nima ai baza’ayi banda niba wanga santi.”

Ya kare maganan yana me daukan sandwich din yakai bakinsa.

Idanu ya lumshe tare da jinjina kansa, saboda yanda yaji dadin sandwich dinma harya zarce yanda Ramadan ke fadi.

Rayyern kuwa tab’e bakinsa yayi, tare da kawar da kansa gefe.

Riyyam-nsra kuwa sake gyara zama yayi, tare da ninke k’afafunsa, d’ago da kansa yayi ya kalli Mamy da kuma Rayyern, lokaci d’aya kuma sai yaji duk jikinsa yayi sanyi, wanda hakan yasa asanyaye yace.

“Mamy, Hamma Rayyern this week dinnan fa zan koma Ethiopia”.
Cikin abinda ba gaza one second ba duk suka katse dariyarsu tare da zuba mishi ido cikin tsareshi da ido Rayyern yace.
“Meyasa? Yaushe ka tsara tafiyar?”.
Kanshi ya jingina jikin kujera cikin sanyi yace.
“Saboda Mammy ta matsa akan na dawo, tun last week take min maganan dawowa na to daga nan na fara shirin tafiyar, kuma nima nayi kewarsu sosai, sannan kuma na gama aikin da nazoyi ak’asar nan, yanzu babu wani abu daya ragemin sai komawa”.

Cike da tsananin mamaki Ramadan, ya d’ago da kansa ya kalli Riyyam-nsra din.


Murya araunace yace.

“Koma wa Ethiopia kuma Riyyam? sannan kuma this week why ka bari sai end of the month mana.”

Murmushi Riyyam-nsra din yayi, tare da kwantar da kanshi, cikin sanyi yace.

“Dole zan koma Hamma Ramadan ko shekarane ai zaizo dole in koma, saboda yanzu bani da wani reason na zaman k’asar nan, dama daliline ya kawoni.”

Idanu Rayyern dake zaune ya zubawa Riyyam din, Cikin yanayin nazarta yace.

“Wani aiki ne ya kawo ka, then wani reason?”

Murmushi mai kama dana waskewa Riyyam-nsra din yayi, kana cikin samun madafa yace.

“No Hamma Rayyern ba wani babban aiki bane fa, d’an k’aramin aiki ne kuma ma harna gamashi, dama kawai inada passion nazu wa Nigeria ne kan TIKTOK nema fa.”

Idanu Rayyern ya zuba masa batare daya sake cewa komai ba.

Mamy kuwa cikin dan yanayin damuwa tace.

“Haba Riyyam tafiya hakanan lokaci d’aya, ba zato ba tsammani ka bari mana kad’an k’ara kwanaki.”

Murmushi Riyyam din yayi, tare kuma dasa hannu ya shafa sumar kansa, cikin dan sakewa yace.

“Mamy Mammy ta matsa akan saina dawo, baya ga haka ma najima a k’asarnan almost 4to5 month fa.”

Shiru duk sukayi cike da jimamin tafiyar Riyyam din.

Musamman Ramadan da yakejin zaiyi kewar Riyyam din sosai, haka ma Jannart Domin ba kad’anba Riyyam-nsra din ke d’ebe mata kewa, domin akullum tana ganinsa kaman Abdull d’insu ne, baya ga haka kuma Riyyam din yana da shiga zuciya.

Rayyern kuwa mik’ewa yayi tsam ya nufi sama, saboda yagaji sosai a hospital baya ga haka, kuma yau dinma yaje company saidai ba new company dinsu yaje ba, yaje company dinsu wanda ake sarrafa auduga ne.

Koda ya haura saman kwanciyarsa yayi.

Acan falo kuwa basu yi wani hira sosai ba, duk suka watse kowa ya koma d’akinsa.


Almost 3days.
Kenan yau wanda acikin kwanaki ukun kuma, komai yana tafiya dai-dai musamman ab’angaren new Company, din da su Rayyern din suke son budewa.

Dan zuwa yanzu ankammala komai da komai, har an fara sarrafa kayan provision.

Kowanne store dake cikin company din kuwa, an cika sa da sarafeffen kayan provisions kala daban daban.
Komai na dafawa sun sarrafa shi.

Alhamdulillahi kuma ranar Friday aka tsaida amatsayin, ranar da za’a bud’e companyn.


