Showing 135001 words to 138000 words out of 350584 words
gashin idanunta.
Shi kuwa Rayyern dake kwance a hankali ya ɗan ja numfashin wahala tare da fesar dashi.
Kana ya rumtse idanunshi da ƙarfi tare da taune lips ɗinshi, duka biyu saboda so yake ya tashi, amman gaba ɗaya jikinshi daga kugunsa zuwa sawun takawarsa sunyi lakwas.
Wannan abun shiyasa baya son allurar.
Dan muddin akayi mishi ita sai yayi kusan mako guda karfinsa bai dawo dai-dai ba.
Da sauri Ramadan ya matso kusa dashi.
Dai-dai lokacin kuma Riyyam-nsra shima ya sauko ƙasa.
A tare suka ɗan sunkuyo kanshi, ahankali ya buɗe idanunshi jin muryar Abba nakiran sunansa.
“Rayyern! Rayyern!!”.
Cikin wata iriyar sassanyar murya can ƙasan maƙoshi yace.
“Na'am Abba”.
Jin Rayyern din ya amsa ne kuma, yasa Abba cikin jin daɗi yace.
“Alhamdulillah! Alhamdulillah!!”
Rayyern kuwa cikin ƙarfin hali da jarunta ya tattaro ragowar kuzarin sa baki ɗaya.
Ya yunƙura alamun zai tashi.
Da sauri Ramadan yasa hannunsa zai tallabeshi.
Cikin sanyin murya yace.
“Barni zan iya”.
Cike da rauni Ramadan yace.
“Hamma Rayyern bazaka iyaba”.
Kar-kar haka jikinsa ke rawa.
Lokacin da ya samu ya juyo ya ɗago kanshi.
Da sauri ya rumtse idanunshi ganin kamar kan Jannart yake.
Haka yasa ya miƙawa Ramadan hannunsa.
Da sauri ya kamoshi kana ya yunƙura ya zauna.
Lokacin Mamy ma ta iso cikin jin daɗi tace.
“Alhamdulillah sannu ko Babana”.
Kanshi ya gyada mata.
Ita kuwa Jannart a hankali ta miƙe tsaye.
Cikin son tsaida hawayenta ta nufi Kitchen.
Tashinta ne yasa Abba matsowa kusa dashi.
Hakama Mamy nanfa sukayi ta mishi sannu.
Ita kuwa Jannart tana shiga Kitchen aikin da Mamy ta fara taci gaba da yinsa.
Su kuwa A falon cikin ƙarfin hali ya maida kansa ya jingina da jikin kujera, kana a hankali ya fara yunƙurin tashi tsaye.
Da sauri Abba ya tallabeshi gefen damanshi.
Kana Riyyam-nsra ya tallabe gefen hagunshi.
Ramadan kuwa da Mamy ido suka zuba musu, sunaga yadda yake taka kafafunsa da suke karkarwa.
A hankali suka fara take steps din da taimakon su Abba ya samu.
Suka haura.
Kai tsaye Bedroom dinsa suka wuce dashi.
Suna shiga suka kwantar dashi.
Sanin kuma allurar zata sashi bacci ne yasa Abba juyawa ya fita.
Shi kuwa Riyyam-nsra gefensa ya zauna.
Yana gyara masa pillow.
Rayyern din kuwa yana kwanciya, lokacin ɗaya bacci ya fara fuzgarshi.
Ramadan ko ganin sun haura sama ne, ya sashi fita kaitsaye kuma Mai-nasara pharmacy ya nufa, inda yaje ya d’auko magungunan da Rayyern din Kesha Idan ciwon ya tashi.
Ita kuwa Mamy Kitchen ta koma nan sukaci gaba da aikinsu ita da Jannart.
Bayan sallan isha'i.
A hankali Jannart ta dan juyo tana kallon kofar babban falon,
daga nan cikin falonta.
Da sauri kuma ta miƙe jin muryar mutumin nan da taji ana kiransa da Baba Mauɗo yana sallama.
Da alamun kuma babu kowa a main falon.
Da sauri ta mike ta nufo falon.
Baba Mauɗo Kuma tsaye yake bakin ƙofar, ya ɗan turota yana sallama da ɗan buga kofar.
A hankali tace.
“Wa alaikassalam Baba ka shigo mana”.