Kasancewar kuma yau alhamis, shiyasa ake ta shirin bude companyn gobe, wannan yasa gaba d’aya Rayyern bai samu ya zauna ba.
Hasalima Koda ya fita bashi ya dawo gida ba, sai k’arfe 10 dai-dai.
Wannan yasa agajiye yayi bacci.

Washegari ranar jumma’a.

Kusan gaba d’ayansu Atare suka tafi masallacin jumma’a, bayan sun Idar da sallah ne kuma, Abba ke sake shaidawa Baba Maud’o cewar yaune, zasu bud’e sabon kamfanin nasu.

Sosai Baba Maud’o yayi farinciki, tare kuma da fatan Allah ya sanya al'khairi, ya kad’e duk wata fitina, ya kuma sanya musu riba mai albarka.

Da. “Ameen Ameen.”
Abba ya amsa.

Bayan sun dawo daga masallacin ne kuma, suka soma shiri dan zuwa bud’e companyn.

Ganin yanda suke ta hada
hada ne kuma yasa, Jannart dake gefen Mamy matsowa kusa da Mamy cikin sigar rok’o tace.

“Ayyah Mamy dan Allah nima zanje in ba matsala.”

Murmushi Mamy tayi tare da juyowa ta kalleta cikin sakin fuska tace.

“To Jannart ai zaki iya zuwa, amma bari na tambayi Abbanku naji me zaice tunda kin san a tsare kike.”

Kai Jannart din ta jinjina, cike kuma dajin dadi ta cigaba, da juya pepper chicken din da takeyi tare da cewa.
“Toh Mamy a gaya mishi Allah yasa a barni”.
Amin
Mamy tace tana fita Kitchen din.
direct sashin Abba ta wuce, Koda taje ta sameshi yana shiryawa.

Zama tayi abakin gadonsa, cikin tausasa murya da kuma bashi girma amatsayinsa na Mijinta tace.

“Dama magana nazo muyi.”

Aje hular hannunsa yayi tare da cewa.
“Ina jinki”.
Cikin zuba mishi ido tace.
“Jannart ce ta sameni wai tanason zuwa bikin bud’e companyn, shine nace bari nazo naji ta bakin ka.”

Kai Abban ya dan jinjina cikin gamsuwa yace.

“To ai ba abundamuwa bane, zata iya binmu saimu tafi tare ko, kice mata ta shirya.”

Dan Murmushi Mamyn tayi, saidai kuma cikin jimami tace.

“Amma Alhaji kamanta cewar zamanta awajenmu sirrine.”

D’an Jim Abban yayi na wasu mintuna kana yace.

“Babu damuwa, zata iyayin shigar da babu wanda zai ganeta, misali ko irin shigar larabawa haka da suke rufe fuska, kinga Idan tayi haka babu wanda zai shaida ta ko!?.”

“Hakane To bari naje na sanar mata.”
Mamyn ta fad’a tana me mik’ewa tsaye.

A kitchen din ta samu Jannart, Cikin kulawa kuma tace mata taje ta shirya, saidai amma tayi shigar da bakowane zai ganeta ba.

Cikin jindadi Jannart din tace.
“To.”
Kasancewar ta kammala aikin da takeyi dinne kuma, yasa kaitsaye ta wuce d’akinta Dan shiryawa.

Acan b’angaren su Ramadan kuwa tsab suka shirya, cikin shigar manyan kaya, shida Riyyam-nsra kayansu iri d’aya Getzner ce orange color mai masifar maiƙo da kyau kalar kayan ya ƙara haska fatarsu saida sukayi wani yellow-yellow.

Bayan sun gama shiryawanne kuma duk suka fito falo.

Dai-dai lokacin kuma Rayyern ya fito daga cikin dakinsa, yayi kyau sosai cikin shigar suit din dake jikinsa Pink guava mai dan ɗigon maroon.
Wanirin sheƙi yakeyi suit din rigar cikin itama maroon hakama net din sa.
Kana ga takalmam toms maroon suma masu masifar kyau da sheki.
Ga kuma wani had’add’en agogon daya saka.
Sosai yayi kyau masifar kyau sajen shin nan ya kwanta lib-lib sai sheƙi sukeyi yan siraran lips ɗinsa jajaye suma suna sheki,
Tattausan sumar kanshi tana kwance lib sai ƙamshi da sheƙi sukeyi.
Wayarsa ce riƙe a hannunsa.
Yana takowa da dan sassarfa,
cikar haiba da kuma kwarjininsa duk sun bayyana.
“Wow Masha Hamma Rayyern kayi masifar kyau”.
Cewar Ramadan yayinda tuni Riyyam-nsra kuma yaketa daukansu hoto.

Haka suka rankayo zuwa falo, yana gaba Suna biye dashi abaya.

Koda suka sauk’o k’asa afalo suka samu Mamy.
Sai kuma Abba, Dr. Sulaiman, da kuma Usman P.A, duk sun shirya sauk’owan su Rayyern din kawai suke jira.

“Abba mutafi time yana kurewa.”
Rayyern din ya fad’a yana me duba agogon hannunsa.

Kai Abba Ya jinjina, tare da Kallon Mamy Cikin kulawa yace.

“Kira Jannart.”

“To” Mamyn tace, saidai batakai ga mikewa ba, Jannart din ta bud’e kofar falon ta ta fito.

Sanye take da doguwar riga maroon colour, Wacce aka k’awata jikinta da adon fararen duwatsu shuwariski.

Rigar irin abaya masu fad’innan ne, da tayiwa jikinta matukar kyau, sai kuma babban mayafin da ta saka akanta, wanda kuma ta nad’ashi har akan fuskarta, kamar dai yanda larabawa keyi, hakan kuwa shiyasa idanunta kawai ake iya gani.

Bak’aramin kyau tayi ba, domin tafito ne a balarabiya sak, tayi kyau ainun.

Wanda har hakan yasa akaron farko, Rayyern ya kasa d’auke idanunsa daga kanta.
Duk da yaji bakincikin cewar da ita zasu tafi, amma ya yaba da shigar jikin nata ainun.

“Masha Allah Jannart kinyi kyau.”

Mamy ta fad’a cikin yabawa shigar dake jikin Jannart din, saboda shigane na musulunci, da kuma shigane daya boye asalin kamanninta.

Atare duk suka rankaya suka fita, zuwa compound din gidan, inda tsala tsalan motoci suke jiransu.

Wata black Range Rover Rayyern ya shiga, haka ma Abba da Baba Maud’o.

Su Ramadan da Riyyam-nsra kuwa motocinsu daban, Yayinda Mamy da Jannart ma suka shiga nasu motar.
Haka Usman P.A da Dr Sulaiman.
Convoy motocin nasu sukayi, ahaka har suka isa cikin babban kamfanin. Daya amsa sunansa kamfani.

Jama’a da kuma yan jaridune cike awajen, bayan su Rayyern din sun isone kuma, wajen ya dinke da sowa.

Haka dai suka karasa wajen zama na musamman suka zauna, sosai Jannart ta yaba da tsarin kamfanin. Domin tayi imani ko kamfanin Dadynta bai kai wannan ba.

Taro akayi mai tsabta bayan kowa yaci yasha ne kuma, aka bude companyn.

Yan Jarida kam sun samu abunda sukeso, musamman da suka ga yanda Rayyern yasa, wasu daga cikin ma’aikatan kamfanin, suka cika motoci da kayan provision, inda ya bada umarnin, akai kowacce mota ta abinci, gidan yari, da gidan Marayu, sauran motocin kuma yace rabawa gajiyayyu.
Ai kuwa hakan da yayi ya daki zuciyar mutane da yawa, hakan yasa yan jarida suka kara kaimi wajen shooting.

Alhamdulillah anyi taro lafiya, inda taron ya samu halartar manyan baki, yan kasuwa shareholders mata da maza suke ta zuwa, kowa yanaso ya zuba hannun jarinsa a kamfanin.
Bayan duk Jama’an dake wajen sun watse ne kuma, suka tattara duk suka koma gida.
Zuwa lokacin kuwa har dare ya soma yi, wannan yasa agajiye dukansu suka koma gida.

Washegari Saturday still a busy suka tashi, musamman Rayyern.

Yayinda Riyyam-nsra kuwa keta shirye shiryen, komawarsa Ethiopia.
Saboda ranan Monday Insha Allah zai tafi.

Acikin yan kwanakin kuma duk cikin hidima suke, saboda mutane daban daban da suke zuwa gidan su Rayyern din Taya murna yayinda shi kuwa Rayyern yanzu bai samun zuwa asibiti ma, a Company yake wuni kullum sabida yana son dai-dai ta komai ta yadda in ya tafi ta online zaci gaba da aiyukansa wasu kuwa ya mikasu ga MD.