Dai-dai lokacin kuma Mamy ta fito daga side ɗinsu.
Cikin girmamawa tace.
“A'a Baba Mauɗo ka shigo mana”.
Cikin kamala yace.
“Toh”.
Kana ya shigo.
A hankali Jannart ta dan rusuna tare da cewa.
“Barka da dare Baba”.
Juyawa yayi ya kalleta cikin wani irin mamaki da nazarin fuska da kammanin muryar yarinyar yace.
“Barka dai, Ya mai gidan naki da jikin?”.
Cike da girmamawa tace.
“Alhamdulillah jiki da sauƙi”.
“Masha Allah. Allah ya ƙara mana sauki”.
Ya faɗa yana mai juyowa yana kallon Mamy dake cewa.
“Bismillah mu isa yana sama, Abbansu ma yana can”.
Hakan ne yasa ya nufi saman.
Ita kuwa Mamy juyowa tayi ta kalli Jannart, da idanunta suka dan yi ja cikin kulawa tace.
“Kinyi salla ko?”.
Kai ta gyaɗa mata alaman eh.
Ita kuwa Mamy.
Ba tare da tace mata komaiba ta nufi Dinning area.
Foodflask ta ɗauko wanda tasa mata,
Abincin da sukayi sakwara ce, da miyar agushi.
Miƙa mata tayi tare da plate da spoon tace.
“Gashi ki zauna kici abinci, ki kuma bar zubda hawayen nan haka kinji ko Mamana”.
Cikin sanyi tace to.
Kana ta amshi kular ta wuce ɗakinta.
Ita kuwa Mamy Kitchen ta koma tazo ta shiryawa su Ramadan nasu ta kai musu falon sama.
Anan ta samesu.
Baba Mauɗo da Abba Kuma suna cikin dakin Rayyern ɗin.
Ganin har yanzu bacci yakeyi ne, yasa suka fito.
Ita kuwa Jannart ajiye kular tayi a falon.
Ba tare da tayi niyar ciba, ta kwanta a ƙasa bisa carpet din, tana rike da wayarta.
Sam ta rasa me take tunawa,
saidai kawai ta fahimci cewa yau gidan babu daɗi dan ciwon Rayyern ɗin.
Sabida su Ramadan masu ɗebe mata kewa da Riyyam-nsra mai sata farin ciki duk yau basa da Gud Mood.
Tana nan kwance ahaka har tayi bacci.
A folon kuwa suna fitowa suka samu Dr Sulaiman ya iso.
Nan Abba ya koma dashi ya ɗan ƙara dudduba shi.
Kana ya sallamesu ya tafi.
Haka dai su Ramadan suka tafi dakinsu.
Mamy kuwa falon Jannart ta leƙa ganin tana bacci ne yasa ta wuce side ɗinsu.
Dan tasan yau Abba a dakin Rayyern zai kwana.
Haka
Hakan kuwa akayi.
Rayyern kuwa baccin yayi mai zurfi sai karfe uku da rabi ya farka.
Abba da kanshi ya hada masa ruwa yayi wonka,
Kana yayi al'wala.
Yana fitowa yayi ramuwar sallan magriba da isha'i, sannan ya dan sha tea ɗin da Abba ya hada masa da kansa.
Toh kuma daga nan sai idonsa ya ɗan bushe.
Sai da akayi sallan asuba.
Kafin ya koma wani baccin.
Koda Abba suka dawo masallacin sun sameshi yana bacci.
Nan suka fito.
Mamy da Jannart kuwa Kitchen suka shiga dan haɗa breakfast.
Kasan cewar yau ɗin asabar ce ba aiki.
Yasa Riyyam-nsra da Ramadan ma basu tashi da wuriba.
Sai karfe tara suka fito,
d’akin Rayyern suka shiga.
Zaune suka sameshi bisa carpet ya jingina jikinsa da gado.
Mamy da Abba ne zaune agabanshi.
Mamy na haɗa mishi tea.
Abba Kuma da kanshi yake zuba mishi ferfesun jan nama da Jannart tayi mishi yayi laushi tibis.
A hankali ya ɗan juyo ya kalli Radaman dake cewa.
“Hamma ya jikin naka?”.
Cikin sauƙe numfashi yace.
“Alhamdulillah”.