Kasancewar yau Lahadi ne kuma yasa, Riyyam-nsra shiryawa yaje gidansu Naseer.

Hira sukayi sosai da Naseer din kafun daga bisani yayiwa, Umman Naseer din sallama, daga nan kuma gidan Malam Mai-nasara suka wuce.

Bayan sunyi masa sallama ne kuma, suka dawo nan gidan su Rayyern din.

Hira suka sha sosai, duk da cewar zuciyarsu babu dadi, saboda sunsan zasu yi kewar Riyyam din sosai.

Washegari Monday kuwa, k’arfe 8 dai-dai jirgin su Riyyam din zai tashi.

Duk yau din haka suka tashi babu dadi, saboda shakuwar dake tsakaninsu more Especially Ramadan da yayi zugum,
dan har wani ciwon kai yakeji, saboda tafiyar Riyyam-nsra din.

Haka ma Jannart.

K’arfe 7:50 am dai-dai kuwa Abba, Baba Maud’o, Rayyern da kuma Ramadan suka rakashi airport, cike da kewarsa, kyautttuka kuwa babu irin wanda basu bashi ba, domin Rayyern ma ba k’aramin kud’i yayiwa Riyyam-nsra din transfer ba.

Jannart kuwa har snacks tayi masa, tare da basa kyautan wani Apple Watch dinta mai kyau.

Sosai yayi musu godiya da irin karamcin da suka nuna masa, Koda yazo shiga jirgi,
Ruggume Ramadan yayi sai ga hawaye shar-shar a idanunsa
Cikin rawar murya yace.
“Hamma Ramadan azanzo aurenka”.
Cikin rawan murya Ramadan yace.
“Zanyi kewarka Riyyam-nsra inaji ba dadi tamkar zan rabu da rabin jikina nakeji”.
Da sauri Baba Mauɗo ya juya musu baya yana maijin wasu irin zafafan hawaye na tsastsafo mishi.
A hakan yaji Riyyam-nsra ya ruggumeshi ta baya kawai sai yaji hawayen sun silalo mishi.
“Allah sarki Baba Mauɗona zanyi kewarka”.
Ina ya kasa mgn domin in yayi mgn zasu gane yana kuka.
Cikin rauni Rayyern ya ɗan kamo hannunsa tare da cewa.
“Toh Riyyam-nsra mu zauna kawai mana”.
Da sauri ya sharce hawayen sa tare da juyawa gaban Abba ya ruggumeshi yana cewa.
“Mammay na nake son gani da kai mata sakonta amman in sha Allah nan kusa zan dawo”.
Daga nan ya juya ya nufi wurin shiga jirgin
Yana zubda k’walla tare da daga musu hannu, aransa yakejin zaiyi kewarsu sosai.
Saidai kuma yasani cewa.
Lallai watarana zai dawo, zai dawo ya zauna acikinsu, zama kuma na musamman bawai irin wanda sukayi ayanzun ba.

K’’arfe 8 dai-dai jirgin su Riyyam-nsra din ya d’aga, zuwa k’asar Ethiopia.

Haka su Rayyern din suka dawo gida, jikinsu asanyaye.

Ramadan ne ya zauna akusa da Jannart, cikin sanyi yace.

“Wallahi duk gidannan babu dadi, Riyyam shi ke samu duk wani farinciki, gashi yanzu ya tafi, again kuma Hamma Rayyern ma nanda one week zai tafi, gaskiya nima tafiya zanyi.”

Cikin.sanyi Jannar tace.

“Gsky dole muji gidan ba daɗi,
To ba gani ba ga Mamy, ka daina fushi.”

Longoɓar da kai Ramadan din yayi, tare da mikewa tsaye, Cikin yanayin jin yuwa yace.

“Muje ki bani abinci My Aunty.”

Mamy dake kallonsu ne tayi murmushi, cike da k’aunar y’ay’annata tace.

“To Ramadan kamanta da cewar, Rayyern da Jannart zai tafi? ai zama mu kad’ai kam ya kama mu.”

Jin abunda Mamyn ta fad’ane kuma, yasa Jannart saurin juyowa ta kalli Mamyn, domin kwata kwata ita bata masan da zancen ba.