Riyyam-nsra kuwa matsoshi yayi da kyau tare da cewa.
“Hamma Rayyern Mammy ta gaishe ka da jiki.
Zaiton ma tace in gaisheka da jiki”.
Cikin sanyi yace.
“Ngd".
Ganin kuma alamun bai son surutune.
Yasa suka sauƙo ƙasa.
Abba kuwa cikin kulawa yace.
“Rayyern kaci abincin tunda ɗuminsa kaji”.
Cikin sanyi yace.
“Abba na gaji bazan iya cin nama da sassafen nan ba”.
Da sauri Mamy tace.
“Rayyern yayi laushi sosai fa”.
Cikin narke fuska yace.
“Bani tea ɗin kawai is okay".
Haka suka hakura suka barshi.
Tea ɗin yasha.
Kana Abba ya kuma hada masa ruwan wonka yayi.
Koda ya fito daga wankan, wasu tausassun riga da wondo yasa wanda Abban ya fito masa dasu.
Mamy kuwa tuni ta sauko k’asa,
aƙasan ta samu su Ramadan da Riyyam nsra a dining area suna zaune, Yayinda Jannart ke zuba musu abinci.
Da sauri Mamy tace.
“Kai kun kai abincin su Baba Mauɗo kuwa?”
Kai Riyyam-nsra ya gyaɗa tare da cewa.
“Eh Mamy nakai musu, yanzu ma na dawo”.
“To yayi.”
Mamyn tace tare da zama gefensu, nan sukayi Karin kumallon.
Wunin ranar dai haka sukayi shi a gida gaba dayansu.
Alhamdulillah kuma jikin Rayyern da sauki, sai dai rashin karfi da rashin cin abinci, dama kuma da rashin son mgn da bayayi, dama kuma shi ba gwanin surutu bane, balle kuma yanzu ga halin ciwo.
Washe gari ranar lahadi ma
Haka suka wuni.
Duk da surutun Riyyam-nsra ya rage,
saboda jikin Hamman nasa.
Da yamma kuma Nasir Ahmad yazo ya duba Rayyern din da jiki.
Bayan sun d’an taba hira shida Riyyam nsra ne kuma, yayi musu sallama daga nan kuma gidan Malam Mai-nasara ya wuce.
Nan yake sanar masa abinda ke faruwa...
Jannart kuwa tun ranar tun lokacin kuma bata sake ganinsa ba ko jin muryarsa.
Yayinda Mamy kuwa duk a zatonta Jannart din, duk safiya tana zuwa duba jikin Rayyern din.
Washe gari Ranar Monday Alhamdulillah jikin da sauki sosai, domin karfinsa ma ya ɗan fara dawowa.
Bayan sunyi breakfast ne kuma Ramadan ya tafi asibiti.
Hakan yasa Jannart da kuma Riyyam-nsra, sai kuma Mamy ne ke zaune afalon.
D’ago kai Riyyam nsra din yayi, tare da kallon Jannart dake riƙe da wayarsa, tana kallon comments ɗin followers ɗinsa akan wata wakar fullancin daya bibiya.
jin wayar tasa tana ringing ne kuma yasashi kallonta, tare da d’an gyara zamansa yace.
“Aunty Jannart Waye”.
“Mammy ce”.
Ta bashi amsa tana miƙo masa wayar.
Da sauri ya amshi wayar tare da amsa kiran
“Assalamu alaikum yah Mammy”.
Jim ya ɗanyi na tsawon kusan daƙiƙu 2, kana a hankali ya miƙe tsaye tare da fara haurawa sama yana cewa.
“Afwan Mamma wlh shine baya son surutu, ko wayarsa bai amsa kira, tun ranar nake son hadaku toh ganin baida lfyarne yasa nai shiru”.
Ya ƙare mgnar yana ida hawa saman.
Kai tsaye dakin Rayyern ɗin ya nufa da sallama a bakinsa.
A falon kuwa cike da mamaki Mamy ta bishi da ido.
Zuwa yanzu ta fara tsoron wani al'amarin, to wai ma ya akayi bata taɓa tunanin Riyyam-nsra ya nuna mata hoton Mammansa ba?.
Tayi wannan tunanin.
Jannart kuwa da sauri ta juyo ta kalli wayarta dake gefenta, cikin mamaki ta zubawa wayar ido ganin number dake kiranta...
Shi kuwa Riyyam-nsra a hankali ya isa gaban Rayyern dake zaune bisa kujera.
Yasa system ɗin shi a gaba da alamun aiki zaiyi dan yanzu ya buɗe ta.
Idonshi ya ɗago ya zubawa Riyyam-nsra su.
Shi kuwa Riyyam-nsra cikin karya wuya.
Da rauni ya iso garesa, murya a raunace yace.
“Ayyah Hamma Rayyern, dan Allah ga waya kayi mgna da Mammy na, tun shekaran jiya take cemin in hadaku ta gaidaka da jiki taji muryarka”.
Ya ƙarashe mgnar yana karya wuya.
Ga mamakin Rayyern kuwa sai ga hawaye na zubowa a fuskar yaron.
Shi kuwa Riyyam-nsra cikin yin rau-rau da ido.
Ya miƙa masa wayar tare da cewa.
“Dan Allah Hamma Rayyern kada kace a'a”.
Ya rigada ya gama karya mishi zuciya da hawayensa.
Duk da ko mgnar yayi sai yaji ya gaji shiyasa baya son yawan mgn.
A hankali yasa hannunshin ya amshi wayar.
Cikin nitsuwa ya manna wayar a kunneshi tare dasa kafaɗarsa ya makale wayar.
Murya a sanyaye yace.
“Assalamu alaikum”.
A can ƙasar Ethiopia kuwa.
Wani irin lumshe ido Mamma tayi, tare da jan wani irin dogon numfashi, kana cikin tsananin harbawar da zuciyarta keyi tace.
“Wa alaikassalam Mauɗo am!!!”.
Wani irin rumtse idanu Rayyern yayi da azaban ƙarfi tare dasa hannunshi y...!
*Albishirinku! Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA*
NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA.
Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.
Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke taimakawa (sex hormones 😍) dinki.
Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!?
Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu.
Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki?
Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu,
Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ki zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan.
Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya.
Akwai daya bangaren wato *KAMSHI*
Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, sayan na gari maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia.
Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.
🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA
*(GARKUWAR MA'AURATA)*
By
*GARKUWAR FULANI*
Ya dafe ƙahon zuciyarshi sabida wani irin masifeffen harbawa da yaji tayi da azaban ƙarfi.
“Yah salam”.
Shine abinda ya iya fada cikin zuciyarsa.
Yayinda Riyyam-nsra kuwa ya zauna a kasa, a gabanshi tare dasa hannunshi duka biyu ya tallabe Fuskarsa, kana ya zubawa Rayyern ɗin idanu kamar mai kallon madubi ko TV.
Shi kuwa Rayyern wani irin sakewa yaji jijiyoyin kanshi zuwa zuciyarsa sunayi.
Suna bada sautin
Ras-ras, yayinda duk kofofin gargasar jikinsa suka fara amsa amon muryar baiwar Allah nan.
Yayinda can wurin Mammy ma haka abin yake.
Dan Tuni ita wasu hawaye na ke tsiyayo mata, Yayinda takejin zuciyarta nayi mata ani irin duka.
Cikin rumtse idanunta tace.
“Maudo ya jikin naka?”.
Idanunsa ya dan lumshe, cikin kuma jin wani sabon bugun zuciya yace.
“Mammmmmy jiki da sauƙi Alhamdulillah.”
Riyyam nsra kuwa dake gefe, wasu irin zafafan hawaye ne suka zubo, daga cikin idanunsa, wanda sukafi kama da hawayen farin ciki.
Yayinda shikuwa Rayyern meda kanshi yayi ya jingine, jikin kujerar yana mai amsar saƙon da jijiyoyin jikinsa suke bashi.
Cikin kasala kuma ya motsa lips ɗinsa tare da cewa.
“Amin Mammy.”
Ya fad’i hakanne kuma saboda, addu’ar da Mammyn tayi masa.
Mammy kuwa Idanunta ta lumshe, cikin kuma danne abunda takeji, yayi tsaye acikin zuciyarta, ta soma yi mishi addu’an samun lafiya, tare da sa mishi al'barka.
Sai kuma ta daura da cewa.
“Ina Ramadan?”
Cikin sauƙe numfashi Rayyern din yace.