Ramadan kuwa fuska ya sake kwab’ewa Cikin yanayin damuwa yace.

“Gaskiya Mamy nima zan tafi London shak’atawa, ko ki gayawa Abba Dan Allah yaje, gidansu Rayhanna mana, atambayamin aure, gidan ya rame da yawa, please Mamy.”

Ya k’are maganan yana me had’e hannayensa, alaman rok’o.

Murmushi Mamy tayi, kana cikin kulawa tace.

“To me kakeci na baka na zuba Ramadan, ai komai ya kusa, tunda har ankai kudin, nagani inaso, kuma iyayen Rayhannan sunce zasu tuntub’i Abbanku.”

Idanu Ramadan din ya dan zazzaro cikin, mamaki hadi da tsananin jin dadi yace.

“Wow Mamy yaushe akayi haka bansani ba, Dan Allah su Abba sunje.”

Murmushi Mamyn tayi tare da jinjina masa Kai tace.

“Eh su Abbanku sunje shekaran jiya, shine kuma yace kada na fad’a maka, da alama surprising dinka yakeson yi yanzuma subutar bakine.”

“Masha Allah Alhamdulillah, thank you Mamayna, soon nima zanyi aure wow.”

Ramadan din ya fadi haka cikin tsananin jin dadin daya rage masa kewar Riyyam-nsra.

Mamy da Jannart kuwa murmushi sukayi.

Haka dai suka d’an tab’a hira, kafun daga bisani suka watse.

Jannart kam gaba daya jin cewa da ita, za’a tafi Mascow yasa jikinta yin sanyi.

Wanda hakanne ma yasa ta d’aukar waya, ta kira Abba Kabir.

Bugu biyu kuwa ya d’auka bayan sun gaisa ne, kuma ta gyara zama kaman Abban yana gabanta tace.

“Abba kaji wai dani zai tafi Mascow, d’azu Mamy take fad’a.”

Daga can b’angaren Abba Kabir yayi murmushi, Cikin kuma jin dadi yace.
“Waye ɗin”.
Cike da kunya tace.
“Shi Doctor din”.
Murmushi mai sauti Barrister Kabir yayi tare da cewa.
“Masha Allah Jannart, ai babu damuwa zaku iya zuwa, Allah Ubangiji ya tsare ya kuma kareku aduk inda kuke, yaushe ne zaku tafin?”

Fuskarta ta d’an shagwabe Cikin yanayin sanyi, tace.

“Abba basu fadamin ranar ba, amma nasan zasu fada ma Idan lokaci yayi.”

“To shikenan Jannart.”

Abba Kabir din ya fad’a, daga haka kuma hira kadan sukayi sannan sukayi sallama.

Washegari kuwa Abba da kasan ya kira Barrister Kabir ya sanar masa batun tafiyar.

Wanda kuma yau ya kama saura kwana biyu tafiyar tasu, sosai kuma suke ta shirye shirye tuni Rayyern ya tsara ayukan campany'nsa yadda ya dace.

Ana Gobe zasu tafi dinne kuma, Abba Kabir yazo sukayi sallama da Jannart din.

Washegari.

1:pm dai-dai jirginsu zai t
Yashi zuwa Mascow, hakan yasa tunda safe suka kammala shirinsu.

Cike da yakinin kewarsu, Mamy Abba da kuma Ramadan suka rakasu airport.

Karfe takwas jirginsu ya tashi zuwa, Abuja.

Bayan sun isa Abujan ne kuma, da kammanin awanni biyu jirginsu na zuwa Mascow ya d’aga zuwa sararin samaniya.

Ko acikin jirgin kuwa kujeransu na hade dana juna, tunda suka kama hanya kuwa, Jannart ta kwantar da kanta akan kujera tare da lumshe idonta dan bacci dake fuzgarta,
haka ma Rayyern shidinma lub yayi, Ahankali yake sauke ajiyar zuciya, tare kuma da ajiye idanunsa akan, yatsun hannunta wanda suke shinning.


Tafiya sukayi mai Nisan zango k’arfe.
8: 30 na daren garin, jirginsu ya sauk’e ababban airport din dake cikin garin na Mascow...!




*Albishirinku! Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA*

NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA.
Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.

Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke taimakawa (sex hormones 😍) dinki.
Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!?
Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login