“Ya tafi wurin aiki”.
Daga can b’angaren Mammy kuwa Kai ta jinjina, tare da soma tambayan shi, akan sauran ahlin gidan nasu.
Shikuwa Rayyern duk yanda yakejin, mood d’insa na sanjawa, amma anutse yake amsa mata, kana kuma
Cikin girmamawa.
Kamar da wasa kuwa, shida Mammyn saida sukayi mgnar mituna shida kana sukayi sallama.
Bayan ya zare wayar akan kunnensa ne kuma, ya mikawa Riyyam nsra.
Cikin sauri kuwa Riyyam ya karb’i wayan, tare da mikewa tsaye, direct ya koma dakin Ramadan.
Ganin fitan Riyyam dinne kuma yasa, Rayyern jingine kansa da jikin kujera, tare da rumtse idanunshi.
Asanyaye kuma cikin tausasshiyar muryarsa, yake fad’in.
“Yah ilahi ya mujibadda'awati.
Ya salam”.
Sune abunda yake fad’a yana mejin
tamkar kanshi zai juye, abubuwa da yawa keyi masa yawo acikin tunanin sa.
“Maudona!!”
Ya maimaita kalmar da yaji ya tsaya mai arai, dan sai yakejin tamkar ya tab’a jinta.
Idanunshi ya buɗe kana a hankali yace.
“Toh ko dai Baba Mauɗon da nake jine yasa naji kamar nasan kalmar ada can baya?”
Saurin girgiza kanshi yayi, tare dasa hakwaransa ya cije lips d’insa.
Take kuma ya fad’a dogon nazari, wanda hakan yasa ya gaza ci gaba da aikin da yake son yin.
A can falon kuwa, cike da mamaki Jannart ta zubawa wayarta ta ido
Taki amsawa.
“Jannart ba kiranki akeyi ba ki amsa mana”.
Mamy ta fada tana kallonta cikin kulawa.
Jannart din kuwa cikin yanayin nazari tace.
“Mamy number’n ba suna, ban san waye bane”.
Ta ida mgnar tana jawo wayar jin da tayi sako ya shigo mata.
“Toh ki amsa mana ai zakiji waye ne”.
Cewar Mamy.
Jannart din kuwa kai ta ɗago daga duba sakon tare da cewa.
“Lah ashe ma Aunty Dijat ce”.
Ganin kiran ya kuma shigowa ne yasa ta amsa kiran.
Tare da kara wayar a kunne.
Da sauri tace.
“Abba kaine”.
Gyara zama Barrister Kabir yayi tare da cewa.
“Eh nine dai Jannart, na fahimci.
Daddynki yana iya zargar wayata da bin diddiginta ne, yasa na kiraki da wayan Khadija."
Cikin gamsuwa tace.
“Ayyah Daddy na”.
Miƙewa Mamy tayi ta bar wurin.
Sabida ta barta ta ɗan sake.
Ta sake din kuwa ganin Mamyn ta tafi cikin nitsuwa tace.
“Abba ya lbrin su Daddyn ya Mom tayi, ina Yah Azeez na?”.
Da sauri yace.
“Me ruwanki dasu”.
Shiru tayi cikin sanyi jiki ta miƙe ta nufi falon ta.
shi kuwa Barrister Kabir cikin kulawa yace.
“Kina lfy ko".
“Lfy lau Alhamdulillah Abba”.
Ta bashi amsa tana zama.
“Gaba ɗaya jiya ke nai ta tunawa da sanyin nan, ki kula da kanki sosai kin san irin wannan sanyin ƙarshen hunturun yafi miki illa da tada ciwonki, kiyaye shan ruwan sanyi da AC, sannan kike rufe Windows ɗinki duka sabida hazo kinji ko?".
Cikin nitsuwa tace.
“Toh Abba”.
Juyowa yayi ya kalli Dijat dake ta son ya Bata wayar suyi magana da Jannart din, kauda kanshi yayi daga kallonta tare da cewa.
“Gidan naku duk lfy ko?”.
Gyara labulen window dake kusa da ita tayi kana a hankali tace.
“Uhumm shine dai baida lfy, tun ran jumma'a, wai ciwon cikinsa ya tashi, sai ka gani Abba kamar zai mutu fa”.
Ta k’are